< Mika 1 >
1 Dette er Herrens ord som kom til Mika fra Moreset i de dager da Jotam, Akas og Esekias var konger i Juda, det som han skuet om Samaria og Jerusalem.
Maganar Ubangiji ta zo wa Mika mutumin Moreshet a zamanin Yotam, da na Ahaz, da kuma na Hezekiya, sarakunan Yahuda, Mika ya ga wahayi a kan Samariya da kuma a kan Urushalima. Ga abin da ya ce.
2 Hør, I folk, alle sammen! Gi akt, du jord med alt som på dig er! Og Herren, Israels Gud, være vidne mot eder, Herren fra sitt hellige tempel!
Ku ji, ya ku mutane duka, ki saurara, ya ke duniya da dukan mazauna cikinki, bari Ubangiji Mai Iko Duka yă zama shaida a kanku, daga haikalinsa mai tsarki.
3 For se, Herren går ut fra sin bolig; han stiger ned og farer frem over jordens høider.
Duba! Ubangiji yana zuwa daga wurin zamansa; zai sauko yă taka maɗaukakan wuraren duniya.
4 Fjellene smelter under ham, og dalene revner - som voks for ilden, som vann når det øses ut over et stup.
Duwatsu za su narke a ƙarƙashin ƙafafunsa, kamar kaki a gaban wuta, kwaruruka kuma za su ɓace, kamar ruwan da yake gangarowa daga tsauni.
5 For Jakobs frafall skjer alt dette, for de synder Israels hus har gjort. Hvem er ophavet til Jakobs frafall? Mon ikke Samaria? Og hvem til Judas offerhauger? Mon ikke Jerusalem?
Duk wannan zai faru saboda laifin Yaƙub, da kuma zunuban gidan Isra’ila ne. Mene ne laifin Yaƙub? Shin, ba Samariya ba ce? Ina ne maɗaukakan wuraren Yahuda? Shin, ba Urushalima ba ce?
6 Så vil jeg da gjøre Samaria til en grusdynge på marken, til et sted for vindyrkning, og jeg vil velte dets stener ned i dalen og avdekke dets grunnvoller.
“Saboda haka zan mai da Samariya tarin juji, wurin noman inabi. Zan zubar da duwatsunta a cikin kwari in kuma bar harsashin gininta a bayyane.
7 Og alle dets utskårne billeder skal sønderslås, og alle dets horegaver brennes op med ild, og alle dets avgudsbilleder vil jeg ødelegge; for av horelønn har det samlet dem, og til horelønn skal de atter bli.
Za a ragargaje dukan allolinta; za a ƙone dukan baye-bayenta na haikali da wuta; zan lalatar da dukan gumakanta. Tun da ta wurin karuwanci ne ta tattara su, ga karuwanci kuma za su koma.”
8 Over dette vil jeg klage og hyle, jeg vil gå barbent og naken; jeg vil opløfte klageskrik som sjakalene og jamre mig som strutsene.
Saboda wannan zan yi baƙin ciki, in yi kuka; zan yi tafiya ba takalmi, zan tuɓe, in kuma yi tafiya tsirara. Zan yi kuka kamar dila, in yi baƙin ciki kamar mujiya.
9 For dets sår er ulægelige; for ulykken er kommet like til Juda, den har nådd like til mitt folks port, til Jerusalem.
Gama raunin Samariya ba mai warkewa ba ne; ya bazu har Yahuda. Ya ma kai bakin ƙofar mutanena, har ma Urushalima da kanta.
10 Forkynn det ikke i Gat, gråt ikke der! I Bet-Leafra velter jeg mig i støvet.
Kada a faɗe shi a Gat; kada ma a yi kuka. A maimako haka, a yi birgima a cikin ƙura a Bet-Leyafra.
11 Dra bort, I Sjafirs innbyggere, i nakenhet og vanære! Sa'anans innbyggere våger sig ikke ut. Bet-Haesels klageskrik gjør det umulig for eder å bli der.
Ku wuce tsirara da kuma kunya, ku mazaunan Shafir. Bet-Ezel tana makoki domin babu wani daga Za’anan da ya fito don yă taimaka.
12 For Marots innbyggere vrir sig i smerte over sin tapte lykke; for ulykke er faret ned fra Herren, like til Jerusalems port.
Mazaunan Marot sun ƙosa su ga alheri, amma Ubangiji ya sauko da azaba, har zuwa ƙofar Urushalima.
13 Spenn traveren for vognen, I innbyggere av Lakis! Syndens ophav var du for Sions datter, for hos dig blev Israels overtredelser funnet.
Ku da kuke zama a Lakish, ku ɗaura wa dawakai kekunan yaƙi. Gama ku kuka fara yin zunubi a Sihiyona, gama an sami laifofin Isra’ila a cikinku.
14 Derfor skal du gi avkall på Moreset-Gat; husene i Aksib blir som en sviktende bekk for Israels konger.
Saboda haka za ku ba da kyautan bankwana ga Moreshet Gat. Garin Akzib zai zama abin yaudara ga sarakunan Isra’ila.
15 Ennu en gang skal jeg la eder få en eiermann, I Maresas innbyggere! Til Adullam skal Israels stormenn komme.
Ku mazaunan Maresha Ubangiji zai kawo wanda zai ci ku da yaƙi. Sarakunan Isra’ila za su gudu zuwa Adullam.
16 Gjør dig skallet, klipp håret vekk for dine barns skyld, de som var din lyst! Gjør ditt hode så skallet som gribbens, for de er ført bort fra dig.
Ku aske kanku ƙwal don makoki, ku yi wa kanku ƙwalƙwal kamar ungulu. Gama za a ja’ya’yan da kuke farin ciki a kai su bauta.