< Matteus 4 >

1 Da blev Jesus av Ånden ført ut i ørkenen for å fristes av djevelen.
Sa'an nan Ruhu ya bi da Yesu zuwa cikin jeji, domin Ibilis ya gwada shi.
2 Og da han hadde fastet firti dager og firti netter, blev han til sist hungrig.
Da ya yi azumi kwana arba'in dare da rana, daga baya yunwa ta kama shi.
3 Og fristeren kom til ham og sa: Er du Guds Sønn, da si at disse stener skal bli til brød!
Sai mai jarabtar nan ya zo, ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci duwatsun nan su zama gurasa.”
4 Men han svarte og sa: Det er skrevet: Mennesket lever ikke av brød alene, men av hvert ord som går ut av Guds munn.
Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake cewa, 'Ba da gurasa kadai mutum zai rayu ba, sai dai da kowace magana da ta ke fitowa daga wurin Allah.'''
5 Da tok djevelen ham med sig til den hellige stad og stilte ham på templets tinde, og sa til ham:
Sa'an nan Ibilis ya kai shi tsattsarkan birni ya dora shi can kan kololuwar ginin haikali,
6 Er du Guds Sønn, da kast dig ned! for det er skrevet: Han skal gi sine engler befaling om dig, og de skal bære dig på hendene, forat du ikke skal støte din fot på nogen sten.
ya ce masa, “In kai Dan Allah ne, to dira kasa. Domin a rubuce yake cewa, 'Zai ba mala'ikunsa umarni game da kai,' kuma, 'Za su daga ka da hannuwansu, domin kada ka yi tuntube da dutse.'''
7 Jesus sa til ham: Det er atter skrevet: Du skal ikke friste Herren din Gud.
Yesu ya ce masa, “kuma a rubuce yake, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'''
8 Atter tok djevelen ham med op på et meget høit fjell og viste ham alle verdens riker og deres herlighet og sa til ham:
Kuma, sai Ibilis ya kai shi kan wani dutse mai tsawo kwarai, ya nuna masa dukan mulkokin duniya da darajarsu.
9 Alt dette vil jeg gi dig hvis du vil falle ned og tilbede mig.
Ya ce masa, “Dukan wadannan zan baka idan ka rusuna ka yi mani sujada.''
10 Da sa Jesus til ham: Bort fra mig, Satan! for det er skrevet: Herren din Gud skal du tilbede, og ham alene skal du tjene.
Sai Yesu ya ce masa, “Tafi daga nan, Shaidan! Domin a rubuce yake, 'Ka yi wa Ubangiji Allahnka sujada, shi kadai za ka bauta wa.'''
11 Da forlot djevelen ham, og se, engler kom til ham og tjente ham.
Sa'an nan Ibilis ya rabu da shi, sai kuma mala'iku suka zo suka yi masa hidima.
12 Men da han fikk høre at Johannes var kastet i fengsel, drog han bort til Galilea.
To, da Yesu ya ji an kama Yahaya, sai ya tashi zuwa kasar Galili.
13 Og han forlot Nasaret og kom og tok bolig i Kapernaum ved sjøen, i Sebulons og Naftalis landemerker,
Ya bar Nazarat, ya koma Kafarnahum da zama, can bakin tekun Galili, kan iyakar kasar Zabaluna da Naftali.
14 forat det skulde opfylles som er talt ved profeten Esaias, som sier:
Wannan ya faru domin a cika fadar annabi Ishaya cewa,
15 Sebulons land og Naftalis land ved sjøen, landet på hin side Jordan, hedningenes Galilea,
“Kasar Zabaluna da kasar Naftali, ta bakin teku, da hayin Kogin Urdun, Galili ta al'ummai!
16 det folk som satt i mørke, har sett et stort lys, og for dem som satt i dødens land og skygge, for dem er et lys oprunnet.
Mutane mazauna duhu suka ga babban haske, sannan ga wadanda ke zaune a yankin da inuwar mutuwa, haske ya keto masu.”
17 Fra den tid begynte Jesus å forkynne og si: Omvend eder; for himlenes rike er kommet nær!
Daga lokacin nan, Yesu ya fara wa'azi, yana cewa, “Ku tuba domin mulkin sama ya kusa.”
18 Men da han vandret ved den Galileiske Sjø, så han to brødre, Simon, som kalles Peter, og hans bror Andreas, i ferd med å kaste garn i sjøen; for de var fiskere;
Yana tafiya a bakin tekun Galili, sai ya ga wadansu 'yan'uwa biyu, Saminu da ake kira Bitrus, da dan'uwansa Andarawas, suna jefa taru a teku, domin su masunta ne.
19 og han sa til dem: Følg mig, så vil jeg gjøre eder til menneskefiskere!
Yesu ya ce masu, “Ku zo, ku biyo ni, zan mai da ku masuntan mutane.”
20 Og de forlot straks sine garn og fulgte ham.
Nan da nan sai suka bar tarunsu, suka bi shi.
21 Og da han gikk videre frem, så han to andre brødre, Jakob, Sebedeus' sønn, og hans bror Johannes, sitte i båten med sin far Sebedeus, i ferd med å bøte sine garn, og han kalte dem.
Da Yesu ya ci gaba da tafiya, sai ya ga wadansu mutum biyu, su kuma 'yan'uwa ne, Yakubu dan Zabadi, da dan'uwansa Yahaya, suna cikin jirgi tare da mahaifinsu Zabadi, suna gyaran tarunsu. Sai ya kira su.
22 Og de forlot straks båten og sin far og fulgte ham.
Nan take suka bar mahaifinsu da jirgin, suka bi shi.
23 Og Jesus gikk omkring i hele Galilea og lærte folket i deres synagoger og forkynte evangeliet om riket og helbredet all sykdom og all skrøpelighet blandt folket,
Yesu ya zazzaga dukan kasar Galili, yana koyarwa a majami'unsu, yana shelar bisharar mulkin, yana kuma warkar da kowace cuta da rashin lafiya a cikin mutane.
24 og ryktet om ham kom ut over hele Syria, og de førte til ham alle dem som hadde ondt og led av alle slags sykdommer og plager, både besatte og månesyke og verkbrudne, og han helbredet dem.
Labarinsa ya bazu a cikin dukan kasar Suriya, kuma mutanen suka kakkawo masa dukan marasa lafiya, masu fama da cuta iri iri, da masu shan azaba, da kuma masu aljannu, da masu farfadiya, da shanyayyu. Yesu ya warkar da su.
25 Og meget folk fulgte ham fra Galilea og Dekapolis og Jerusalem og Judea og landet hinsides Jordan.
Taro masu yawa suka bi shi daga kasar Galili, da Dikafolis, da Urushalima, da kasar Yahudiya, har ma daga hayin Urdun.

< Matteus 4 >