< Matteus 25 >
1 Da skal himlenes rike være å ligne med ti jomfruer som tok sine lamper og gikk ut for å møte brudgommen.
Sa'annan mulkin sama zai zama kamar budurwai goma da suka dauki fitilunsu domin su taryi ango.
2 Men fem av dem var dårlige og fem kloke;
Biyar daga cikin su masu hikima ne biyar kuma wawaye.
3 de dårlige tok sine lamper, men tok ikke olje med sig;
Sa'adda wawayen budurwai suka dauki fitilunsu, ba su dauki karin mai ba.
4 men de kloke tok olje i sine kanner sammen med lampene.
Amma budurwai masu hikimar suka dauki gorar mai tare da fitilunsu.
5 Men da brudgommen gav sig tid, slumret de alle inn og sov.
To da angon ya makara, dukkan su sai suka fara gyangyadi sai barci ya dauke su.
6 Men midt på natten lød der et rop: Se, brudgommen kommer! gå ham i møte!
Amma da tsakkar dare sai aka yi shela, 'Ga ango ya iso! Ku fito taryensa.
7 Da våknet alle jomfruene og gjorde sine lamper i stand.
Sai dukka budurwan nan suka tashi suka gyaggyara fitilunsu.
8 Men de dårlige sa til de kloke: Gi oss av eders olje! for våre lamper slukner.
Wawayen su ka ce da masu hikimar, 'Ku sammana kadan daga manku gama fitilunmu su na mutuwa.'
9 Men de kloke svarte: Nei; det vilde ikke bli nok både til oss og til eder; gå heller til kjøbmennene og kjøp til eder selv!
“Amma masu hikimar suka ce 'Tun da man ba zai ishe mu tare da ku ba, sai ku je gun ma su sayarwa ku sayo wa kanku.
10 Men mens de gikk bort for å kjøpe, kom brudgommen, og de som var rede, gikk inn med ham til bryllupet; og døren blev lukket.
Sa'adda suka tafi sayan man, sai angon ya shigo, kuma wadanda suke a shirye su ka shiga tare da shi bukin auren, sai aka rufe kofar.
11 Til sist kom da også de andre jomfruer og sa: Herre! herre! lukk op for oss!
Bayan dan lokaci kadan sauran budurwan suka dawo suna cewa, 'Mai gida, mai gida, bude mana kofar.'
12 Men han svarte og sa: Sannelig sier jeg eder: Jeg kjenner eder ikke.
Amma ya amsa ya ce, 'A gaskiya ina gaya maku, ni ban san ku ba.'
13 Våk derfor! for I vet ikke dagen eller timen.
Don haka sai ku lura, don baku san rana ko sa'a ba.
14 For det er likesom en mann som vilde drage utenlands og kalte sine tjenere for sig og overgav dem sin eiendom,
Domin yana kama da wani mutum da zai tafi wata kasa. Ya kira barorinsa ya ba su dukiyar sa.
15 og en gav han fem talenter, en annen to, og atter en annen en, hver efter som han var duelig til, og så drog han utenlands.
Ga wani ya ba shi talanti biyar, ga wani ya ba shi biyu, ga wani kuma ya ba shi talanti daya. kowa an bashi gwargwadon iyawarsa, sai wannan mutum ya yi tafiyar sa
16 Den som hadde fått de fem talenter, gikk da straks bort og kjøpslo med dem, og tjente fem talenter til.
nan da nan sai wanda ya karbi talanti biyar ya sa nasa a jari, ya sami ribar wasu talanti biyar.
17 Likeså den som hadde fått de to; han tjente to til.
Haka ma wanda ya karbi talanti biyu ya sami ribar wasu biyu.
18 Men den som hadde fått den ene, gikk bort og gravde i jorden og gjemte sin herres penger.
Amma bawan da ya karbi talanti dayan ya yi tafiyar sa, ya haka rami, ya binne kudin mai gidansa.
19 Lang tid derefter kom da disse tjeneres herre og holdt regnskap med dem.
To bayan tsawon lokaci sai ubangidan barorin nan ya dawo, domin yayi lissafin kudinsu.
20 Da kom han frem som hadde fått de fem talenter, og hadde med sig fem talenter til og sa: Herre! du gav mig fem talenter; se, jeg har tjent fem talenter til.
Bawan da ya karbi talanti biyar, ya kawo nasa da ribar wasu biyar. Yace, 'Maigida, ka bani talanti biyar, gashi na samo ribar karin talanti biyar.'
21 Hans herre sa til ham: Vel, du gode og tro tjener! du har vært tro over lite, jeg vil sette dig over meget; gå inn til din herres glede!
Maigidansa yace masa, 'Madalla, bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abu kadan. Zan sa ka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
22 Da kom også han frem som hadde fått de to talenter, og sa: Herre! du gav mig to talenter; se, jeg har tjent to talenter til.
Bawan da ya karbi talanti biyun, ya zo yace, 'Maigida, ka ba ni talanti biyu. Gashi kuwa na sami karin ribar wasu biyun.'
23 Hans herre sa til ham: Vel, du gode og tro tjener! du har vært tro over lite, jeg vil sette dig over meget; gå inn til din herres glede!
Ubangidansa yace masa, 'Madalla, kai bawa na gari mai aminci! Ka yi aminci akan abubuwa kadan. Zan saka akan abubuwa masu yawa. Ka shiga cikin farincikin maigidanka.'
24 Men også han kom frem som hadde fått den ene talent, og sa: Herre! jeg visste at du er en hård mann, som høster hvor du ikke sådde, og sanker hvor du ikke strødde;
Sai bawan da ya karbi talanti daya ya zo yace, 'Maigida, na san kai mai tsanani ne. Kana girbi inda baka yi shuka ba, kuma kana tattarawa inda ba ka watsa ba.
25 derfor blev jeg redd, og gikk bort og gjemte din talent i jorden; se, her har du ditt.
Na ji tsoro, don haka sai na je na boye talantinka a rami. Duba, ga abinda yake naka.'
26 Da svarte hans herre og sa til ham: Du dårlige og late tjener! du visste at jeg høster hvor jeg ikke sådde, og sanker hvor jeg ikke strødde!
Amma ubangidansa ya amsa yace, kai mugu malalacin bawa, ka san cewa ni mai girbi ne inda ban shuka ba kuma ina tattarawa inda ban zuba ba.
27 derfor burde du ha satt mine penger ut hos pengevekslerne, så hadde jeg fått mitt igjen med renter når jeg kom.
To da ba sai ka kai kudina a banki ba, da bayan na dawo da sai in karbi abina da riba.
28 Ta derfor talenten fra ham og gi den til ham som har de ti talenter!
Saboda haka ku kwace talantin daga gare shi ku baiwa mai talanti goman nan.
29 For hver den som har, ham skal gis, og han skal ha overflod; men den som ikke har, fra ham skal tas endog det han har.
Gama ga wanda yake da shi za'a kara masa har ma a yalwace za'a kara bashi. Amma ga wanda bashi da komai abinda ke nasa ma za'a kwace.
30 Og kast den unyttige tjener ut i mørket utenfor! Der skal være gråt og tenners gnidsel.
Ku jefa wannan mugun bawan marar amfani, cikin duhu mai zurfi, inda ake kuka da cizon hakora.'
31 Men når Menneskesønnen kommer i sin herlighet, og alle englene med ham, da skal han sitte på sin herlighets trone.
Sa'adda Dan mutum zai zo cikin daukakarsa da dukan Mala'iku tare da shi, sa'annan zai zauna kursiyinsa na daukaka.
32 Og alle folkeslag skal samles for hans åsyn, og han skal skille dem fra hverandre, likesom hyrden skiller fårene fra gjetene,
A gabansa za'a tattara dukkan al'ummai, zai rarraba mutanen daya'daya, kamar yadda makiyayi yake rarraba tumaki daga awaki.
33 og han skal stille fårene ved sin høire side, men gjetene ved den venstre.
Zai sa tumakin a hannunsa na dama, amma awakin a hannunsa na hagu.
34 Da skal kongen si til dem ved sin høire side: Kom hit, I min Faders velsignede! arv det rike som er beredt eder fra verdens grunnvoll blev lagt!
Sa'annan sarkin zai ce wa na hannun damarsa, 'Ku zo ku da Ubana ya albarkata, ku gaji mulkin da aka shirya maku kafin a kafa duniya.
35 For jeg var hungrig, og I gav mig å ete; jeg var tørst, og I gav mig å drikke; jeg var fremmed, og I tok imot mig;
Gama na ji yunwa kuka bani abinci; Na ji kishi kuka bani ruwa; Na yi bakunci kun bani masauki;
36 jeg var naken, og I klædde mig; jeg var syk, og I så til mig; jeg var i fengsel, og I kom til mig.
Na yi huntanci kuka tufasar dani; Na yi ciwo kuka kula dani; Ina kurkuku kuka ziyarceni.'
37 Da skal de rettferdige svare ham og si: Herre! når så vi dig hungrig og gav dig mat, eller tørst og gav dig drikke?
Sa'annan masu adalcin za su amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa muka baka abinci? Ko kana jin kishi muka baka ruwan sha?
38 Når så vi dig fremmed og tok imot dig, eller naken og klædde dig?
Kuma yaushe muka ganka kana bakunci har muka baka masauki? Ko kuma kana huntanci da muka tufatar da kai?
39 Når så vi dig syk eller i fengsel og kom til dig?
Yaushe kuma muka ganka kana ciwo ko a kurkuku har muka ziyarce ka?'
40 Og kongen skal svare og si til dem: Sannelig sier jeg eder: Hvad I har gjort imot en av disse mine minste brødre, det har I gjort imot mig.
Sa'annan Sarkin zai amsa masu yace, 'Hakika Ina gaya maku, duk abinda kuka yi wa daya mafi kakanta daga cikin 'yan'uwana a nan ni kuka yi wa.'
41 Da skal han også si til dem ved den venstre side: Gå bort fra mig, I forbannede, i den evige ild, som er beredt djevelen og hans engler! (aiōnios )
Sa'annan zai cewa wadanda suke hannunsa na hagu, 'Ku rabu da ni, ku la'anannu, ku tafi cikin wutar jahannama da aka shirya wa Shaidan da aljannunsa, (aiōnios , questioned)
42 For jeg var hungrig, og I gav gav mig ikke å ete; jeg var tørst, og I gav mig ikke å drikke;
domin ina jin yunwa baku bani abinci ba; ina jin kishi ba ku bani ruwa ba;
43 jeg var fremmed, og I tok ikke imot mig; jeg var naken, og I klædde mig ikke; jeg var syk og i fengsel, og I så ikke til mig.
Ina bakunci amma baku bani masauki ba; ina huntanci, baku tufasar da ni ba; ina ciwo kuma ina kurkuku, baku kula da ni ba.'
44 Da skal også de svare ham og si: Herre! når så vi dig hungrig eller tørst eller fremmed eller naken eller syk eller i fengsel og tjente dig ikke?
Sa'annan suma zasu amsa su ce, 'Ubangiji, yaushe muka ganka kana jin yunwa, ko kishin ruwa, ko kana bakunci, ko kana huntanci, ko ciwo, kuma a kurkuku, da bamu yi maka hidima ba?'
45 Da skal han svare dem og si: Sannelig sier jeg eder: Hvad I ikke har gjort imot en av disse minste, det har I heller ikke gjort imot mig.
Sa'annan zai amsa ya ce masu, 'Ina gaya maku hakika abin da baku iya yiwa mafi karanta daga cikin wadannan ba, ba ku yi mani ba.'
46 Og disse skal gå bort til evig pine, men de rettferdige til evig liv. (aiōnios )
Wadannan kuwa zasu tafi cikin madawwamiyar azaba amma adalai zuwa rai madawwami.” (aiōnios )