< Markus 2 >
1 Og nogen dager derefter gikk han atter inn i Kapernaum, og det spurtes at han var hjemme.
Bayan’yan kwanaki, da Yesu ya sāke shiga Kafarnahum, sai mutane suka ji labarin zuwansa gida.
2 Og mange samlet sig, så de ikke lenger fikk rum, ikke engang ved døren, og han talte ordet til dem.
Mutane suka taru da yawa har ma babu wuri, ko a bakin ƙofa ma, sai ya yi musu wa’azin bishara.
3 Og de kom til ham med en verkbrudden, som blev båret av fire mann;
Waɗansu mutum huɗu suka zo wajensa ɗauke da wani shanyayye.
4 og da de ikke kunde komme frem til ham for folketrengselen, tok de taket av der hvor han var, og brøt hull og firte ned sengen som den verkbrudne lå på.
Da ba su iya kai shi wurin Yesu ba, saboda taron, sai suka buɗe rufin gidan saman, bisa daidai inda Yesu yake. Bayan da suka huda rami, sai suka saukar da shanyayyen, kwance a kan tabarmarsa.
5 Og da Jesus så deres tro, sa han til den verkbrudne: Sønn! dine synder er dig forlatt.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Saurayi, an gafarta zunubanka.”
6 Men nogen skriftlærde satt der og tenkte i sine hjerter:
To, waɗansu malaman dokoki da suke zaune a wurin, suka yi tunani a zuciyarsu, suna cewa,
7 Hvorfor taler denne mann så? Han spotter Gud; hvem kan forlate synder uten en, det er Gud?
“Me ya sa mutumin nan yake magana haka? Yana saɓo! Wane ne zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
8 Og Jesus kjente straks i sin ånd at de tenkte så ved sig selv, og han sa til dem: Hvorfor tenker I slikt i eders hjerter?
Nan da nan, Yesu ya gane a ruhunsa abin da suke tunani a zuciyarsu, sai ya ce musu, “Me ya sa kuke tunanin waɗannan abubuwa?
9 Hvad er lettest, enten å si til den verkbrudne: Dine synder er dig forlatt, eller å si: Stå op og ta din seng og gå?
Wanne ya fi sauƙi, a ce wa shanyayyen, ‘An gafarta zunubanka,’ ko a ce, ‘Tashi, ɗauki tabarmarka ka yi tafiya’?
10 Men forat I skal vite at Menneskesønnen har makt på jorden til å forlate synder - så sier han til den verkbrudne:
Amma don ku san cewa, Ɗan Mutum yana da iko a duniya yă gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen,
11 Jeg sier dig: Stå op og ta din seng og gå hjem til ditt hus!
“Ina ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka, ka tafi gida.”
12 Og han stod op og tok straks sin seng og gikk ut for alles øine, så alle blev ute av sig selv av forundring og priste Gud og sa: Slikt har vi aldri sett.
Sai ya tashi, ya ɗauki tabarmarsa, ya yi tafiyarsa a gabansu duka. Wannan ya ba wa kowa mamaki, suka kuma ɗaukaka Allah suna cewa, “Ba mu taɓa ganin abu haka ba!”
13 Og han gikk atter ut til sjøen, og alt folket kom til ham, og han lærte dem.
Yesu ya sāke tafiya bakin tafkin. Taro mai yawa ya zo wurinsa, sai ya fara koya musu.
14 Og da han gikk videre, så han Levi, Alfeus' sønn, sitte på tollboden, og han sa til ham: Følg mig! Og han stod op og fulgte ham.
Yana cikin tafiya, sai ya ga Lawi, ɗan Alfayus zaune a inda ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.” Sai Lawi ya tashi, ya bi shi.
15 Og det skjedde at han satt til bords i hans hus; og mange toldere og syndere satt til bords med Jesus og hans disipler; for det var mange av dem, og de fulgte ham.
Yayinda Yesu yake cin abinci a gidan Lawi, sai masu karɓar haraji da “masu zunubi” da yawa, suka zo suka ci tare da shi da almajiransa, gama akwai mutane da yawa da suka bi shi.
16 Og da de skriftlærde og fariseerne så at han åt sammen med toldere og syndere, sa de til hans disipler: Han eter og drikker med toldere og syndere!
Da malaman dokoki, waɗanda su ma Farisiyawa ne, suka ga yana ci tare da masu “zunubi” da masu karɓar haraji, sai suka tambayi almajiransa, suka ce, “Me ya sa yake ci tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
17 Og da Jesus hørte det, sa han til dem: De friske trenger ikke til læge, men de som har ondt; jeg er ikke kommet for å kalle rettferdige, men for å kalle syndere.
Da jin wannan, Yesu ya ce musu, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya. Ban zo domin in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi.”
18 Og Johannes' og fariseernes disipler holdt faste, og de kom og sa til ham: Hvorfor faster Johannes' disipler og fariseernes disipler, men dine disipler faster ikke?
To, almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, sai waɗansu mutane suka zo suka tambayi Yesu, suka ce, “Yaya almajiran Yohanna da na Farisiyawa suna azumi, amma almajiranka ba sa yi?”
19 Og Jesus sa til dem: Kan vel brudesvennene faste så lenge brudgommen er hos dem? Så lenge de har brudgommen hos sig, kan de ikke faste.
Yesu ya amsa ya ce, “Yaya abokan ango za su yi azumi, sa’ad da yana tare da su? Ai, ba za su yi ba, muddin yana tare da su.
20 Men de dager skal komme da brudgommen blir tatt fra dem, og da skal de faste, på den dag.
Ai, lokaci yana zuwa da za a ɗauke musu angon. A sa’an nan ne fa za su yi azumi.
21 Ingen syr en lapp av ukrympet tøi på et gammelt klædebon, ellers river den nye lapp et stykke med sig av det gamle, og riften blir verre.
“Ba mai facin sabon ƙyalle a tsohuwar riga. In ya yi haka, sabon ƙyallen zai yage daga tsohuwar, yagewar kuwa za tă zama da muni.
22 Og ingen fyller ny vin i gamle skinnsekker; ellers vil vinen sprenge sekkene og vinen spilles og sekkene ødelegges; men ny vin i nye skinnsekker!
Ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a tsofaffin salkuna. In ya yi haka, ruwan inabin zai farfashe salkunan, yă yi hasarar ruwan inabin, salkunan kuma su lalace. A’a, yakan zuba sabon ruwan inabin a sababbin salkuna.”
23 Og det skjedde at han gikk igjennem en aker på sabbaten, og hans disipler begynte å plukke aks mens de gikk der.
Wata ranar Asabbaci, Yesu yana ratsa gonakin hatsi, sai almajiransa da suke tafiya tare da shi, suka fara kakkarya waɗansu kan hatsi.
24 Og fariseerne sa til ham: Se, hvorfor gjør de på sabbaten det som ikke er tillatt?
Farisiyawa suka ce masa, “Duba, me ya sa suke yin abin da doka ta hana a yi, a ranar Asabbaci?”
25 Og han sa til dem: Har I aldri lest hvad David gjorde da han var i nød og sultet, han selv og de som var med ham,
Ya amsa ya ce, “Ashe, ba ku taɓa karanta abin da Dawuda ya yi ba, sa’ad da shi da abokan tafiyarsa suka ji yunwa, suna kuma cikin bukata?
26 hvorledes han gikk inn i Guds hus, da Abjatar var yppersteprest, og åt skuebrødene, som ingen har lov til å ete uten prestene, og gav også dem som var med ham?
Ya shiga gidan Allah a zamanin Abiyatar babban firist, ya ci keɓaɓɓen burodin nan, ya kuma ba wa abokan tafiyarsa abin da firistoci kaɗai sukan ci bisa ga doka?”
27 Og han sa til dem: Sabbaten blev til for menneskets skyld, og ikke mennesket for sabbatens skyld.
Sai ya ce musu, “An yi Asabbaci saboda mutum ne, ba mutum saboda Asabbaci ba.
28 Så er da Menneskesønnen herre også over sabbaten.
Don haka, Ɗan Mutum Ubangiji ne, har ma da na Asabbaci.”