< Markus 10 >

1 Og han stod op derfra, og kom til Judeas landemerker og landet på hin side Jordan, og folket kom igjen sammen til ham, og han lærte dem atter, som han pleide.
Sai Yesu ya tashi daga nan ya tafi yankin Yahudiya, da kuma ƙetaren Urdun. Taron mutane suka sāke zuwa wurinsa, ya kuma koya musu kamar yadda ya saba.
2 Og fariseerne kom til ham og spurte for å friste ham: Har en mann lov til å skille sig fra sin hustru?
Waɗansu Farisiyawa suka zo suka gwada shi, ta wurin yin masa tambaya cewa, “Daidai ne bisa ga doka, mutum yă saki matarsa?”
3 Han svarte og sa til dem: Hvad har Moses foreskrevet eder?
Ya amsa ya ce, “Me Musa ya umarce ku?”
4 De sa: Moses har gitt lov til å skrive et skilsmissebrev og skille sig fra henne.
Suka ce, “Musa ya ba da izini mutum yă rubuta takardar saki, yă kuma kore ta.”
5 Men Jesus sa til dem: For eders hårde hjertes skyld har han skrevet eder dette bud.
Yesu ya ce, “Saboda taurin kanku ne, Musa ya rubuta muku wannan doka.
6 Men fra skapningens begynnelse skapte Gud dem til mann og kvinne.
Amma a farkon halitta, Allah ya ‘halicce su miji da mace.’
7 Derfor skal mannen forlate sin far og mor og holde sig til sin hustru,
‘Saboda wannan dalili, mutum zai bar mahaifinsa da mahaifiyarsa, yă manne wa matarsa,
8 og de to skal være ett kjød. Så er de da ikke lenger to, men ett kjød.
su biyun kuma za su zama jiki ɗaya.’Saboda haka, su ba mutum biyu ba ne, amma mutum ɗaya.
9 Derfor, det som Gud har sammenføiet, det skal et menneske ikke adskille.
Domin haka, abin da Allah ya haɗa, kada mutum yă raba.”
10 Og da de var kommet inn i huset, spurte disiplene ham atter om dette.
Da suna cikin gida kuma, sai almajiran suka tambayi Yesu game da wannan.
11 Og han sa til dem: Den som skiller sig fra sin hustru og gifter sig med en annen, han gjør sig skyldig i hor mot henne,
Ya amsa ya ce, “Duk wanda ya saki matarsa, ya auri wata, yana da laifin aikata zina a kan matar da ya saki.
12 og dersom hustruen skiller sig fra sin mann og gifter sig med en annen, driver hun hor.
In kuma ta saki mijinta ta auri wani, ta yi zina ke nan.”
13 Og de bar små barn til ham, forat han skulde røre ved dem; men disiplene truet dem som bar dem.
Mutane suka kawo ƙananan yara wurin Yesu don yă taɓa su, amma almajiran suka kwaɓe su.
14 Men da Jesus så det, blev han vred og sa til dem: La de små barn komme til mig, hindre dem ikke! for Guds rike hører sådanne til.
Da Yesu ya ga haka, sai ya yi fushi, ya ce musu, “Ku bar yara ƙanana su zo wurina, kada ku hana su, gama mulkin Allah na irin waɗannan ne.
15 Sannelig sier jeg eder: Den som ikke tar imot Guds rike som et lite barn, han skal ingenlunde komme inn i det.
Gaskiya nake gaya muku, duk wanda bai karɓi mulkin Allah kamar ƙaramin yaro ba, ba zai taɓa shiga mulkin ba.”
16 Og han tok dem i favn og la sine hender på dem og velsignet dem.
Sai ya ɗauki yaran a hannuwansa, ya ɗibiya musu hannuwansa, ya kuma albarkace su.
17 Og da han gikk ut på veien, kom en løpende og falt på kne for ham og spurte ham: Gode mester! hvad skal jeg gjøre for å arve evig liv? (aiōnios g166)
Da Yesu ya kama hanya, sai wani mutum ya ruga da gudu ya zo wajensa, ya durƙusa a gabansa ya ce, “Malam nagari, me zan yi domin in gāji rai madawwami?” (aiōnios g166)
18 Men Jesus sa til ham: Hvorfor kaller du mig god? Ingen er god uten én, det er Gud.
Yesu ya amsa ya ce, “Don me kake ce da ni mai nagarta? Ai, ba wani nagari, sai Allah kaɗai.
19 Budene kjenner du: Du skal ikke drive hor, du skal ikke slå ihjel, du skal ikke stjele, du skal ikke si falskt vidnesbyrd, du skal ikke frata nogen hvad hans er, hedre din far og din mor.
Ka san dokokin da suka ce, ‘Kada ka yi kisankai, kada ka yi zina, kada ka yi sata, kada ka ba da shaida ta ƙarya, kada ka cuci wani, ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka.’”
20 Men han sa til ham: Mester! alt dette har jeg holdt fra min ungdom av.
Mutumin ya ce, “Malam, ai, tun ina yaro na kiyaye duk waɗannan.”
21 Da så Jesus på ham og fikk ham kjær og sa til ham: Ett fattes dig; gå bort, selg alt det du har, og gi det til de fattige, så skal du få en skatt i himmelen; kom så og følg mig!
Yesu ya kalle shi da ƙauna ya ce, “Abu ɗaya ka rasa, ka tafi ka sayar da duk abin da kake da shi, ka ba wa matalauta, za ka kuwa sami dukiya a sama. Sa’an nan ka zo ka bi ni.”
22 Men han blev ille til mote over den tale og gikk bedrøvet bort; for han var meget rik.
Da jin wannan, sai mutumin ya ɓata fuskarsa, ya tafi da baƙin ciki, gama yana da arziki sosai.
23 Og Jesus så sig om og sa til sine disipler: Hvor vanskelig det vil være for de rike å komme inn i Guds rike!
Yesu ya dudduba, sai ya ce wa almajiransa, “Yana da wuya fa masu arziki su shiga mulkin Allah!”
24 Disiplene blev forferdet over hans ord. Da tok Jesus atter til orde og sa til dem: Barn! hvor vanskelig det er for dem som setter sin lit til sin rikdom, å komme inn i Guds rike!
Almajiransa suka yi mamakin kalmominsa. Amma Yesu ya sāke ce musu, “’Ya’yana, yana da wuya fa a shiga mulkin Allah!
25 Det er lettere for en kamel å gå gjennem et nåleøie enn for en rik å gå inn i Guds rike.
Ya fi sauƙi raƙumi yă shiga ta kafar allura, da mai arziki yă shiga mulkin Allah.”
26 Da blev de ytterlig forferdet og sa til hverandre: Hvem kan da bli frelst?
Almajiran suka yi mamaki ƙwarai, suka ce wa juna, “To, wa zai sami ceto ke nan?”
27 Jesus så på dem og sa: For mennesker er det umulig, men ikke for Gud; for alt er mulig for Gud.
Yesu ya kalle su ya ce, “Ga mutum kam, wannan ba mai yiwuwa ba ne, amma ga Allah, wannan mai yiwuwa ne; dukan abubuwa masu yiwuwa ne ga Allah.”
28 Peter tok til orde og sa til ham: Se, vi har forlatt alt og fulgt dig.
Bitrus ya ce, “Mun bar kome domin mu bi ka!”
29 Jesus svarte og sa: Sannelig sier jeg eder: Det er ingen som har forlatt hus eller brødre eller søstre eller mor eller far eller barn eller akrer for min skyld og for evangeliets skyld,
Yesu ya amsa ya ce, “Gaskiya nake gaya muku, babu wanda zai bar gida, ko’yan’uwa maza da mata, ko mahaifiya, ko mahaifi, ko’ya’ya, ko gonaki saboda ni, da kuma bishara,
30 uten at han skal få hundrefold igjen, nu her i tiden hus og brødre og søstre og mødre og barn og akrer under forfølgelser, og i den kommende verden evig liv. (aiōn g165, aiōnios g166)
sa’an nan yă kāsa samun ninkinsu ɗari a zamanin yanzu (na gidaje, da’yan’uwa mata, da’yan’uwa maza, da uwaye, da’ya’ya, da gonaki amma tare da tsanani) a lahira kuma yă sami rai madawwami. (aiōn g165, aiōnios g166)
31 Men mange som er de første, skal bli de siste, og de siste de første.
Amma da yawa da suke na farko, za su zama na ƙarshe, na ƙarshe kuma, za su zama na farko.”
32 Men de var på veien op til Jerusalem, og Jesus gikk foran dem, og de var forferdet, og de som fulgte med, fryktet. Og han tok atter de tolv til sig og begynte å si dem hvorledes det skulde gå ham:
Suna haurawa a hanyarsu zuwa Urushalima ke nan, Yesu yana a gaba, almajiran suna bin sa suna mamaki, waɗanda suke bi kuma suna ji tsoro. Ya sāke kai Sha Biyun nan gefe, ya gaya musu abin da zai faru da shi.
33 Se, vi går op til Jerusalem, og Menneskesønnen skal overgis til yppersteprestene og de skriftlærde, og de skal dømme ham til døden og overgi ham til hedningene,
Ya ce, “Za mu haura zuwa Urushalima, za a bashe Ɗan Mutum, ga manyan firistoci da malaman dokoki. Za su yi masa hukuncin kisa, a kuma ba da shi ga Al’ummai,
34 og de skal spotte ham og spytte på ham og hudstryke ham og slå ham ihjel, og tre dager efter skal han opstå.
waɗanda za su yi masa ba’a, su tofa masa miyau, su yi masa bulala, su kuma kashe shi. Bayan kwana uku kuma yă tashi.”
35 Da gikk Jakob og Johannes, Sebedeus' sønner, til ham og sa: Mester, vi vil gjerne at du skal gjøre for oss det vi ber dig om.
Sai Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi maza suka zo wurinsa suka ce, “Malam, muna so ka yi mana duk abin da muka roƙa.”
36 Han sa til dem: Hvad vil I da at jeg skal gjøre for eder?
Ya tambaye su ya ce, “Me kuke so in yi muku?”
37 De sa til ham: Gi oss at den ene av oss må sitte ved din høire og den andre ved din venstre side i din herlighet!
Suka amsa suka ce, “Ka bar ɗayanmu yă zauna a damarka, ɗayan kuma a hagunka, a cikin ɗaukakarka.”
38 Men Jesus sa til dem: I vet ikke hvad det er I ber om. Kan I drikke den kalk jeg drikker, eller døpes med den dåp jeg døpes med?
Yesu ya ce, “Ba ku san abin da kuke roƙo ba. Za ku iya shan kwaf da zan sha, ko a yi muku baftisma da baftismar da aka yi mini?”
39 De sa til ham: Det kan vi. Men Jesus sa til dem: Den kalk jeg drikker, skal I drikke, og den dåp jeg døpes med, skal I døpes med;
Suka ce, “Za mu iya.” Yesu ya ce musu, “Za ku sha kwaf da zan sha, a kuma yi muku baftisma da aka yi mini,
40 men å sitte ved min høire eller ved min venstre side, det tilkommer det ikke mig å gi nogen, men det gis dem som det er beredt.
amma zama a damana ko haguna, ba ni nake ba da izinin ba. Waɗannan wurare na waɗanda aka riga aka shirya musu ne.”
41 Og da de ti hørte dette, begynte de å harmes på Jakob og Johannes.
Da sauran goman suka ji wannan, sai suka yi fushi da Yaƙub da Yohanna.
42 Da kalte Jesus dem til sig og sa: I vet at de som gjelder for å være fyrster, hersker over sine folk, og deres stormenn bruker makt over dem.
Yesu ya kira su ya ce musu, “Kun sani waɗanda aka san su da mulkin al’ummai sukan nuna musu iko, hakimansu ma sukan gasa musu iko.
43 Men så er det ikke blandt eder; den som vil bli stor blandt eder, han skal være eders tjener,
Ba haka ya kamata yă zama da ku ba. A maimakon, duk wanda yake so yă zama babba a cikinku, dole yă zama bawanku.
44 og den som vil bli den første blandt eder, han skal være alles træl;
Duk wanda kuma yake so yă zama na farko, dole yă zama bawan kowa.
45 for Menneskesønnen er heller ikke kommet for å la sig tjene, men for selv å tjene og gi sitt liv til en løsepenge for mange.
Gama ko Ɗan Mutum ma, bai zo domin a bauta masa ba, amma don yă yi bauta, yă kuma ba da ransa fansa saboda mutane da yawa.”
46 Og de kom til Jeriko; og da han gikk ut fra Jeriko med sine disipler og meget folk, satt Timeus' sønn, Bartimeus, en blind tigger, ved veien,
Sai suka iso Yeriko. Sa’ad da Yesu da almajiransa tare da taro mai yawa suke barin birnin, wani makaho da ake kira Bartimawus kuwa (wato, “ɗan Timawus”), yana zaune a gefen hanya yana bara.
47 og da han hørte at det var Jesus fra Nasaret, begynte han å rope: Jesus, du Davids sønn! miskunn dig over mig!
Da ya ji cewa Yesu Banazare ne, sai ya ɗaga murya, yana cewa, “Yesu Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
48 Og mange truet ham at han skulde tie; men han ropte enda meget mere: Du Davids sønn! miskunn dig over mig!
Mutane da yawa suka kwaɓe shi, suka ce yă yi shiru, amma ya ƙara ɗaga murya yana cewa, “Ɗan Dawuda, ka yi mini jinƙai!”
49 Og Jesus stod stille og sa: Kall ham hit! Og de kalte på den blinde og sa til ham: Vær frimodig, stå op! han kaller på dig.
Yesu ya tsaya ya ce, “Ku kira shi.” Sai suka kira makahon suka ce, “Ka yi farin ciki! Tashi tsaye! Yana kiranka.”
50 Og han kastet sin kappe av sig og sprang op og kom til Jesus.
Ya jefar da mayafinsa waje ɗaya, ya yi wuf, ya zo wurin Yesu.
51 Og Jesus tok til orde og sa til ham: Hvad vil du jeg skal gjøre for dig? Den blinde sa til ham: Rabbuni! at jeg må få mitt syn igjen!
Yesu ya tambaye shi ya ce, “Me kake so in yi maka?” Makahon ya ce, “Rabbi, ina so in sami ganin gari.”
52 Da sa Jesus til ham: Gå bort! din tro har frelst dig. Og straks fikk han sitt syn igjen og fulgte ham på veien.
Yesu ya ce, “Je ka, bangaskiyarka ta warkar da kai.” Nan da nan, ya sami ganin gari, ya kuma bi Yesu suka tafi.

< Markus 10 >