< Lukas 8 >
1 Og det skjedde derefter at han drog omkring fra by til by og fra landsby til landsby og forkynte evangeliet om Guds rike, og de tolv var med ham,
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 og likeså nogen kvinner som var helbredet for onde ånder og sykdommer: Maria med tilnavnet Magdalena, som syv onde ånder var faret ut av,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 og Johanna, som var gift med Kuzas, Herodes' foged, og Susanna og mange andre, som tjente dem med det de eide.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 Da nu meget folk strømmet sammen, og de som bodde omkring i byene, drog ut til ham, sa han i en lignelse:
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 En såmann gikk ut for å så sin sæd, og da han sådde, falt noget ved veien; og det blev trådt ned, og himmelens fugler åt det op.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 Og noget falt på stengrunn; og da det var vokset op, visnet det, fordi det ikke hadde væte.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 Og noget falt midt iblandt torner; og tornene vokste op med og kvalte det.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 Og noget falt i god jord; og det vokste op og bar frukt i hundre fold. Da han sa dette, ropte han: Den som har ører å høre med, han høre!
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 Men hans disipler spurte ham hvad denne lignelse skulde bety.
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 Han sa da: Eder er det gitt å få vite Guds rikes hemmeligheter; men de andre gis det i lignelser, forat de skal se og dog ikke se, og høre og dog ikke forstå.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Men dette er lignelsen: Sæden er Guds ord.
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 De ved veien er de som hører det; så kommer djevelen og tar ordet bort fra deres hjerte, forat de ikke skal tro og bli frelst.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 De på stengrunn er de som tar imot ordet med glede når de hører det; men de har ikke rot; de tror til en tid, og i prøvelsens stund faller de fra.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 Det som falt iblandt torner, det er de som hører, og mens de vandrer under bekymringer og rikdom og livets lyst, kveles de, og bærer ikke fullmoden frukt.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 Men det i den gode jord, det er de som hører ordet og holder det fast i et vakkert og godt hjerte og bærer frukt i tålmodighet.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 Men ingen som tender et lys, skjuler det med et kar eller setter det under en seng; han setter det i en stake, forat de som kommer inn, kan se lyset.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 For det er ingen ting skjult som ikke skal bli åpenbar, og ingen ting dulgt som ikke skal bli kjent og komme for dagen.
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Se derfor til hvorledes I hører! for den som har, ham skal gis, og den som ikke har, fra ham skal endog tas det han tykkes sig å ha.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Men hans mor og hans brødre kom til ham, og de kunde ikke nå frem til ham for folket.
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 Det blev da meldt ham: Din mor og dine brødre står utenfor og vil gjerne få se dig.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 Men han svarte og sa til dem: Min mor og mine brødre er disse som hører Guds ord og gjør efter det.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 Og det skjedde en av dagene at han gikk ut i en båt, og hans disipler med ham, og han sa til dem: La oss fare over til hin side av sjøen! Og de la fra land.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 Men mens de seilte, sovnet han; og det fór en stormvind ned over sjøen, og båten fyltes, og de var i fare.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 Da gikk de til ham og vekket ham op og sa: Mester! mester! vi går under! Men han stod op og truet vinden og bølgene; og de la sig, og det blev blikkstille.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 Og han sa til dem: Hvor er eders tro? Men de blev forferdet og undret sig og sa til hverandre: Hvad er da dette for en, som endog byder vindene og vannet, og de er ham lydige?
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 Og de seilte frem til gergesenernes bygd, som er rett imot Galilea.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 Da han var gått i land, møtte det ham en mann fra byen, som var besatt av onde ånder; han hadde ikke hatt klær på sig i lang tid, og han holdt sig ikke i hus, men i gravene.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 Da han så Jesus, satte han i et skrik og falt ned for ham og sa med høi røst: Hvad har jeg med dig å gjøre, Jesus, du den høieste Guds Sønn? Jeg ber dig, pin mig ikke!
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 For han bød den urene ånd fare ut av mannen; i lange tider hadde den revet ham med sig, og han blev bundet med lenker og fotjern og holdt under vakt; og han sønderrev båndene og blev drevet av den onde ånd ut i ørkenene.
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 Men Jesus spurte ham: Hvad er ditt navn? Han svarte: Legion! For mange onde ånder var faret i ham.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 Og de bad ham at han ikke vilde byde dem fare ned i avgrunnen. (Abyssos )
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos )
32 Men det var på stedet en stor svinehjord, som gikk og beitet i fellet, og de bad ham at han vilde gi dem lov til å fare inn i dem; og han gav dem lov.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 Så fór da de onde ånder ut av mannen og inn i svinene; og hjorden styrtet sig ut over stupet ned i sjøen og druknet.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 Men da gjæterne så det som hadde hendt, tok de flukten, og fortalte det i byen og i bygden.
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 Folk kom da ut for å se hvad som hadde hendt, og de kom til Jesus, og fant mannen som de onde ånder var faret ut av, sittende påklædd og ved sans og samling ved Jesu føtter, og de blev forferdet.
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 Men de som hadde sett det, fortalte dem hvorledes den besatte var blitt frelst.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 Og hele folkemengden i gergesenernes bygd bad ham dra bort fra dem; for det var en stor frykt over dem. Og han gikk i båten og vendte tilbake igjen.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Mannen som de onde ånder var faret ut av, bad om å få være med ham. Men han sendte ham fra sig og sa:
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 Gå hjem til ditt hus og fortell hvor store ting Gud har gjort imot dig! Og han gikk bort og kunngjorde over hele byen hvor store ting Jesus hadde gjort imot ham.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 Men da Jesus kom tilbake, tok folket imot ham; for alle ventet på ham.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 Og se, det kom en mann ved navn Jairus, som var forstander for synagogen, og han falt ned for Jesu føtter og bad ham komme inn i hans hus;
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 for han hadde en eneste datter, omkring tolv år gammel, og hun lå for døden. Da nu Jesus gikk avsted, trengte folket sig inn på ham;
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 og en kvinne som hadde hatt blodsott i tolv år og hadde kostet på læger alt det hun skulde leve av, og ikke kunnet bli helbredet av nogen,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 hun trådte til bakfra og rørte ved det ytterste av hans klædebon, og straks stanset hennes blodsott.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 Og Jesus sa: Hvem var det som rørte ved mig? Men da alle nektet, sa Peter og de som var med ham: Mester! Folket trykker og trenger dig jo!
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 Men Jesus sa: Det var nogen som rørte ved mig; for jeg kjente at en kraft gikk ut fra mig.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 Da nu kvinnen så at det ikke var skjult det hun hadde gjort, kom hun skjelvende og falt ned for ham og fortalte ham, så hele folket hørte det, av hvad grunn hun rørte ved ham, og hvorledes hun straks blev helbredet.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 Da sa han til henne: Datter! din tro har frelst dig; gå bort i fred!
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 Mens han ennu taler, kommer en fra synagoge-forstanderen og sier til ham: Din datter er død; umak ikke mesteren!
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 Men da Jesus hørte det, svarte han ham: Frykt ikke, bare tro, så skal hun bli frelst!
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 Da han nu kom inn i huset, lot han ingen gå inn med sig uten Peter og Johannes og Jakob og pikens far og mor.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 Og alle gråt og jamret sig over henne; men han sa: Gråt ikke! hun er ikke død, hun sover.
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 Og de lo ham ut; for de visste at hun var død.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 Men han tok henne ved hånden og ropte: Pike, stå op!
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 Da vendte hennes ånd tilbake, og hun stod straks op; og han bød at de skulde gi henne mat.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 Og hennes foreldre blev forferdet; men han bød dem at de ikke skulde tale til nogen om det som var skjedd.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.