< Lukas 5 >

1 Men det skjedde da folket trengte sig inn på ham og hørte Guds ord, og han stod ved Gennesaret-sjøen,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 da så han to båter ligge ved sjøen; men fiskerne var gått ut av dem og skyllet garnene.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Han gikk da ut i en av båtene, som tilhørte Simon, og bad ham legge litt ut fra land; og han satte sig i båten og lærte folket.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Men da han holdt op å tale, sa han til Simon: Legg ut på dypet, og kast eders garn ut til en drett!
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Og Simon svarte ham: Mester! vi har strevet hele natten og ikke fått noget; men på ditt ord vil jeg kaste ut garnene.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Og de gjorde så, og fanget en stor mengde fisk; og deres garn revnet.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Og de vinket til sine lagsbrødre i den andre båt, at de skulde komme og ta i med dem; og de kom, og de fylte begge båtene, så de holdt på å synke.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Men da Simon Peter så det, falt han ned for Jesu knær og sa: Herre, gå fra mig! for jeg er en syndig mann.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 For redsel kom over ham og alle dem som var med ham, for den fiskedrett som de hadde fått;
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 likeså Jakob og Johannes, Sebedeus' sønner, som var i lag med Simon. Og Jesus sa til Simon: Frykt ikke! fra nu av skal du fange mennesker.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Da rodde de båtene i land og forlot alt og fulgte ham.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Og det skjedde da han var i en av byene, se, da var det en mann som var full av spedalskhet; og da han så Jesus, falt han ned på sitt ansikt, bad ham og sa: Herre! om du vil, kan du rense mig.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Og Jesus rakte hånden ut, rørte ved ham og sa: Jeg vil; bli ren! Og straks forlot spedalskheten ham.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 Og han bød ham at han ikke skulde si det til nogen; men gå og te dig for presten og ofre for din renselse, således som Moses har påbudt, til et vidnesbyrd for dem!
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Men ordet om ham kom ennu mere ut, og meget folk kom sammen for å høre og for å bli helbredet for sine sykdommer;
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 men han drog sig tilbake til øde steder og var der i bønn.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Og det skjedde en av dagene mens han lærte, og der satt fariseere og lovlærere som var kommet fra hver by i Galilea og Judea og fra Jerusalem, og Herrens kraft var hos ham til å helbrede:
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 se, da kom nogen menn som bar en mann på en seng, han var verkbrudden; og de søkte å få ham inn og legge ham ned foran ham.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Og da de for folketrengselen ikke fant nogen vei til å få ham inn, steg de op på taket og firte ham med sengen ned mellem takstenene midt foran Jesus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Og da han så deres tro, sa han: Menneske! dine synder er dig forlatt.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Da begynte de skriftlærde og fariseerne å tenke så: Hvem er denne mann, som taler bespottelser? Hvem kan forlate synder uten Gud alene?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Men da Jesus merket deres tanker, svarte han og sa til dem: Hvad er det I tenker i eders hjerter?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Hvad er lettest, enten å si: Dine synder er dig forlatt, eller å si: Stå op og gå?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Men forat I skal vite at Menneskesønnen har makt på jorden til å forlate synder - så sa han til den verkbrudne: Jeg sier dig: Stå op og ta din seng og gå hjem til ditt hus!
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Og straks stod han op for deres øine og tok det han lå på, og gikk hjem til sitt hus og priste Gud.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Da kom det forferdelse over dem alle, og de priste Gud, og de blev fulle av frykt og sa: Idag har vi sett utrolige ting!
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Derefter gikk han ut, og han så en tolder ved navn Levi sitte på tollboden; og han sa til ham: Følg mig!
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Og han forlot alt og stod op og fulgte ham.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Og Levi gjorde et stort gjestebud for ham i sitt hus, og der var en stor mengde toldere og andre som satt til bords med dem.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 Og fariseerne og deres skriftlærde knurret mot hans disipler og sa: Hvorfor eter og drikker I med toldere og syndere?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Og Jesus svarte og sa til dem: De friske trenger ikke til læge, men de som har ondt;
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 jeg er ikke kommet for å kalle rettferdige, men syndere til omvendelse.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 De sa til ham: Johannes' disipler holder jevnlig faste og bønn, og fariseernes disipler likeså; men dine eter og drikker.
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 Men Jesus sa til dem: Kan I vel få brudesvennene til å faste så lenge brudgommen er hos dem?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 Men de dager skal komme da brudgommen blir tatt fra dem; da skal de faste, i de dager.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Han sa også en lignelse til dem: Ingen river en lapp av et nytt klædebon og setter den på et gammelt; ellers river han det nye i sønder, og lappen av det nye passer ikke til det gamle.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Og ingen fyller ny vin i gamle skinnsekker; ellers vil den nye vin sprenge sekkene, og den selv spilles og sekkene ødelegges;
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 men ny vin skal fylles i nye skinnsekker.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Og ingen som har drukket gammel vin, har lyst på ny; han sier: den gamle er god.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Lukas 5 >