< Lukas 1 >
1 Eftersom mange har tatt sig fore å sette op en fortelling om de ting som er fullbyrdet iblandt oss,
Mutane da dayawa sun yi kokarin rubutu akan abubuwan da suka cika a tsakaninmu,
2 således som de som fra først av var øienvidner og blev ordets tjenere, har overgitt oss det,
kamar yanda suka danka mana su, wadanda tun daga farko suka zama shaidu da idanunsu kuma manzanni ne na sakon.
3 så har også jeg foresatt mig, efterat jeg nøie har gransket alt sammen fra først av, å nedskrive det i sammenheng for dig, gjæveste Teofilus,
Sabili da haka, ni ma, bayan da na yi bincike da kyau akan yanayin wadannan abubuwa tun da farko na ga ya yi kyau in rubuta wadannan abubuwa bi da bi ya mafi girmaTiyofilas.
4 forat du kan lære å kjenne hvor pålitelige de lærdommer er som du er oplært i.
Ya zama haka domin ka san gaskiyar abin da aka koya maka ne.
5 I de dager da Herodes var konge i Jødeland, var det en prest ved navn Sakarias, av Abias skifte, og han hadde en hustru av Arons døtre, og hennes navn var Elisabet.
A cikin zamanin Hirudus, Sarkin Yahudiya, akwai wani firist mai suna Zakariya, daga yankin Abija. Matarsa daga cikin yaya mata na zuriyar Haruna ce, kuma sunan ta Alisabatu ne.
6 De var begge rettferdige for Gud, og vandret ulastelig i alle Herrens bud og forskrifter.
Dukan su biyu masu adalci ne a gaban Allah; marasa zargi a tafiyarsu cikin dukan dokoki da farilan Ubangiji.
7 Og de hadde ikke barn; for Elisabet var ufruktbar, og de var begge kommet langt ut i årene.
Amma ba su da da, domin Alisabatu ba ta haihuwa, kuma a wannan lokacin dukansu sun tsufa kwarai.
8 Men det skjedde mens han gjorde prestetjeneste for Gud, da raden var kommet til hans skifte,
Ya zama kuma a lokacin da Zakariya yana gaban Allah, yana yin hidimar sa ta firist bisa ga tsari da ka'idar aikinsa.
9 at det efter preste-tjenestens sedvane tilfalt ham å gå inn i Herrens tempel og ofre røkelse;
Bisa ga al'adar zaben firist da zai yi hidima, an zabe shi ta wurin kuri'a ya shiga cikin haikalin Ubangiji domin ya kona turare.
10 og hele folkemengden stod utenfor og bad i røkofferets stund.
Dukan taron Jama'a suna addu'a a waje a sa'adda ake kona turaren.
11 Da åpenbarte en Herrens engel sig for ham og stod på høire side av røkoffer-alteret.
A lokacin, mala'ikan Ubangiji ya bayana a gare shi yana tsaye a gefen daman bagadi na turaren.
12 Og da Sakarias så ham, blev han forferdet, og frykt falt på ham.
Zakariya ya firgita sa'adda ya gan shi; tsoro ya kama shi.
13 Men engelen sa til ham: Frykt ikke, Sakarias! din bønn er hørt, og din hustru Elisabet skal føde dig en sønn, og du skal kalle ham Johannes;
Amma mala'ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya, domin an ji addu'ar ka. Matar ka Alisabatu za ta haifa maka da. Za ka kira sunansa Yahaya.
14 og han skal bli dig til glede og fryd, og mange skal glede sig over hans fødsel.
Za ka yi murna da farin ciki, kuma da yawa za su yi murna da haifuwarsa.
15 For han skal være stor for Herren, og han skal ikke drikke vin og sterk drikk, og han skal fylles med den Hellige Ånd like fra mors liv;
Domin zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba zai sha ruwan inabi ba ko wani abu mai sa maye, kuma zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun daga cikin cikin mahaifiyarsa.
16 og han skal omvende mange av Israels barn til Herren deres Gud,
Kuma mutanen Isra'ila da yawa za su juya zuwa ga Ubangiji Allahnsu.
17 og han skal gå i forveien for ham i Elias' ånd og kraft, for å vende fedres hjerter til barn og ulydige til rettferdiges sinnelag, for å berede Herren et velskikket folk.
Zai yi tafiya a gaban Unbangiji a cikin ruhu da ikon Iliya. Zai yi haka domin ya juya zuciyar Ubanni zuwa ga 'ya'yansu, domin marasa biyayya su yi tafiya a cikin tafarkin adalai. Don ya shirya wa Ubangiji mutanen da aka shirya dominsa.”
18 Og Sakarias sa til engelen: Hvorav skal jeg vite dette? Jeg er jo en gammel mann, og min hustru er langt ute i årene.
Zakariya ya ce wa mala'ikan, “Ta yaya zan san wannan? Ga shi na tsufa kuma matata tana da shekaru da yawa.”
19 Og engelen svarte ham: Jeg er Gabriel, som står for Guds åsyn, og jeg er utsendt for å tale til dig og forkynne dig dette glade budskap;
Mala'ikan ya amsa ya ce masa, “Nine Jibra'ilu, wanda ke tsaye a gaban Allah. An aiko ni in gaya maka wannan labari mai dadi.
20 og se, du skal bli målløs, og ikke kunne tale før den dag da dette skjer, fordi du ikke trodde mine ord, som skal fullbyrdes i sin tid.
Kuma duba, za ka zama bebe, ba za ka iya magana ba, sai ran da wadannan abubuwa suka cika. Ya zama haka domin ba ka gaskanta da kalmomina ba, wadanda za su cika a daidai lokacin.”
21 Og folket stod og ventet på Sakarias, og de undredes over at han blev så lenge i templet.
Sa'adda mutane suke jiran Zakariya. Sun yi mamaki yadda ya dauki lokaci sosai a cikin haikali.
22 Men da han kom ut, kunde han ikke tale til dem, og de skjønte at han hadde sett et syn i templet, og han nikket til dem, og var og blev stum.
Amma da ya fita, bai iya yin magana da su ba. Sun gane da cewa ya ga wahayi lokacin da yake cikin haikali. Ya ci gaba da yi masu alamu, ba ya magana.
23 Og det skjedde da hans tjenestedager var til ende, da drog han hjem til sitt hus.
Ya zama bayan da kwanakin hidimarsa suka kare, ya tafi gidansa.
24 Men efter disse dager blev hans hustru Elisabet fruktsommelig, og hun trakk sig tilbake i ensomhet i fem måneder, og sa:
Bayan kwanakin nan, matarsa Alisabatu ta samu juna biyu. Ta boye kanta har na watani biyar. Ta ce,
25 Så har Herren gjort med mig i de dager da han så til mig for å bortta min vanære iblandt menneskene.
“Wannan shi ne abin da Allah ya yi mani da ya dube ni domin ya dauke kunyata a gaban jama'a.”
26 Men i den sjette måned blev engelen Gabriel sendt fra Gud til en by i Galilea som heter Nasaret,
A cikin watan ta na shidda, an aiki Mala'ika Jibra'ilu daga wurin Allah zuwa wani birni a Galili mai suna Nazarat,
27 til en jomfru som var trolovet med en mann ved navn Josef, av Davids hus, og jomfruens navn var Maria.
zuwa ga wata budurwa wanda aka ba da ita ga wani mutum mai suna Yusufu. Shi dan zuriyar Dauda ne, kuma ana kiran budurwar Maryamu.
28 Og engelen kom inn til henne og sa: Vær hilset, du benådede! Herren er med dig; velsignet er du blandt kvinner!
Ya zo wurin ta ya ce, “A gaishe ki, ke da ki ke da tagomashi sosai! Ubangiji yana tare da ke.
29 Men hun blev forferdet over hans ord, og grundet på hvad dette skulde være for en hilsen.
Amma ta damu kwarai da wadannan kalmomi sai ta yi tunani ko wacce irin gaisuwa ce wannan.
30 Og engelen sa til henne: Frykt ikke, Maria! for du har funnet nåde hos Gud;
Mala'ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, domin kin samu tagomashi a wurin Allah.
31 og se, du skal bli fruktsommelig og føde en sønn, og du skal kalle ham Jesus.
Duba, za ki sami juna biyu, za ki haifi da. Za ki kira sunansa 'Yesu'.
32 Han skal være stor og kalles den Høiestes Sønn, og Gud Herren skal gi ham hans far Davids trone,
Zai zama mai girma, kuma za a ce da shi Dan Allah Madaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi kursiyin ubansa Dauda.
33 og han skal være konge over Jakobs hus evindelig, og det skal ikke være ende på hans kongedømme. (aiōn )
Zai yi mulkin dukkan gidan Yakubu har abada, kuma mulkinsa ba shi da iyaka.” (aiōn )
34 Men Maria sa til engelen: Hvorledes skal dette gå til, da jeg ikke vet av mann?
Maryamu ta ce wa mala'ikan, “Yaya wannan zai faru, tun da shike ni ban san namiji ba?”
35 Og engelen svarte henne: Den Hellige Ånd skal komme over dig, og den Høiestes kraft skal overskygge dig; derfor skal også det hellige som fødes, kalles Guds Sønn.
Mala'ikan ya amsa ya ce mata, “Ruhu Mai-tsarki zai sauko a kan ki, kuma ikon Madaukaki zai lullube ki. Sabili da haka, za a kira mai tsarkin da za ki haifa Dan Allah.
36 Og se, Elisabet, din slektning, har også undfanget en sønn i sin alderdom, og hun, som kaltes ufruktbar, er nu i sin sjette måned.
Ki kuma duba, ga 'yar'uwarki Alisabatu ta samu juna biyu a tsufanta. Watannin ta shida kenan, ita wadda aka kira ta bakarariya.
37 For ingen ting er umulig for Gud.
Gama babu abin da ba shi yiwuwa a wurin Allah.”
38 Da sa Maria: Se, jeg er Herrens tjenerinne; mig skje efter ditt ord! Og engelen skiltes fra henne.
Maryamu ta ce, “To, ni baiwar Ubangiji ce. Bari ya faru da ni bisa ga sakonka.” Sai mala'ikan ya bar ta.
39 Men Maria stod op i de dager og skyndte sig til fjellbygdene, til en by i Juda,
Sai Maryamu ta tashi da sauri a cikin kwanakin nan, zuwa kasa mai duwatsu, zuwa wani birni a Yahudiya.
40 og hun kom inn i Sakarias' hus og hilste på Elisabet.
Ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Alisabatu.
41 Og det skjedde da Elisabet hørte Marias hilsen, da sprang fosteret i hennes liv, og Elisabet blev fylt med den Hellige Ånd
Ya zama sa'adda Alisabatu ta ji gaisuwar Maryamu, sai dan da ke cikinta ya yi tsalle, an cika Alisabatu kuma da Ruhu Mai Tsarki.
42 og ropte med høi røst og sa: Velsignet er du blandt kvinner, og velsignet er ditt livs frukt!
Ta daga murya, ta ce, “Mai albarka kike a cikin mata, kuma mai albarka ne dan cikinki.
43 Og hvorledes times mig dette, at min Herres mor kommer til mig?
Kuma don me ya faru da ni da uwar Ubangijina ta ziyarce ni?
44 For se, da lyden av din hilsen nådde mitt øre, sprang fosteret i mitt liv med fryd.
Kuma duba, da na ji karar gaisuwan ki sai dan ciki na ya yi tsalle domin murna.
45 Og salig er hun som trodde; for fullbyrdes skal det som er sagt henne av Herren.
Kuma mai albarka ce wadda ta gaskanta cewa abubuwan da aka alkawarta mata daga wurin Ubangiji za su cika.
46 Da sa Maria: Min sjel ophøier Herren,
Maryamu ta ce, “Zuciyata ta yabi Ubangiji,
47 og min ånd fryder sig i Gud, min frelser,
kuma ruhu na ya yi murna da Allah mai ceto na.”
48 han som har sett til sin tjenerinnes ringhet. For se, fra nu av skal alle slekter prise mig salig,
Domin ya dubi kaskancin baiwarsa. Duba, daga yanzu, dukkan tsararraki za su ce da ni mai albarka.
49 fordi han har gjort store ting imot mig, han, den mektige, og hellig er hans navn,
Domin shi madaukaki ya yi mani manyan abubuwa, kuma sunansa Mai Tsarki ne.
50 og hans miskunn er fra slekt til slekt over dem som frykter ham.
Jinkansa ya tabbata daga tsara zuwa tsara wadanda suke girmama shi.
51 Han gjorde veldig verk med sin arm, han adspredte dem som var overmodige i sitt hjertes tanke;
Ya nuna karfinsa da hannuwansa; ya warwatsa ma su girman kai game da tunanin zuciyarsu.
52 han støtte stormenn fra deres høiseter og ophøiet de små;
Ya nakasar da magada daga kursiyoyinsu, ya kuma fifita nakasassu.
53 hungrige mettet han med gode gaver, og rikmenn lot han gå bort med tomme hender.
Ya ciyar da mayunwata da abubuwa masu kyau, amma ya aiki attajirai wofi.
54 Han tok sig av Israel, sin tjener, for å komme miskunn i hu
Ya ba da taimako ga bawan sa Isra'ila, domin ya tuna ya kuma nuna jinkai
55 - således som han talte til våre fedre - mot Abraham og hans ætt til evig tid. (aiōn )
(kamar yanda ya fada wa ubaninmu) ga Ibrahim da zuriyarsa har abada.” (aiōn )
56 Og Maria blev hos henne omkring tre måneder, og vendte så hjem igjen til sitt hus.
Maryamu ta zauna da Alisabatu tsawon watanni uku sai ta koma gidanta.
57 Men for Elisabet kom tiden da hun skulde føde, og hun fødte en sønn,
Da lokaci yayi da Alisabatu za ta haifi danta, ta kuma haifi da namiji.
58 og hennes granner og frender fikk høre at Herren hadde gjort sin miskunn stor mot henne, og de gledet sig med henne.
Makwabtanta da 'yan'uwanta sun ji cewa Ubangiji ya ribanbanya jinkansa akanta, sai suka yi murna tare da ita
59 Og det skjedde på den åttende dag, da kom de for å omskjære barnet, og de vilde kalle ham Sakarias efter hans far.
Ya zama akan rana ta takwas, sun zo domin a yi wa yaron kaciya. Da sun kira sunansa “Zakariya” kamar sunan ubansa,
60 Da tok hans mor til orde og sa: Nei, han skal hete Johannes.
amma mahaifiyarsa ta amsa ta ce, “A'a, za a kira shi Yahaya.”
61 Og de sa til henne: Men det er jo ingen i din ætt som har dette navn.
Suka ce mata, “Babu wani a cikin danginku wanda ake kira da wannan suna.”
62 De gjorde da tegn til hans far for å få vite hvad han vilde han skulde hete.
Sun nuna alama ga ubansa bisa ga yanda ya ke so a rada masa suna.
63 Og han bad om en tavle og skrev disse ord: Johannes er hans navn. Og de undret sig alle.
Ubansa ya nemi a ba shi allon rubutu, sai ya rubuta, “Sunansa Yahaya.” Dukan su suka yi mamaki kwarai da wannan.
64 Men straks blev hans munn oplatt og hans tunge løst, og han talte og lovet Gud.
Nan take, sai bakinsa ya bude kuma harshensa ya saki. Ya yi magana ya kuma yabi Allah.
65 Og det kom frykt på alle dem som bodde deromkring, og i alle Judeas fjellbygder talte de med hverandre om alle disse ting,
Tsoro ya kama dukan wadanda suke zama kewaye da su. Sai labarin ya bazu cikin dukan kasar duwatsu ta Yahudiya.
66 og alle som hørte det, la det på hjerte og sa: Hvad skal det da bli av dette barn? For Herrens hånd var med ham.
Kuma dukan wadanda suka ji su, sun ajiye su a cikin zuciyarsu, suna cewa, “To me wannan yaro zai zama ne?” Domin hannun Ubangiji yana nan tare da shi.
67 Og hans far Sakarias blev fylt med den Hellige Ånd og talte profetiske ord og sa:
Ruhu Mai-tsarki ya cika mahaifinsa Zakariya sai ya yi anabci cewa,
68 Lovet være Herren, Israels Gud, han som så til sitt folk og forløste det!
“Yabo ga Ubangiji, Allah na Isra'ila domin ya zo ya taimaki mutanen sa kuma ya yi aikin ceto domin su.”
69 Og han opreiste oss et frelsens horn i sin tjener Davids hus,
Ya ta da kahon ceto dominmu daga gidan bawansa Dauda, daga zuriyar Dauda bawansa,
70 således som han talte gjennem sine hellige profeters munn fra fordums tid av, (aiōn )
kamar yadda ya fada ta bakin annabawansa tsarkaka tun zamanin zamanai. (aiōn )
71 en frelse fra våre fiender og fra alle deres hånd som hater oss,
Zai kawo mana ceto daga magabtan mu da kuma daga hannun makiyanmu.
72 for å gjøre miskunn mot våre fedre og komme sin hellige pakt i hu,
Zai yi haka domin ya nuna jinkai ga ubaninmu ya kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 den ed han svor Abraham, vår far,
rantsuwar da ya fada wa ubanmu Ibrahim.
74 for å fri oss av våre fienders hånd og gi oss å tjene ham uten frykt
Ya rantse zai yardar mana, bayan da an kubutar da mu daga hannun makiyanmu, mu bauta masa ba tare da tsoro ba,
75 i hellighet og rettferdighet for hans åsyn alle våre dager.
a cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakin ranmu.
76 Men også du, barn, skal kalles den Høiestes profet; for du skal gå frem for Herrens åsyn for å rydde hans veier,
I, kai kuma, yaro, za a kira ka annabi na Madaukaki, domin za ka tafi gaban fuskar Ubangiji ka shirya hanyoyinsa, ka shirya mutane domin zuwansa,
77 for å lære hans folk frelse å kjenne ved deres synders forlatelse
domin ba mutanensa ilimin ceto ta wurin gafarar zunubansu.
78 for vår Guds miskunnelige hjertelags skyld, som lot solopgang fra det høie gjeste oss,
Wannan zai faru ne domin girman jinkan Allahnmu, sabili da hasken rana daga bisa za ya zo wurinmu,
79 for å lyse for dem som sitter i mørke og dødsskygge, for å styre våre føtter inn på fredens vei.
domin haskakawa akan wadanda ke zaune a cikin duhu da kuma cikin inuwar mutuwa. Zai yi hakan nan domin ya kiyaye kafafunmu zuwa hanyar salama.
80 Men barnet vokste og blev sterkt i ånden, og han var i ødemarkene til den dag da han blev ført frem for Israel.
Yaron ya yi girma ya kuma zama kakkarfa a cikin ruhu, yana kuma cikin jeji sai ranar bayyanuwarsa ga Isra'ila.