< 3 Mosebok 24 >

1 Og Herren talte til Moses og sa:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Byd Israels barn at de skal la dig få ren olje av støtte oliven til lysestaken, så lampene kan settes op til enhver tid.
“Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
3 Utenfor vidnesbyrdets forheng i sammenkomstens telt skal Aron alltid holde dem i stand fra aften til morgen for Herrens åsyn; det skal være en evig lov for eder, fra slekt til slekt.
Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
4 På lysestaken av rent gull skal han alltid holde lampene i stand for Herrens åsyn.
Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
5 Du skal ta fint mel og bake tolv kaker av det; hver kake skal være to tiendedeler av en efa.
“Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
6 Og du skal legge dem i to rader, seks i hver rad, på bordet av rent gull for Herrens åsyn.
A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
7 Og du skal legge ren virak på hver rad, og den skal være et ihukommelses-offer for brødene, et ildoffer for Herren.
Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
8 På hver sabbatsdag skal brødene gjennem alle tider legges frem for Herrens åsyn; det skal være en gave fra Israels barn - en evig pakt.
Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
9 De skal høre Aron og hans sønner til, og de skal ete dem på et hellig sted; for de er høihellige og er hans del av Herrens ildoffer - en evig rettighet.
Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
10 En mann som var sønn av en israelittisk kvinne, men hadde en egypter til far, gikk engang ut blandt Israels barn. Da kom den israelittiske kvinnes sønn og en israelittisk mann i trette med hverandre i leiren,
To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
11 og den israelittiske kvinnes sønn spottet Herrens navn og bannet det, og de førte ham til Moses. Hans mor hette Selomit, Dibris datter, av Dans stamme.
Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
12 De satte ham fast, forat de kunde få avgjørelse ved et ord fra Herren.
Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
13 Og Herren talte til Moses og sa:
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
14 Før spotteren utenfor leiren, og alle de som hørte det, skal legge sine hender på hans hode, og hele menigheten skal stene ham.
“Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
15 Og du skal tale til Israels barn og si: Når nogen banner sin Gud, skal han lide for sin synd.
Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
16 Og den som spotter Herrens navn, skal late livet, hele menigheten skal stene ham; enten det er en fremmed eller en innfødt, skal han stenes når han spotter Herrens navn.
duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
17 Når en slår et menneske ihjel, skal han late livet.
“‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
18 Men den som slår et stykke fe ihjel, skal godtgjøre det, liv for liv.
Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
19 Når nogen volder sin næste mén på hans legeme, skal der gjøres det samme med ham som han selv har gjort:
Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
20 brudd for brudd, øie for øie, tann for tann; det samme mén som han volder en annen, skal han selv få.
karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
21 Den som slår et stykke fe ihjel, skal godtgjøre det; men den som slår et menneske ihjel, skal late livet.
Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
22 En og samme rett skal gjelde for eder, den skal gjelde for den fremmede som for den innfødte; for jeg er Herren eders Gud.
Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
23 Og Moses sa dette til Israels barn, og de førte spotteren utenfor leiren og stenet ham - Israels barn gjorde som Herren hadde befalt Moses.
Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< 3 Mosebok 24 >