< 3 Mosebok 18 >

1 Og Herren talte til Moses og sa:
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Tal til Israels barn og si til dem: Jeg er Herren eders Gud.
“Yi wa Isra’ilawa magana ka kuma faɗa musu cewa, ‘Ni ne Ubangiji Allahnku.
3 I skal ikke gjøre som de gjør i Egyptens land, som I bodde i, og I skal ikke gjøre som de gjør i Kana'ans land, som jeg vil føre eder til, og I skal ikke vandre efter deres skikker.
Kada ku yi yadda suke yi a Masar inda da kuke zama, kuma ba a ku yi kamar yadda suke yi a ƙasar Kan’ana inda nake kawo ku ba. Kada ku yi yadda suke yin abubuwa.
4 I skal gjøre efter mine bud, og I skal holde mine lover, så I følger dem; jeg er Herren eders Gud.
Dole ku kiyaye dokokina kuma ku lura ku bi farillaina. Ni ne Ubangiji Allahnku.
5 Og I skal holde mine lover og mine bud, for det menneske som gjør efter dem, skal leve ved dem; jeg er Herren.
Ku kiyaye farillaina da dokokina, gama mutumin da ya aikata waɗannan abubuwa zai rayu ta wurinsu. Ni ne Ubangiji.
6 Ingen av eder skal røre ved nogen kvinne av sin nære slekt for å ha omgang med henne; jeg er Herren.
“‘Kada wani ya kusaci wani dangi na kusa don yă yi jima’i. Ni ne Ubangiji.
7 Din fars og din mors leie skal du ikke vanære; hun er din mor, du skal ikke ha omgang med henne.
“‘Kada ka ƙasƙantar da mahaifinka ta wurin kwana da mahaifiyarka. Ita mahaifiyarka ce; kada ka yi jima’i da ita.
8 Din stedmor skal du ikke ha omgang med; hun er din fars hustru.
“‘Kada ka yi jima’i da matar mahaifinka, wannan zai ƙasƙantar da mahaifinka.
9 Din søster, enten det er din fars datter eller din mors datter, enten hun er født hjemme eller født ute, skal du ikke ha omgang med.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwarka, ko’yar mahaifinka ko’yar mahaifiyarka, ko an haife ta a gida ɗaya da kai ko kuwa a wani wuri dabam.
10 Din sønnedatter eller din datterdatter skal du ikke ha omgang med; for det er ditt eget kjød.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar ɗanka ko’yar’yarka, wannan zai ƙasƙantar da kai.
11 Din stedmors datter, som også er din fars datter, skal du ikke ha omgang med; hun er din søster.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar matar mahaifinka wadda aka haifa wa mahaifinka; ita’yar’uwarka ce.
12 Din fars søster skal du ikke ha omgang med; hun er din fars nære slekt.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifinka, ita dangin mahaifinka ne na kusa.
13 Din mors søster skal du ikke ha omgang med; for hun er din mors nære slekt.
“‘Kada ka yi jima’i da’yar’uwar mahaifiyarka, domin ita dangin mahaifiyarka ce na kusa.
14 Din farbrors leie skal du ikke vanære, hans hustru skal du ikke komme for nær; hun er din fars søster.
“‘Kada ka ƙasƙantar da ɗan’uwan mahaifinka ta wurin kusaci matarsa don ka yi jima’i da ita, ita bābarka ce.
15 Din sønnekone skal du ikke ha omgang med; hun er din sønns hustru, du skal ikke ha omgang med henne.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗanka. Ita matar ɗanka ne; kada ka yi jima’i da ita.
16 Din brors hustru skal du ikke ha omgang med - ikke vanære din brors leie.
“‘Kada ka yi jima’i da matar ɗan’uwanka; wannan zai ƙasƙanta ɗan’uwanka.
17 Du skal ikke ha omgang med en kvinne og tillike med hennes datter; hennes sønnedatter eller hennes datterdatter skal du heller ikke ta og ha omgang med; de er hennes nære slekt, det er skammelig ferd.
“‘Kada ka yi jima’i da mace da kuma’yarta. Kada ka yi jima’i da’yar ɗanta ko’yar’yarta; su danginta ne na kusa. Wannan mugun abu ne.
18 Du skal ikke ta din hustrus søster til ekte mens din hustru lever, så du vekker fiendskap mellem dem ved å ha omgang med dem begge.
“‘Kada ka auri’yar’uwar matarka ta zama kishiyar matarka ka kuma yi jima’i da ita yayinda matarka tana da rai.
19 En kvinne som er uren i sin månedlige svakhet, skal du ikke gå inn til og ha omgang med.
“‘Kada ka kusaci mace don ka yi jima’i da ita a lokacin ƙazantar al’adarta.
20 Din næstes hustru skal du ikke ha samleie med, sa du blir uren ved henne.
“‘Kada ka yi jima’i da matar maƙwabcinka ka ƙazantar da kanka tare da ita.
21 Du skal ikke gi noget av dine barn fra dig til ildoffer for Molok; du skal ikke vanhellige din Guds navn; jeg er Herren.
“‘Kada ku ba da wani daga cikin’ya’yanku don a yi hadaya wa Molek, gama ba za ku ƙasƙantar da sunan Allahnku ba. Ni ne Ubangiji.
22 Hos en mann skal du ikke ligge som en ligger hos en kvinne; det er en vederstyggelighet.
“‘Kada ka kwana da namiji kamar yadda namiji yakan kwana da ta mace, wannan abin ƙyama ne.
23 Du skal ikke ha omgang med noget dyr, for da blir du uren; heller ikke skal en kvinne la noget dyr ha omgang med sig; det er skamløs ferd.
“‘Kada ka yi jima’i da dabba ka ƙazantar da kanka. Mace ba za tă ba da kanta ga dabba don yă yi jima’i da ita ba; wannan abin ƙyama ne.
24 Gjør eder ikke urene med noget sådant! For alt dette gjorde de sig urene med de hedninger som jeg driver ut for eders øine,
“‘Kada ku ƙazantar da kanku da wani daga cikin waɗannan, domin haka al’umman da zan kora a gabanku suka ƙazantu.
25 og landet blev urent, og jeg hjemsøker det for dets misgjerning, så landet utspyr sine innbyggere.
Har ƙasar ma ta ƙazantu, saboda haka na hukunta ta saboda zunubinta, ƙasar kuwa ta amayar da mazaunanta.
26 Men I skal holde mine lover og mine bud og ikke gjøre nogen av disse vederstyggelige gjerninger, hverken den innfødte eller den fremmede som bor iblandt eder;
Amma dole ku kiyaye farillaina da kuma dokokina. Kada haifaffe ɗan ƙasa da baƙin da suke zama a cikinku yă yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama,
27 for alle disse vederstyggelige gjerninger har landets innbyggere gjort, de som var der før eder, og således blev landet urent.
gama mutanen da suka zauna a wannan ƙasa kafin ku sun aikata dukan waɗannan abubuwa, suka kuma ƙazantu.
28 Ellers kommer landet til å utspy eder, fordi I gjør det urent, likesom det utspyr det folk som har vært der før eder.
Kuma in kuka ƙazantar da ƙasar, za tă amayar da ku kamar yadda ta amayar da al’umman da suka riga ku.
29 For hver den som gjør nogen av alle disse vederstyggelige gjerninger, skal utryddes av sitt folk, hver og en som gjør sådant.
“‘Duk wanda ya yi wani daga cikin waɗannan abubuwa banƙyama, dole a fid da mutumin daga cikin mutanensa.
30 Så skal I da ta vare på det jeg vil ha varetatt, så I ikke gjør efter nogen av de vederstyggelige skikker som de har fulgt før eder, og ikke fører urenhet over eder ved dem; jeg er Herren eders Gud.
Ku kiyaye umarnaina kuma kada yi ku wata al’ada mai banƙyamar da aka yi kafin ku zo kuma kada ku ƙazantar da kanku da su. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”

< 3 Mosebok 18 >