< Josvas 4 >

1 Da nu hele folket var kommet vel over Jordan, sa Herren til Josva:
Da al’umma gaba ɗaya suka ƙetare Urdun, Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 Velg ut tolv menn av folket, én mann av hver stamme,
“Ka zaɓi mutum goma sha biyu daga cikin mutane, ɗaya daga kowace kabila,
3 og byd dem og si: Ta op her fra Jordans bunn tolv stener, fra det sted hvor prestenes føtter står, og hold dem ferdige, og bær dem med eder over og legg dem ned på det sted hvor I blir denne natt over!
ka ce musu kowa yă ɗauki dutse ɗaya daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, ku kai su, ku ajiye a inda za ku sauka yau.”
4 Da lot Josva de tolv menn kalle som han hadde valgt blandt Israels barn, én mann for hver stamme.
Sai Yoshuwa ya kira mutum goma sha biyu da ya zaɓa daga cikin Isra’ilawa, ɗaya daga kowace kabila
5 Og Josva sa til dem: Gå foran Herrens, eders Guds ark ut i Jordan og ta hver sin sten op på skulderen, efter tallet på Israels barns stammer!
ya ce musu, “Ku je tsakiyar Urdun inda akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku yake. Kowannenku yă ɗauki dutse ɗaya a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilan Isra’ila,
6 Disse stener skal være et tegn blandt eder. Når eders barn i fremtiden spør: Hvad er dette for stener?
yă zama muku alama. Nan gaba in yaranku suka tambaye ku suka ce, ‘Mece ce ma’anar kasancewar duwatsun nan a nan?’
7 da skal I si til dem: Jordans vann delte sig foran Herrens pakts-ark; da den drog ut i Jordan, delte Jordans vann sig, og disse stener skal være til et minne om dette for Israels barn til evig tid.
Sai ku ce musu, ruwan Urdun ya yanke a gaban akwatin alkawari na Ubangiji, a lokacin da akwatin alkawarin ya ƙetare Urdun. Waɗannan duwatsu za su zama abin tuni ga Isra’ilawa har abada.”
8 Israels barn gjorde som Josva bød, og tok tolv stener op av Jordan, således som Herren hadde sagt til Josva, efter tallet på Israels barns stammer, og de bar dem med sig over til det sted hvor de blev natten over, og la dem ned der.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Yoshuwa ya umarce su. Suka ɗauki duwatsu guda goma sha biyu bisa ga yawan kabilan Isra’ila, yadda Ubangiji ya gaya wa Yoshuwa; suka tafi da su masauƙinsu, a can suka ajiye su.
9 Og ute i Jordan, på det sted hvor de prester som bar paktens ark, stod med sine føtter, reiste Josva tolv stener op, og de står der den dag idag.
Yoshuwa ya ɗora duwatsu goma sha biyun a tsakiyar Urdun daidai inda firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya. Suna nan a can har wa yau.
10 Prestene som bar paktens ark, blev stående ute i Jordan, til det var skjedd alt det som Herren hadde befalt Josva å si til folket, efter alt det som Moses hadde befalt Josva. Og folket skyndte sig og gikk over.
Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Yoshuwa yă gaya wa mutane, kamar yadda Musa ya ce Yoshuwa yă yi. Mutanen suka wuce da sauri.
11 Og da hele folket var kommet vel over, drog Herrens ark og prestene frem foran folket.
Sai da dukan mutanen suka wuce sa’an nan akwatin alkawari da firistoci suka sha gaba.
12 Og Rubens barn og Gads barn og den halve Manasse stamme drog fullt rustet frem foran Israels barn, således som Moses hadde sagt til dem.
Mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse suka ƙetare da shirin yaƙi, suka wuce gaban Isra’ila kamar yadda Musa ya ce su yi.
13 Det var omkring firti tusen menn som væbnet til strid drog frem for Herrens åsyn til kamp på Jerikos ødemarker.
Wajen mutum dubu arba’in shirye domin yaƙi, suka wuce a gaban Ubangiji zuwa filayen Yeriko.
14 Den dag gjorde Herren Josva stor for hele Israels øine, og de fryktet ham, likesom de hadde fryktet Moses, alle hans livs dager.
A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Yoshuwa a gaban Isra’ilawa; suka kuma ba shi girma dukan kwanakin ransa, kamar yadda suka girmama Musa.
15 Og Herren sa til Josva:
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
16 Byd prestene som bærer vidnesbyrdets ark, at de skal stige op av Jordan!
“Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin Shaida su fito daga cikin Urdun.”
17 Og Josva bød prestene og sa: Stig op av Jordan!
Sai Yoshuwa ya umarci firistoci ya ce, “Ku fito daga cikin Urdun.”
18 Da nu prestene som bar Herrens pakts-ark, steg op av Jordan og hadde satt sine føtter på det tørre land, da vendte Jordans vann tilbake til sitt leie og gikk som før over alle sine bredder.
Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
19 Det var den tiende dag i den første måned at folket steg op av Jordan, og de leiret sig ved Gilgal, lengst mot øst i landet omkring Jeriko.
A rana ta goma ga wata na farko, mutane suka haura daga Urdun suka sauka a Gilgal a gabashin iyakar Yeriko.
20 Og der i Gilgal reiste Josva op de tolv stener som de hadde tatt op av Jordan.
Sai Yoshuwa ya kafa duwatsu goma sha biyun nan da suka ɗauko daga Urdun.
21 Og han sa til Israels barn: Når eders barn i fremtiden spør sine fedre: Hvad er dette for stener?
Ya ce wa Isra’ilawa, “Nan gaba in yaranku suka tambayi iyayensu suka ce, ‘Mece ce ma’anar waɗannan duwatsun?’
22 da skal I fortelle eders barn det og si: Israel gikk tørrskodd over Jordan her,
Ku ce musu, ‘Isra’ilawa sun ƙetare kogin Urdun a kan busasshiyar ƙasa.’
23 fordi Herren eders Gud lot Jordans vann tørke bort foran eder til I kom over, likesom Herren eders Gud gjorde med det Røde Hav, som han lot tørke bort foran oss til vi kom over,
Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya yanke a gabanku, har sai da kuka gama wucewa, kamar yadda ya yi a Jan Teku, a lokacin da ya busar da shi a gabanmu har sai da muka gama wucewa.
24 forat alle folk på jorden skal kjenne at Herrens hånd er sterk, og forat I alle dager skal frykte Herren eders Gud.
Ya yi wannan ne domin dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji mai iko ne, domin kuma ku zama masu tsoron Ubangiji Allahnku.”

< Josvas 4 >