< Johannes 9 >

1 Og da han gikk videre, så han en mann som var født blind.
Da Yesu yana wucewa, sai ya ga wani mutum makaho tun daga haihuwa.
2 Og hans disipler spurte ham: Rabbi! hvem er det som har syndet, han eller hans foreldre, siden han skulde fødes blind?
Sai almajiransa suka tambaye shi, “Mallam, wa yayi zunubi, mutumin ne ko iyayensa, har aka haife shi makaho?”
3 Jesus svarte: Hverken han har syndet eller hans foreldre, men det var forat Guds gjerninger skulde åpenbares på ham.
Yesu ya amsa, Ba mutumin ne ko iyayensa suka yi zunubi ba, amma domin aikin Allah ya bayyana a cikinsa.
4 Jeg må gjøre hans gjerninger som har sendt mig, så lenge det er dag; natten kommer da ingen kan arbeide.
Dole mu yi aikin wanda ya aiko ni tunda rana. Dare na zuwa inda ba mai iya yin aiki.
5 Mens jeg er i verden, er jeg verdens lys.
Yayinda ina duniya, ni ne hasken duniya.”
6 Da han hadde sagt dette, spyttet han på jorden og gjorde en deig av spyttet og smurte deigen på hans øine.
Bayan da Yesu ya fadi wadannan abubuwan, ya tofa yawu a kasa, ya kwaba kasar da yawunsa, sai ya shafe idanun mutumin da kasar.
7 og han sa til ham: Gå og vask dig i dammen Siloa, det er utlagt: utsendt. Han gikk da bort og vasket sig, og kom tilbake seende.
Ya ce masa, tafi, ka wanke a tafkin Siloam (ma'anarsa: aike).” Sai mutumin ya tafi, ya wanke, ya dawo yana gani.
8 Grannene og de som før hadde sett ham sitte og tigge, sa da: Er det ikke han som satt og tigget?
Sai makwabtansa da mutanen da da suka gan shi tun can yana roko suka ce, “Ba wannan mutum ne wanda ya ke zaune yana roko ba?”
9 Andre sa: Jo, det er han; andre sa: Nei, men han ligner ham. Han selv sa: Det er mig.
Wadansu suka ce, “shi ne.” Wadansu suka ce, “A'a, amma yana kama da shi.” Amma shi ya ce, “Ni ne wannan mutum.”
10 De sa da til ham: Hvorledes blev dine øine åpnet?
Suka ce masa, “To yaya aka bude maka idanu?”
11 Han svarte: Den mann som heter Jesus, gjorde en deig og smurte på mine øine og sa til mig: Gå til Siloa og vask dig! Da jeg så gikk bort og vasket mig, fikk jeg mitt syn.
Sai ya amsa, “Mutumin da ake ce da shi Yesu shi ya kwaba kasa ya shafa mani a idanuna ya ce mani, 'je ka kogin Siluwam ka wanke.' Sai naje na wanke, sannan na samu gani.”
12 De sa til ham: Hvor er han? Han sier: Jeg vet ikke.
Suka ce masa, “Ina yake?” Ya amsa, “Ban sani ba.”
13 Da fører de ham som hadde vært blind, frem for fariseerne.
Suka kawo mutumnin da yake makaho a da wurin farisawa.
14 Men det var sabbat den dag da Jesus gjorde deigen og åpnet hans øine.
A ranar asabar ne kwa Yesu ya kwaba kasa ya bude masa idanu.
15 Fariseerne spurte ham da likeså hvorledes han hadde fått sitt syn. Han sa til dem: Han la en deig på mine øine, og jeg vasket mig, og nu ser jeg.
Har yanzu farisawan suka tambaye shi yadda ya sami ganin gari. Ya ce masu, “Ya sa mani kasa a idanuna, na wanke, kuma yanzu ina gani.”
16 Nogen av fariseerne sa da: Denne mann er ikke fra Gud, siden han ikke holder sabbaten. Andre sa: Hvorledes kan en synder gjøre sådanne tegn? Og det var splid iblandt dem.
Wadansu daga cikin farisawa suka ce, “Wannan mutum ba daga Allah yake ba domin ba ya kiyaye ranar Asabar. “Wadansu suka ce, “Yaya mai zunubi zai yi irin wadannan alamu?” Sai rabuwa ta shiga tsakanin su.
17 Da sier de atter til den blinde: Hvad sier du om ham, siden det var dine øine han åpnet? Han sa: Han er en profet.
Sai suka tambayi makahon kuma, “Me kake cewa game da shi dashike ya bude maka idanu?” Makahon ya ce, “shi annabi ne.”
18 Jødene trodde da ikke om ham at han hadde vært blind og fått sitt syn, før de fikk kalt for sig foreldrene til ham som hadde fått sitt syn,
Har yanzu kam Yahudawan basu yarda da makantarsa ba da ganin gari da ya samu, sai da suka kirayo iyayen shi wanda ya sami ganin garin.
19 og de spurte dem: Er dette eders sønn som I sier er født blind? Hvorledes går det da til at han nu ser?
Su ka tambayi iyayen, “Wannan shine yaronku da kuka ce an haife shi makaho? Yaya yanzu ya ke iya gani?”
20 Hans foreldre svarte: Vi vet at dette er vår sønn, og at han er født blind;
Sai iyayen suka amsa masu, “Mun san wannan yaronmu ne kuma a makaho aka haife shi.
21 men hvorledes det er gått til at han nu ser, det vet vi ikke, eller hvem som har åpnet hans øine, det vet vi heller ikke; spør ham selv! han er gammel nok, han vil selv svare for sig.
Yadda ya ke gani yanzu, bamu sani ba, kuma wanda ya bude masa idanu, bamu sani ba. Ku tambaye shi, ba yaro ba ne. Zai iya magana don kansa.”
22 Dette sa hans foreldre fordi de fryktet for jødene; for jødene var allerede kommet overens om at dersom nogen bekjente ham å være Messias, skulde han utstøtes av synagogen;
Iyayensa sun fadi wadannan abubuwan, domin suna ji tsoron Yahudawan. Gama Yahudiyawan sun rigaya sun yarda duk wanda yace Yesu Almasihu ne, za a fitar dashi daga majami'a.
23 derfor sa hans foreldre: Han er gammel nok; spør ham selv!
Domin wannan ne, iyayensa suka ce, “Ai shi ba yaro ba ne, ku tambaye shi.”
24 De kalte da annen gang den mann for sig som hadde vært blind, og sa til ham: Gi Gud ære! Vi vet at dette menneske er en synder.
Suka sake kiran mutumin dake makaho karo na biyu, suka ce masa, “Ka girmama Allah. Mu kam mun sani wannan mutum mai zunubi ne.”
25 Han svarte da: Om han er en synder, vet jeg ikke; én ting vet jeg, at jeg som var blind, nu ser.
Sai wannan mutum ya amsa, “Ban sani ba ko shi mai zunubi ne. Abu guda daya na sani: da Ni makaho ne, amma yanzu ina gani.”
26 De sa da til ham: Hvad gjorde han med dig? hvorledes åpnet han dine øine?
Sai su ka ce masa, “Me ya yi maka? Ta yaya ya bude idanunka?”
27 Han svarte dem: Jeg har allerede sagt eder det, og I hørte ikke på det; hvorfor vil I atter høre det? Kanskje også I vil bli hans disipler?
Ya amsa, “Na rigaya na gaya maku, amma ba ku ji ba! Don me kuke so ku sake ji? Ko kuma kuna so ku zama almajiransa, haka ne?
28 Da skjelte de ham ut og sa: Du er hans disippel, men vi er Mose disipler.
Sai suka kwabe shi suka ce, “kai ne almajirinsa, amma mu almajiran Musa ne.
29 Vi vet at til Moses har Gud talt, men hvor denne er fra, vet vi ikke.
Mun sani Allah ya yi magana da Musa, amma wannan mutum, bamu san ko daga ina ne ya zo ba.”
30 Mannen svarte dem: Dette er da underlig at ikke I vet hvor han er fra, og han har dog åpnet mine øine.
Mutumin ya amsa masu ya ce, “Tirkashi, baku san inda ya fito ba, duk da haka shi ya bude mani idanu.
31 Vi vet at Gud hører ikke syndere, men den som er gudfryktig og gjør hans vilje, ham hører han.
Mun san da cewa Allah baya jin masu zunubi, amma idan wani mai ibada ne yana kuma yin nufinsa, to yana jin sa.
32 Så lenge verden har stått, er det uhørt at nogen har åpnet øinene på en blindfødt; (aiōn g165)
Tunda duniya ta fara ba a taba jin cewa wani ya bude idanun wanda aka haifa makaho ba. (aiōn g165)
33 var ikke denne mann fra Gud, da kunde han intet gjøre.
In mutumin nan ba daga Allah yake ba, ba zai iya yin komai ba.”
34 De svarte ham: Du er helt igjennem født i synder, og du vil lære oss? Og de kastet ham ut.
Suka amsa suka ce masa, “an haife ka cikin zunubai, yanzu kana so ka yi mana koyarwa?” Sai suka fitar da shi.
35 Jesus fikk høre at de hadde kastet ham ut, og da han traff ham, sa han: Tror du på Guds Sønn?
Yesu ya ji cewa sun fitar da shi daga majami'a. Da ya same shi sai ya ce masa, “Kana bada gaskiya ga Dan Allah?”
36 Han svarte: Hvem er han da, Herre, så jeg kan tro på ham?
Sai ya amsa masa yace, “Wanene shi, Ubangiji, da zan bada gaskiya gare shi?”
37 Jesus sa til ham: Du har sett ham; og han som her taler med dig, han er det.
Yesu yace masa, “Ai ka gan shi, shine wanda yake magana da kai.”
38 Han sa: Jeg tror, Herre! og falt ned for ham.
Mutumin ya ce, “Ubangiji, Na bada gaskiya.” Sai ya yi masa sujada.
39 Og Jesus sa: Til dom er jeg kommet til denne verden, forat de som ikke ser, skal se, og de som ser, skal bli blinde.
Yesu ya ce, “Don hukunci na zo wannan duniya domin wadanda ba su gani su gani, saboda kuma wadanda suke gani su zama makafi.”
40 Nogen av fariseerne, som var sammen med ham, hørte dette og sa til ham: Kanskje vi også er blinde?
Wadansu Farisawa wadanda suke tare da shi suka ji wadannan abubuwan, suka tambaye shi, “Muma makafi ne?”
41 Jesus sa til dem: Var I blinde, da hadde I ikke synd; men nu sier I: Vi ser; derfor blir eders synd.
Yesu ya ce masu, “Inda ku makafi ne, da ba ku da zunubi, amma yanzu kun ce, 'Muna gani', don haka zunubinku ya tabbata.

< Johannes 9 >