< Johannes 21 >

1 Siden åpenbarte Jesus sig atter for disiplene ved Tiberias-sjøen; og han åpenbarte sig på denne måte:
Daga baya Yesu ya sāke bayyana kansa ga almajiransa, a bakin Tekun Tibariya. Ga yadda ya faru.
2 Simon Peter og Tomas, det er tvilling, og Natanael fra Kana i Galilea og Sebedeus' sønner og to andre av hans disipler var sammen.
Siman Bitrus, Toma (wanda ake kira Didaimus), Natanayel daga Kana ta Galili,’ya’yan Zebedi maza, da kuma waɗansu almajirai guda biyu suna tare.
3 Simon Peter sier til dem: Jeg går avsted for å fiske. De sier til ham: Vi går også med dig. De gikk avsted og steg i båten; men den natt fikk de intet.
Sai Siman Bitrus ya ce musu, “Za ni kamun kifi,” suka ce, “Za mu tafi tare da kai.” Saboda haka suka fita suka shiga jirgin ruwa, amma a daren nan ba su kama kome ba.
4 Da det alt led mot morgenen, stod Jesus ved stranden; men disiplene visste ikke at det var Jesus.
Da sassafe, sai ga Yesu tsaye a gaci, amma almajiran ba su gane cewa Yesu ne ba.
5 Jesus sier da til dem: Barn! har I fisk? De svarte ham: Nei.
Sai ya ce musu, “Abokai, kuna da kifi kuwa?” Suka amsa suka ce, “A’a.”
6 Men han sa til dem: Kast garnet på den høire side av båten, så skal I få! De kastet det da ut, og nu var de ikke i stand til å dra det op, så meget fisk var der.
Ya ce musu, “Ku jefa abin kamun kifinku dama da jirgin ruwan, za ku samu.” Da suka yi haka, sai suka kāsa jawo abin kamun kifin saboda yawan kifi.
7 Den disippel som Jesus elsket, sier da til Peter: Det er Herren! Da nu Simon Peter hørte at det var Herren, bandt han sin kjortel om sig - for han var naken - og kastet sig i sjøen;
Sai almajirin da Yesu yake ƙauna ya ce wa Bitrus, “Ai, Ubangiji ne!” Nan da nan da Siman Bitrus ya ji ya ce, “Ai, Ubangiji ne,” sai ya yafa mayafinsa (don dā ma ya tuɓe shi), ya fāɗa cikin ruwan.
8 men de andre disipler kom med båten - de var ikke lang fra land, bare omkring to hundre alen - og drog garnet med fiskene efter sig.
Sauran almajiran kuwa suka bi shi cikin jirgin ruwan, janye da abin kamun kifin cike da kifi, don ba su da nisa daga gaci, wajen yadi ɗari ne.
9 Da de var steget i land, så de glødende kull ligge der, og på dem fisk og brød.
Da suka sauka, sai suka ga garwashin wuta a can da kifi a kai, da kuma’yan burodi.
10 Jesus sier til dem: Kom hit med noget av den fisk som I nu fikk!
Yesu ya ce musu, “Ku kawo waɗansu kifin da kuka kama yanzu.”
11 Simon Peter gikk ombord og drog garnet på land, fullt av store fisker, hundre og tre og femti, og enda det var så mange, gikk garnet ikke i sønder.
Sai Siman Bitrus ya hau ya jawo abin kamun kifin gaci. Ya cika da manyan kifi, 153, amma duk da yawansun nan abin kamun kifin bai tsintsinke ba.
12 Jesus sier til dem: Kom hit og hold måltid! Men ingen av disiplene vågde å spørre ham: Hvem er du? for de forstod at det var Herren.
Yesu ya ce musu, “Ku zo ku karya kumallo.” Ba wani daga cikin almajiran da ya yi karambanin tambayarsa, “Wane ne kai?” Sun san cewa Ubangiji ne.
13 Jesus kommer og tar brødet og gir dem, og likeså fisken.
Yesu ya zo, ya ɗauki burodin ya ba su, haka kuma kifin.
14 Dette var nu tredje gang Jesus åpenbarte sig for sine disipler efterat han var opstanden fra de døde.
Wannan fa shi ne sau na uku da Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa bayan an tashe shi daga matattu.
15 Da de nu hadde holdt måltid, sier Jesus til Simon Peter: Simon, Johannes' sønn! elsker du mig mere enn disse? Han sier til ham: Ja, Herre! du vet at jeg har dig kjær. Han sier til ham: Fø mine lam!
Da suka gama ci, sai Yesu ya ce wa Siman Bitrus, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske fiye da waɗannan?” Ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Ciyar da’ya’yan tumakina.”
16 Atter sier han til ham, annen gang: Simon, Johannes' sønn! elsker du mig? Han sier til ham: Ja, Herre! du vet at jeg har dig kjær. Han sier til ham: Vokt mine får!
Har wa yau Yesu ya ce, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata da gaske?” Ya amsa ya ce, “I, Ubangiji, ka san cewa ina sonka.” Yesu ya ce, “Lura da tumakina.”
17 Han sier tredje gang til ham: Simon, Johannes' sønn! har du mig kjær? Peter blev bedrøvet over at han tredje gang sa til ham: Har du mig kjær? Og han sier til ham: Herre! du vet alt, du vet at jeg har dig kjær. Jesus sier til ham: Fø mine får!
Sau na uku ya ce masa, “Siman ɗan Yohanna, kana ƙaunata?” Sai Bitrus ya ɓata rai saboda Yesu ya tambaye shi sau na uku, “Kana ƙaunata?” Ya ce, “Ubangiji ka san kome duka; ka san cewa, ina ƙaunarka.” Yesu ya ce, “Ciyar da tumakina.
18 Sannelig, sannelig sier jeg dig: Da du var yngre, bandt du selv op om dig og gikk dit du vilde; men når du er blitt gammel, skal du rekke ut dine hender, og en annen skal binde op om dig og føre dig dit du ikke vil.
Gaskiya nake faɗa maka, sa’ad da kake saurayi kakan yi wa kanka sutura ka tafi inda ka so; amma sa’ad da ka tsufa za ka miƙa hannuwanka, wani dabam yă yi maka sutura yă kai ka inda ba ka so.”
19 Dette sa han for å gi til kjenne med hvad slags død han skulde ære Gud. Og da han hadde sagt dette, sier han til ham: Følg mig!
Yesu ya faɗi wannan ne, don yă nuna irin mutuwar da Bitrus zai yi yă ɗaukaka Allah. Sa’an nan ya ce masa, “Bi ni!”
20 Da Peter vender sig, ser han den disippel følge med som Jesus elsket, og som lå op til hans bryst ved nattverden og sa: Herre! hvem er det som forråder dig?
Bitrus ya juya ya ga cewa almajirin nan da Yesu yake ƙauna yana binsu. (Wannan ne ya jingina a jikin Yesu sa’ad da suke cin abincin yamman nan da ya ce, “Ubangiji wane ne zai bashe ka?”)
21 Da nu Peter ser denne, sier han til Jesus: Herre! hvorledes skal det da gå denne?
Da Bitrus ya gan shi sai ya ce, “Ubangiji, wannan fa?”
22 Jesus sier til ham: Om jeg vil at han skal leve til jeg kommer, hvad kommer det dig ved? Følg du mig!
Yesu ya amsa ya ce, “Idan na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki? Kai dai bi ni.”
23 Derfor kom det ord ut blandt brødrene: Denne disippel dør ikke. Og dog sa Jesus ikke til ham at han ikke skulde dø, men: Om jeg vil at han skal leve til jeg kommer, hvad kommer det dig ved?
Saboda wannan, jita-jita ta bazu a cikin’yan’uwa cewa wannan almajirin ba zai mutu ba. Amma fa Yesu bai ce ba zai mutu ba; shi dai ya ce, “In na so yă kasance da rai har in dawo, mene ne naka a ciki?”
24 Dette er den disippel som vidner om dette og har skrevet dette; og vi vet at hans vidnesbyrd er sant.
Wannan shi ne almajirin da ya ba da shaida a kan waɗannan abubuwa ya kuma rubuta su. Mun san cewa shaidarsa gaskiya ce.
25 Men det er også meget annet som Jesus har gjort; skulde det skrives, hver ting for sig, da mener jeg at ikke hele verden vilde rumme de bøker som da måtte skrives.
Yesu ya yi waɗansu abubuwa da yawa kuma. Da a ce an rubuta kowannensu, na tabbata ko duniya duka ba za tă sami wuri saboda littattafan da za a rubuta ba.

< Johannes 21 >