< Johannes 1 >
1 I begynnelsen var Ordet, og Ordet var hos Gud, og Ordet var Gud.
Tun farar farawa akwai Kalma, Kalman kuwa yana nan tare da Allah, Kalman kuwa Allah ne.
2 Han var i begynnelsen hos Gud.
Yana nan tare da Allah tun farar farawa.
3 Alt er blitt til ved ham, og uten ham er ikke noget blitt til av alt som er blitt til.
Ta wurin Kalman ne aka halicci dukan abubuwa. In ba tare da shi ba, babu abin da aka yi wanda aka yi.
4 I ham var liv, og livet var menneskenes lys.
A cikinsa rai ya kasance, wannan rai kuwa shi ne hasken mutane.
5 Og lyset skinner i mørket, og mørket tok ikke imot det.
Hasken yana haskakawa cikin duhu, amma duhun bai rinjaye shi ba.
6 Det fremstod en mann, utsendt fra Gud; hans navn var Johannes;
Akwai wani mutumin da aka aiko daga Allah; mai suna Yohanna.
7 han kom til vidnesbyrd, for å vidne om lyset, forat alle skulde komme til troen ved ham.
Ya zo a matsayin mai shaida domin yă ba da shaida game da wannan haske, don ta wurinsa dukan mutane su ba da gaskiya.
8 Han var ikke lyset, men han skulde vidne om lyset.
Shi kansa ba shi ne hasken ba; sai dai ya zo a matsayin shaida ne kaɗai ga hasken.
9 Det sanne lys, som oplyser hvert menneske, var i ferd med å komme til verden.
Haske na gaskiya da yake ba da haske ga kowane mutum mai shigowa duniya.
10 Han var i verden, og verden er blitt til ved ham, og verden kjente ham ikke.
Yana a duniya, kuma ko da yake an yi duniya ta wurinsa ne, duniya ba tă gane shi ba.
11 Han kom til sitt eget, og hans egne tok ikke imot ham.
Ya zo wurin abin da yake nasa, amma nasa ɗin ba su karɓe shi ba.
12 Men alle dem som tok imot ham, dem gav han rett til å bli Guds barn, dem som tror på hans navn;
Duk da haka dukan waɗanda suka karɓe shi, ga waɗanda suka gaskata a sunansa, ya ba su iko su zama’ya’yan Allah
13 og de er født ikke av blod, heller ikke av kjøds vilje, heller ikke av manns vilje, men av Gud.
’ya’yan da aka haifa ba bisa hanyar’yan adam, ko shawarar mutum ko nufin namiji ba, sai dai haifaffu bisa ga nufin Allah.
14 Og Ordet blev kjød og tok bolig iblandt oss, og vi så hans herlighet - en herlighet som den en enbåren sønn har fra sin far - full av nåde og sannhet.
Kalman ya zama mutum, ya kuwa zauna a cikinmu. Muka ga ɗaukakarsa, ɗaukaka ta wanda yake Ɗaya kuma Makaɗaici, wanda ya zo daga wurin Uba, cike da alheri da gaskiya.
15 Johannes vidner om ham og roper: Det var denne om hvem jeg sa: Han som kommer efter mig, er kommet foran mig, fordi han var før mig.
(Yohanna ya ba da shaida game da shi. Ya ɗaga murya yana cewa, “Wannan shi ne wanda na ce, ‘Mai zuwa bayana ya fi ni girma domin yana nan kafin ni.’”)
16 For av hans fylde har vi alle fått, og det nåde over nåde;
Daga yalwar alherinsa dukanmu muka sami albarka bisa albarka.
17 for loven blev gitt ved Moses, nåden og sannheten kom ved Jesus Kristus.
Gama an ba da doka ta wurin Musa; alheri da gaskiya kuwa sun zo ne ta wurin Yesu Kiristi.
18 Ingen har nogensinne sett Gud; den enbårne Sønn, som er i Faderens skjød, han har forklaret ham.
Ba wanda ya taɓa ganin Allah, sai dai Allah da yake Ɗaya da kuma Makaɗaici wanda yake a gefen Uba, shi ne ya bayyana shi.
19 Og dette er Johannes' vidnesbyrd, da jødene sendte prester og levitter fra Jerusalem for å spørre ham: Hvem er du?
To, ga shaidar Yohanna sa’ad da Yahudawan Urushalima suka aiki firistoci da Lawiyawa su tambaye shi ko shi wane ne.
20 Da bekjente han og nektet ikke; han bekjente: Jeg er ikke Messias.
Bai yi mūsu ba, amma ya shaida a fili cewa, “Ba ni ne Kiristi ba.”
21 Og de spurte ham: Hvad da? Er du Elias? Han sa: Det er jeg ikke. Er du profeten? Og han svarte: Nei.
Sai suka tambaye shi suka ce, “To, wane ne kai? Kai ne Iliya?” Ya ce, “A’a, ni ba shi ba ne.” “Kai ne Annabin nan?” Ya amsa ya ce, “A’a.”
22 De sa da til ham: Hvem er du? så vi kan gi dem svar som har sendt oss; hvad sier du om dig selv?
A ƙarshe suka ce, “Wane ne kai? Ka ba mu amsa don mu mayar wa waɗanda suka aike mu. Me kake ce da kanka?”
23 Han sa: Jeg er en røst av en som roper i ørkenen: Gjør Herrens vei jevn, som profeten Esaias har sagt.
Yohanna ya amsa da kalmomin annabi Ishaya, “Ni murya ne mai kira a hamada, ‘Ku miƙe hanya domin Ubangiji.’”
24 Og de som var utsendt, var fariseere,
To, waɗansu Farisiyawan da aka aika
25 og de spurte ham: Hvorfor døper du da, når du ikke er Messias, og heller ikke Elias, og heller ikke profeten?
suka tambaye shi suka ce, “Don me kake yin baftisma in kai ba Kiristi ba ne, ba kuwa Iliya ba, ba kuma annabin nan ba?”
26 Johannes svarte dem: Jeg døper med vann; midt iblandt eder står den I ikke kjenner,
Yohanna ya amsa ya ce, “Ni dai ina baftisma da ruwa ne, amma a cikinku akwai wani tsaye da ba ku sani ba.
27 han som kommer efter mig, han hvis skorem jeg ikke er verdig til å løse.
Shi ne mai zuwa bayana, wanda ko igiyar takalmansa ma ban isa in kunce ba.”
28 Dette skjedde i Betania på hin side Jordan, hvor Johannes døpte.
Wannan duk ya faru ne a Betani a ƙetaren Urdun, inda Yohanna yake yin baftisma.
29 Dagen efter ser han Jesus komme til sig og sier: Se der Guds lam, som bærer verdens synd!
Kashegari Yohanna ya ga Yesu yana zuwa wajensa sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah mai ɗauke zunubin duniya!
30 Det er ham om hvem jeg sa: Efter mig kommer en mann som er kommet foran mig, fordi han var før mig.
Wannan shi ne wanda nake nufi sa’ad da na ce, ‘Mutum mai zuwa bayana ya fi ni girma, domin yana nan kafin ni.’
31 Og jeg kjente ham ikke; men forat han skulde åpenbares for Israel, derfor er jeg kommet og døper med vann.
Ko ni ma dā ban san shi ba, sai dai abin da ya sa na zo ina baftisma da ruwa shi ne domin a bayyana shi ga Isra’ila.”
32 Og Johannes vidnet og sa: Jeg har sett Ånden komme ned som en due fra himmelen, og han blev over ham.
Sai Yohanna ya ba da wannan shaida, “Na ga Ruhu ya sauko kamar kurciya daga sama ya zauna a kansa.
33 Og jeg kjente ham ikke; men han som sendte mig for å døpe med vann, han sa til mig: Den du ser Ånden komme ned og bli over, han er den som døper med den Hellige Ånd;
Dā ban san shi ba, sai dai wanda ya aiko ni in yi baftisma da ruwa ya gaya mini cewa, ‘Mutumin da ka ga Ruhu ya sauko ya kuma zauna a kansa shi ne wanda zai yi baftisma da Ruhu Mai Tsarki.’
34 og jeg har sett det, og jeg har vidnet at han er Guds Sønn.
Na gani na kuma shaida cewa wannan Ɗan Allah ne.”
35 Dagen efter stod atter Johannes og to av hans disipler der,
Kashegari kuma Yohanna yana can tare da biyu daga cikin almajiransa.
36 og han så Jesus som kom gående, og sa: Se der Guds lam!
Da ya ga Yesu yana wucewa, sai ya ce, “Ku ga, ga Ɗan Rago na Allah!”
37 Og de to disipler hørte hans ord, og de fulgte efter Jesus.
Da almajiran nan biyu suka ji ya faɗi haka, sai suka bi Yesu.
38 Da vendte Jesus sig om, og da han så de fulgte efter ham, sa han til dem: Hvad søker I? De sa til ham: Rabbi! det er utlagt: mester! hvor har du ditt herberge?
Da juyewa, sai Yesu ya ga suna bin sa, sai ya tambaye, su ya ce, “Me kuke nema?” Suka ce, “Rabbi” (wato, “Malam”), “ina kake da zama?”
39 Han sa til dem: Kom og se! Da kom de og så hvor han hadde sitt herberge, og de blev hos ham den dag; det var omkring den tiende time.
Ya amsa musu ya ce, “Ku zo, za ku kuma gani.” Saboda haka suka je suka ga inda yake da zama, suka kuma zauna a can tare da shi. Wajen sa’a ta goma ce kuwa.
40 En av de to som hørte hint ord av Johannes og fulgte efter ham, var Andreas, Simon Peters bror;
Andarawus ɗan’uwan Siman Bitrus, yana ɗaya daga cikin biyun nan da suka bi Yesu bayan da suka ji maganar Yohanna a kan Yesu.
41 han finner først sin bror Simon, og sier til ham: Vi har funnet Messias, det er utlagt: Kristus.
Abu na fari da Andarawus ya yi shi ne ya sami ɗan’uwansa Siman ya gaya masa cewa, “Mun sami Almasihu” (wato, Kiristi).
42 Og han førte ham til Jesus. Jesus så på ham og sa: Du er Simon, Johannes' sønn; du skal hete Kefas, det er utlagt: Peter.
Ya kuma kawo shi wurin Yesu. Yesu ya dube shi ya ce, “Kai ne Siman ɗan Yohanna. Za a ce da kai Kefas” (in an fassara, Bitrus ke nan).
43 Dagen efter vilde han dra derfra til Galilea, og han traff Filip. Og Jesus sa til ham: Følg mig!
Kashegari Yesu ya yanke shawara yă tafi Galili. Da ya sami Filibus sai ya ce masa, “Bi ni.”
44 Men Filip var fra Betsaida, Andreas' og Peters by.
Filibus, kamar Andarawus da Bitrus shi ma daga garin Betsaida ne.
45 Filip traff Natanael, og sa til ham: Ham som Moses har skrevet om i loven, og likeså profetene, ham har vi funnet: Jesus, Josefs sønn, fra Nasaret!
Filibus ya sami Natanayel ya kuma gaya masa, “Mun sami wanda Musa ya rubuta game da shi a cikin Doka, kuma wanda annabawa suka rubuta a kansa, Yesu Banazare, ɗan Yusuf.”
46 Og Natanael sa til ham: Kan det komme noget godt fra Nasaret? Filip sa til ham: Kom og se!
Natanayel ya ce, “A Nazaret! Wani abin kirki zai iya fito daga can?” Filibus ya ce, “Zo ka gani.”
47 Jesus så Natanael komme bortimot sig, og sa om ham: Se, det er en ekte israelitt, som det ikke er svik i.
Da Yesu ya ga Natanayel yana zuwa, sai ya yi magana game da shi cewa, “Ga mutumin Isra’ila na gaske wanda ba shi da ha’inci.”
48 Natanael sa til ham: Hvor kjenner du mig fra? Jesus svarte og sa til ham: Før Filip kalte på dig, mens du var under fikentreet, så jeg dig.
Natanayel ya yi tambaya ya ce, “A ina ka san ni?” Yesu ya amsa ya ce, “Na gan ka yayinda kake a gindin itacen ɓaure, kafin Filibus yă kira ka.”
49 Natanael svarte ham: Rabbi! du er Guds Sønn, du er Israels konge!
Sai Natanayel ya ce, “Rabbi, kai Ɗan Allah ne. Kai ne Sarkin Isra’ila.”
50 Jesus svarte og sa til ham: Fordi jeg sa dig at jeg så dig under fikentreet, derfor tror du? Du skal få se det som er større enn dette.
Yesu ya ce, “Ka gaskata domin na ce maka na gan ka a gindin itacen ɓaure. Za ka ga abubuwan da suka fi haka.”
51 Og han sa til ham: Sannelig, sannelig sier jeg eder: I skal se himmelen åpnet og Guds engler stige op og stige ned over Menneskesønnen.
Sai ya ƙara da cewa, “Gaskiya nake gaya muku, za ku ga sama a buɗe, mala’ikun Allah kuma suna hawa suna kuma sauka a kan Ɗan Mutum.”