< Jobs 9 >
1 Da tok Job til orde og sa:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Ja visst, jeg vet at det er så; hvorledes skulde en mann kunne ha rett mot Gud?
“Lalle, na san wannan gaskiya ne. Amma ta yaya mutum zai iya zama mai adalci a gaban Allah?
3 Om han hadde lyst til å gå i rette med Gud, kunde han ikke svare ham ett til tusen.
Ko da mutum yana so yă yi gardama da shi, ba zai taɓa amsa masa ba ko da sau ɗaya cikin dubu.
4 Vis som han er av hjerte og veldig i styrke - hvem trosset ham og kom vel fra det,
Hikimarsa tana da zurfi, ikonsa yana da yawa. Wane ne ya taɓa yin faɗa da shi har ya yi nasara?
5 han som flytter fjell før de vet av det, som velter dem i sin vrede,
Yana matsar da manyan duwatsu kafin su sani kuma yana juya su cikin fushinsa.
6 som ryster jorden, så den viker fra sitt sted, og dens støtter bever,
Yana girgiza ƙasa, yana girgiza harsashenta.
7 som byder solen, så den ikke går op, og som setter segl for stjernene,
Yana magana da rana sai ta ƙi yin haske; yana hana taurari yin haske.
8 som alene utspenner himmelen og skrider frem over havets høider,
Shi kaɗai ya shimfiɗa sammai ya kuma yi tafiya a kan raƙuman ruwan teku.
9 som har skapt Bjørnen, Orion og Syvstjernen og Sydens stjernekammere,
Shi ne ya halicci Mafarauci da Kare da Zomo, da Kaza, da’Ya’yanta da tarin taurari a sama, da taurarin kudu.
10 som gjør store, uransakelige ting og under uten tall?
Yana yin abubuwan banmamaki waɗanda ba a iya ganewa, mu’ujizai waɗanda ba a iya ƙirgawa.
11 Han går forbi mig, og jeg ser ham ikke; han farer forbi, og jeg merker ham ikke.
Ba na iya ganinsa lokacin da ya wuce ni; ba na sani ya wuce lokacin da ya wuce.
12 Han griper sitt rov - hvem vil hindre ham, hvem vil si til ham: Hvad gjør du?
Wane ne ya isa yă hana shi in ya ƙwace abu? Wa zai ce masa, ‘Me kake yi?’
13 Gud holder ikke sin vrede tilbake; under ham måtte Rahabs hjelpere bøie sig.
Allah ba ya danne fushinsa; ko dodannin ruwan da ake kira ayarin Rahab ya tattake su.
14 Hvorledes skulde da jeg kunne svare ham og velge mine ord imot ham,
“Ta yaya zan iya yin faɗa da shi? Ina zan iya samun kalmomin da zan yi gardama da shi?
15 jeg som ikke kunde svare om jeg enn hadde rett, men måtte be min dommer om nåde!
Ko da yake ba ni da laifi, ba zan iya amsa masa ba; sai dai roƙon jinƙai zan iya yi ga mahukuncina.
16 Om jeg ropte, og han svarte mig, kunde jeg ikke tro at han hørte min røst,
Ko da na yi kira gare shi ya amsa mini, ban yarda cewa zai saurare ni ba.
17 han som vilde knuse mig i storm og uten årsak ramme mig med sår på sår,
Zai sa hadari yă danne ni yă ƙara mini ciwona ba dalili.
18 som ikke vilde tillate mig å dra ånde, men vilde mette mig med lidelser.
Ba zai bari in yi numfashi ba, sai dai yă ƙara mini azaba.
19 Gjelder det styrke, så sier han: Se, her er jeg! Gjelder det rett: Hvem vil stevne mig?
In maganar ƙarfi ne, shi babban mai ƙarfi ne! In kuma maganar shari’a ne, wa zai kai kararsa?
20 Hadde jeg enn rett, skulde dog min egen munn dømme mig skyldig; var jeg enn uskyldig, vilde han dog si at jeg hadde urett.
Ko da ni marar ƙarfi ne, bakina ya isa yă sa in zama mai laifi; in ba ni da laifi, zai sa in yi laifi.
21 Skyldløs er jeg; jeg bryr mig ikke om å leve - jeg forakter mitt liv.
“Ko da yake ba ni da laifi, ban damu da kaina ba; na rena raina.
22 Det kommer ut på ett; derfor sier jeg: Skyldløs eller ugudelig - han gjør dem begge til intet.
Ba bambanci; shi ya sa na ce, ‘Yana hallaka marasa laifi da kuma mugaye.’
23 Når svepen brått rammer med død, spotter han de uskyldiges lidelse.
Lokacin da bala’i ya kawo ga mutuwa, yakan yi dariyar baƙin cikin marasa laifi.
24 Jorden er gitt i den ugudeliges hånd; han tilhyller dens dommeres åsyn. Er det ikke han som gjør det, hvem er det da?
Lokacin da ƙasa ta faɗa a hannun mugaye, yakan rufe idanun masu shari’a. In ba shi ba wa zai yi wannan?
25 Mine dager har vært hastigere enn en løper; de er bortflyktet uten å ha sett noget godt;
“Kwanakina sun fi mai gudu wucewa da sauri; suna firiya babu wani abin jin daɗi a cikinsu.
26 de har faret avsted som båter av rør, som en ørn som slår ned på sitt bytte.
Suna wucewa kamar jirgin ruwan da aka yi da kyauro, kamar jahurma da ta kai wa namanta cafka.
27 Om jeg sier: Jeg vil glemme min sorg, jeg vil la min mørke mine fare og se glad ut,
‘In na ce zan manta da abin da yake damu na, zan yi murmushi in daina nuna ɓacin rai,’
28 da gruer jeg for alle mine plager; jeg vet jo at du ikke frikjenner mig.
duk da haka ina tsoron duk wahalata, domin na san ba za ka ɗauke ni marar laifi ba.
29 Jeg skal jo være ugudelig - hvorfor gjør jeg mig da forgjeves møie?
Tun da an riga an ɗauke ni mai laifi, duk ƙoƙarina a banza yake.
30 Om jeg tvettet mig med sne og renset mine hender med lut,
Ko da na wanke jikina duka da sabulu, na wanke hannuwana kuma da soda,
31 da skulde du dyppe mig i en grøft, så mine klær vemmedes ved mig.
duk da haka za ka jefa ni cikin ƙazamin wuri, yadda ko rigunan jikina ma za su ƙi ni.
32 For han er ikke en mann som jeg, så jeg kunde svare ham, så vi kunde gå sammen for retten;
“Shi ba mutum ba ne kamar ni wanda zan iya amsa masa, har da za mu yi faɗa da juna a wurin shari’a.
33 det er ikke nogen voldgiftsmann mellem oss, som kunde legge sin hånd på oss begge.
In da akwai wanda zai iya shiga tsakaninmu, ya ɗora hannunsa a kanmu tare,
34 Når han bare tok sitt ris bort fra mig, og hans redsler ikke skremte mig!
wani wanda zai sa Allah yă daina duka na, don yă daina ba ni tsoro.
35 Da skulde jeg tale uten å reddes for ham; for slik er jeg ikke, det vet jeg med mig selv.
Sa’an nan ne zan iya yin magana ba tare da jin tsoronsa ba, amma a yadda nake a yanzu ba zan iya ba.