< Jobs 3 >

1 Derefter oplot Job sin munn og forbannet den dag han blev født.
Bayan wannan Ayuba ya buɗe baki ya la’anta ranar da aka haife shi.
2 Job tok til orde og sa:
Ayuba ya ce,
3 Til grunne gå den dag da jeg blev født, og den natt som sa: Et guttebarn er undfanget!
“A hallaka ranar da aka haife ni, da kuma daren da aka ce, ‘An haifi jariri namiji!’
4 Måtte den dag bli til mørke! Måtte Gud i det høie ikke spørre efter den, og intet lys stråle over den!
Bari ranan nan ta zama duhu; kada Allah yă kula da ita; kada rana tă yi haske a wannan rana.
5 Gid mørke og dødsskygge må kreve den tilbake, gid skyer må leire sig over den, gid alt som gjør en dag mørk, må skremme den!
Bari duhu da inuwa mai duhu ta sāke rufe ta; gizagizai kuma su rufe ta; duhu kuma ya rufe haskenta.
6 Den natt - måtte mulm ta den! Den glede sig ikke blandt årets dager, den komme ikke med i måneders tall!
Bari duhu mai yawa yă rufe daren nan; kada a haɗa ta cikin kwanakin shekara, ko kuma cikin kwanakin watanni.
7 Ja, ufruktbar bli den natt! Aldri lyde det jubel i den!
Bari daren yă zama marar amfani; kada a ji wata sowa ta farin ciki.
8 Måtte de som forbanner dager, ønske ondt over den, de som er kyndige i å mane frem Leviatan!
Bari waɗanda suke la’anta ranaku su la’anta wannan rana su waɗanda suke umartar dodon ruwa.
9 Gid dens demrings stjerner må bli mørke! La den vente på lys, uten at det kommer! Måtte den aldri skue morgenrødens øielokk -
Bari taurarinta na safe su zama duhu; bari ranar tă yi ta jiran ganin haske amma kada tă gani,
10 fordi den ikke stengte døren til min mors liv og skjulte møie for mine øine.
gama ba tă hana uwata ɗaukar cikina, don ta hana ni shan wahalan nan ba.
11 Hvorfor døde jeg ikke i mors liv? Hvorfor utåndet jeg ikke straks i fødselsstunden?
“Me ya sa ban mutu ba da za a haife ni, ko kuma in mutu sa’ad da ana haihuwata ba?
12 Hvorfor tok knær imot mig, og hvorfor bryster som jeg kunde die?
Me ya sa aka haife ni, aka tanada nono na sha na rayu?
13 For da kunde jeg nu ligge og hvile; jeg kunde sove og hadde da ro -
Da yanzu ina kwance cikin salama; da ina barcina cikin salama
14 sammen med konger og jordens styrere, som bygget sig ruiner,
tare da sarakuna da mashawarta a cikin ƙasa, waɗanda suka gina wa kansu wuraren da yanzu duk sun rushe,
15 eller med fyrster som eide gull, som fylte sine hus med sølv;
da shugabanni waɗanda suke da zinariya, waɗanda suka cika gidajensu da azurfa.
16 eller jeg var nu ikke til, likesom et nedgravd, ufullbåret foster, lik barn som aldri så lyset.
Ko kuma don me ba a ɓoye ni a cikin ƙasa kamar jaririn da aka haifa ba rai ba, kamar jaririn da bai taɓa ganin hasken rana ba.
17 Der har de ugudelige holdt op å rase, og der hviler de trette.
A wurin mugaye za su daina yin mugunta, gajiyayyu kuma za su huta.
18 Der har alle fanger ro, de hører ikke driverens røst.
Waɗanda aka daure za su sami jin daɗin; an sake su ba za su sāke jin ana tsawata masu ba.
19 Liten og stor er der like, og trælen er fri for sin herre.
Manyan da ƙanana suna a can, bawa kuma ya sami’yanci daga wurin maigidansa.
20 Hvorfor gir han den lidende lys, og liv til dem som bærer sorg i sitt hjerte,
“Don me ake ba da haske ga waɗanda suke cikin ƙunci, rai kuma ga masu ɗacin rai
21 dem som venter på døden uten at den kommer, og som leter efter den ivrigere enn efter skjulte skatter,
ga waɗanda suke neman mutuwa amma ba su samu ba, waɗanda suke nemanta kamar wani abu mai daraja a ɓoye,
22 dem som gleder sig like til jubel, som fryder sig når de finner en grav -
waɗanda suke farin ciki sa’ad da suka kai kabari?
23 til den mann hvis vei er skjult for ham, og som Gud har stengt for på alle kanter?
Don me aka ba mutum rai, mutumin da bai san wani abu game da kansa ba, mutumin da Allah ya kange shi.
24 For mine sukk er blitt mitt daglige brød, og mine klager strømmer som vannet.
Baƙin ciki ya ishe ni maimakon abinci; ina ta yin nishi ba fasawa;
25 For alt det fryktelige jeg reddes for, det rammer mig, og det jeg gruer for, det kommer over mig.
Abin da nake tsoro ya faru da ni; abin da ba na so ya same ni.
26 Jeg har ikke fred, ikke ro, ikke hvile - det kommer alltid ny uro.
Ba ni da salama, ba natsuwa; ba ni da hutu, sai wahala kawai.”

< Jobs 3 >