< Jobs 26 >

1 Da tok Job til orde og sa:
Sai Ayuba ya amsa,
2 Hvor du har hjulpet den avmektige, støttet den kraftløse arm!
“Yadda ka taimaki marar ƙarfi! Yadda ka ceci marar ƙarfi!
3 Hvor du har gitt den uvise råd, og hvilket overmål av visdom du har lagt for dagen!
Ka ba marar hikima shawara! Ka nuna kana da ilimi sosai.
4 Hvem har du fremført dine ord for, og hvis ånd har talt gjennem dig?
Wane ne ya taimake ka ka yi waɗannan maganganu? Kuma ruhun wane ne ya yi magana ta bakinka?
5 Dødsrikets skygger skjelver, vannenes dyp og de som bor i dem.
“Matattu suna cikin azaba, waɗanda suke ƙarƙashin ruwaye da dukan mazauna cikin ruwaye.
6 Dødsriket ligger åpent for ham og avgrunnen uten dekke. (Sheol h7585)
Mutuwa tsirara take a gaban Allah; haka kuma hallaka take a buɗe. (Sheol h7585)
7 Han breder Norden ut over det øde rum, han henger jorden på intet.
Ya shimfiɗa arewancin sararin sama a sarari; ya rataye duniya ba a jikin wani abu ba.
8 Han binder vannene sammen i sine skyer, og skyene brister ikke under dem.
Ya naɗe ruwaye a cikin gizagizansa, duk da haka girgijen bai yage saboda nauyi ba.
9 Han lukker for sin trone, breder sine skyer over den.
Ya rufe fuskar wata, ya shimfiɗa gizagizai a kan shi,
10 En grense har han dradd i en ring over vannene, der hvor lyset grenser til mørket.
ya zāna iyakar fuskar ruwa a kan iyakar da take tsakanin duhu da haske.
11 Himmelens støtter skjelver, og de forferdes for hans trusel.
Madogaran sama sun girgiza, saboda tsawatawarsa.
12 Ved sin kraft oprører han havet, og ved sin forstand knuser han Rahab.
Da ikonsa ya kwantar da teku; da hikimarsa ya hallaka dodon ruwan nan Rahab.
13 Ved hans ånde blir himmelen klar; hans hånd gjennemborer den lettfarende drage.
Da numfashinsa ya sa sararin sama ya yi kyau da hannunsa ya soke macijin nan mai gudu.
14 Se, dette er bare utkantene av hans verk; hvor svak er lyden av det ord vi hører! Men hans veldes torden - hvem forstår den?
Waɗannan kaɗan ke nan daga cikin ayyukansa masu yawa. Kaɗan kawai muke ji game da shi! Wane ne kuwa yake iya gane tsawar ikonsa?”

< Jobs 26 >