< Esaias 22 >

1 Utsagn om Syne-dalen. Hvad fattes dig siden alt ditt folk er steget op på takene?
Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
2 Du larmfulle, du brusende stad, du jublende by! Dine drepte er ikke drept med sverd og ikke død i krig.
Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
3 Dine høvdinger har alle sammen flyktet bort, uten bue er de fanget; alle som fantes i dig, er fanget, enda de hadde flyktet langt bort.
Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
4 Derfor sier jeg: Se bort fra mig! Jeg må gråte bittert. Treng ikke inn på mig for å trøste mig over mitt folks undergang!
Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
5 For en dag med forferdelse og nedtramping og forvirring holder Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud, i Syne-dalen; murer brytes ned, og skrik lyder op imot fjellet.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
6 Elam bærer kogger, drar frem med stridsmenn på vogner og med ryttere, og Kir har tatt dekket av sitt skjold.
Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
7 Dine herligste daler fylles med vogner, og rytterne stiller sig op imot portene.
Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
8 Så tar Herren dekket bort fra Juda, og du ser dig på den dag om efter rustningene i skoghuset,
An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
9 og I ser at Davids stad har mange revner, og I samler vannet i den nedre dam,
kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
10 og I teller Jerusalems hus, og I river husene ned for å styrke muren,
Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
11 og I gjør en grav mellem begge murene for vannet fra den gamle dam; men I ser ikke op til ham som gjorde dette, og ham som uttenkte det for lang tid siden, ser I ikke.
Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
12 Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud, kaller eder den dag til gråt og veklage og til å rake hodet og binde sekk om eder.
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
13 Men se, der er fryd og glede; de slakter okser, de slakter får, de eter kjøtt og drikker vin; de sier: La oss ete og drikke, for imorgen dør vi!
Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
14 Men i mine ører lyder Herrens, hærskarenes Guds åpenbaring: Sannelig, denne misgjerning skal I ikke få utsonet så lenge I lever, sier Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud.
Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
15 Så sier Herren, Israels Gud, hærskarenes Gud: Gå inn til denne overhovmester Sebna, han som står for huset, og si:
Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
16 Hvad har du her, og hvem har du her, siden du her har hugget dig ut en grav, du som hugger dig ut en grav i høiden, huler dig ut en bolig i berget?
Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
17 Se, Herren skal slynge dig, ja slynge dig bort, mann! Han skal rulle dig sammen,
“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
18 han skal nøste dig til et nøste og kaste dig som en ball bort til et vidtstrakt land; dit skal du, og der skal du dø, og dit skal dine herlige vogner, du skamflekk for din herres hus!
Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
19 Jeg vil støte dig bort fra din post, og fra din plass skal du bli kastet ned.
Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
20 Og på den dag vil jeg kalle min tjener Eljakim, Hilkias' sønn,
“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
21 og jeg vil klæ ham i din kjortel og binde ditt belte om ham og gi din makt i hans hånd, og han skal være en far for Jerusalems innbyggere og for Judas hus.
Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
22 Og jeg vil legge nøklen til Davids hus på hans skulder, og han skal lukke op, og ingen lukke til, og lukke til, og ingen lukke op.
Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
23 Og jeg vil feste ham som en nagle på et sikkert sted, og han skal bli et æressete for sin fars hus.
Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
24 Og de skal henge på ham hele tyngden av hans fars hus, de edle og de ville skudd, alle småkarene, både fatene og alle krukkene.
Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
25 På den dag, sier Herren, hærskarenes Gud, skal den nagle som var festet på et sikkert sted, løsne; den skal hugges av og falle ned, og den byrde som hang på den, skal ødelegges; for Herren har talt.
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.

< Esaias 22 >