< Esaias 12 >
1 På den tid skal du si: Jeg takker dig, Herre; for du var vred på mig, men din vrede hørte op, og du trøstet mig.
A wannan rana za ku ce, “Zan yabe ka, ya Ubangiji. Ko da yake a dā ka yi fushi da ni, amma yanzu ka daina fushi da ni ka kuwa ta’azantar da ni.
2 Se, Gud er min frelse, jeg er trygg og frykter ikke; for Herren, Israels Gud, er min styrke og lovsang, og han blev mig til frelse.
Tabbatacce Allah shi ne mai cetona; zan dogara gare shi ba kuwa zan ji tsoro ba. Ubangiji, Ubangiji, ne ƙarfina da waƙata; ya zama mai cetona.”
3 Og I skal øse vann med glede av frelsens kilder.
Da farin ciki zan ɗebo ruwa daga rijiyoyin ceto.
4 Og I skal si på den tid: Takk Herren, påkall hans navn, kunngjør hans gjerninger blandt folkene, forkynn at hans navn er ophøiet!
A wannan rana za ku ce, “Yi godiya ga Ubangiji, ku kira bisa sunansa; a sanar da wannan abin da ya aikata a cikin al’ummai, a kuma yi shela cewa sunansa mai girma ne.
5 Syng Herrens pris, for herlige ting har han gjort! La dette bli kunngjort over hele jorden!
Ku rera ga Ubangiji, gama ya aikata manyan abubuwa; bari a sanar da wannan ga dukan duniya.
6 Rop høit og juble, I Sions innbyggere! Stor er Israels Hellige midt iblandt eder!
Ku tā da murya ku kuma rera don farin ciki, ya ku mutanen Sihiyona, gama Mai Tsarki na Isra’ila da girma yake a cikinku.”