< Hoseas 12 >

1 Efra'im higer efter vind, han jager efter østenvær; hele dagen dynger han op løgn og ødeleggelse; de inngår pakt med Assur, de fører olje til Egypten.
Efraim yana kiwo a kan iska; yana fafarar iskar gabas dukan yini yana riɓaɓɓanya ƙarairayi da rikici. Ya yi yarjejjeniya da Assuriya ya kuma aika wa Masar man zaitun.
2 Herren har trette med Juda, og han skal hjemsøke Jakob for hans ferds skyld, betale ham efter hans gjerninger.
Ubangiji yana da ƙarar da zai kawo a kan Yahuda; zai hukunta Yaƙub bisa ga hanyoyinsa zai sāka masa bisa ga ayyukansa.
3 I mors liv holdt han sin bror i hælen, og i sin manndomskraft kjempet han med Gud.
A cikin mahaifa ya cafke ɗiɗɗigen ɗan’uwansa; a matsayin mutum ya yi kokawa da Allah.
4 Han kjempet med engelen og vant; han gråt og bad ham om nåde; i Betel møtte han ham, og der talte han med oss.
Ya yi kokawa da mala’ika ya kuma rinjaye shi; ya yi kuka ya kuma yi roƙo don tagomashi. Ya same shi a Betel ya kuma yi magana da shi a can,
5 Og Herren, hærskarenes Gud - Herren er det navn han skal kalles med.
Ubangiji Allah Maɗaukaki, Ubangiji ne sunansa sananne!
6 Og du - til din Gud skal du vende om; hold fast ved miskunnhet og rett, og bi stadig på din Gud!
Amma dole ku koma ga Allahnku; ku ci gaba da ƙauna da yin gaskiya, ku kuma saurari Allahnku kullum.
7 I Kana'ans hånd er det falsk vekt; å gjøre urett er hans lyst.
Ɗan kasuwa yana amfani da mudu marar gaskiya; yana jin daɗin cuta.
8 Og Efra'im sier: Ja, jeg er blitt rik, har vunnet mig gods; men i alt mitt strev skal ingen kunne finne nogen urett - nogen synd.
Efraim yana fariya yana cewa, “Ni mai arziki ne ƙwarai; na azurta. Da dukan wadatata ba za a sami wani laifi ko zunubi a gare ni ba.”
9 Men jeg er Herren din Gud fra Egyptens land; jeg vil ennu la dig bo i telt likesom i høitidsdagene.
“Ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya fitar da ku daga Masar; zan sa ku sāke zauna a tentuna, kamar a kwanakin ƙayyadaddun bukukkuwanku.
10 Jeg har talt til profetene, og jeg har latt dem se syner i mengde, og gjennem profetene har jeg talt i lignelser.
Na yi magana da annabawa, na ba su wahayi da yawa na kuma ba da misalai ta wurinsu.”
11 Er Gilead fullt av misgjerninger, så skal de også bli rent til intet; har de ofret okser i Gilgal, så skal og deres altere bli som stenrøser langsmed markens furer.
Gileyad mugu ne? Mutanensa mutanen banza ne! Suna miƙa bijimai a Gilgal? Bagadansu za su zama tsibin duwatsu. A gonar da aka nome.
12 Jakob flyktet til Arams land, Israel tjente for å vinne en hustru - for å vinne en hustru voktet han får.
Yaƙub ya gudu zuwa ƙasar Aram; Isra’ila ya yi bauta don yă sami mata, domin kuma yă biya, sai da ya yi kiwon tumaki.
13 Men ved en profet førte Herren Israel op fra Egypten, og ved en profet voktet han det.
Ubangiji ya yi amfani da annabi don yă fitar da Isra’ila daga Masar ta wurin annabi ya lura da shi.
14 Efra'im har vakt bitter harme; derfor skal hans Herre la hans blodskyld komme over ham, og hans hån skal han gjengjelde ham.
Amma Efraim ya yi muguwar tsokana da ta sa ya yi fushi; shugabansa zai ɗora musu hakkin jini a kansa kuma zai sāka masa saboda wulaƙancinsa.

< Hoseas 12 >