< Hoseas 10 >
1 Israel er et frodig vintre, som bærer frukt; jo mere frukt han fikk, desto flere alter bygget han; jo bedre det gikk hans land, desto vakrere billedstøtter gjorde han sig.
Isra’ila kuringa ce mai yaɗuwa; ya fitar da’ya’ya wa kansa. Yayinda’ya’yan suka ƙaru, ya gina ƙarin bagadai; da ƙasarsa ta wadata, ya yi wa keɓaɓɓun duwatsu ado.
2 Deres hjerte er falskt, nu skal de bøte; han skal bryte ned deres altere og ødelegge deres billedstøtter;
Zuciyarsu masu ruɗu ne, yanzu kuwa dole su ɗauki laifinsu. Ubangiji zai rushe bagadansu yă kuma hallaka keɓaɓɓun duwatsunsu.
3 ja, nu skal de si: Vi har ingen konge; for vi har ikke fryktet Herren, og kongen, hvad kan vel han gjøre for oss?
Sa’an nan za su ce, “Ba mu da sarki domin ba mu girmama Ubangiji ba. Amma ko da ma muna da sarki, me zai yi mana?”
4 De har talt tomme ord, svoret falsk, inngått forbund, og retten skyter op som giftige urter på markens furer.
Sun yi alkawura masu yawa, suka yi rantsuwar ƙarya da kuma yarjejjeniyoyi; saboda haka ƙararraki suka taso kamar ciyayi masu dafi da aka nome a gona.
5 For Bet-Avens kalv er Samarias innbyggere i angst; ja, dens folk sørger over den, og dens avgudsprester skjelver for den - for dens herlighet, fordi den er ført bort fra dem.
Mutanen da suke zama a Samariya suna tsoro saboda gunki maraƙin Bet-Awen. Mutanensa za su yi makokinsa, haka ma firistocinsa matsafa, waɗanda suka yi farin ciki a kan darajarsa, don an ɗauke ta daga gare su aka kai ta zaman bauta.
6 Også den skal føres til Assur, som en gave til kong Jareb; skam skal Efra'im høste, og Israel skal skamme sig over sitt råd.
Za a ɗauke shi a kai Assuriya kamar gandu wa babban sarki. Efraim zai sha kunya; Isra’ila zai sha kunya saboda gumakan itacensa.
7 Samarias konge skal bli borte som en spån på vannets flate.
Samariya da sarkinta za su ɓace kamar kumfa a bisa ruwaye.
8 Og Avens offerhauger, Israels synd, skal tilintetgjøres; torner og tistler skal skyte op på deres altere, og de skal si til fjellene: Skjul oss! og til haugene: Fall over oss!
Za a hallaka masujadai kan tudu na mugunta zunubin Isra’ila ne. Ƙayayuwa da sarƙaƙƙiya za su yi girma su rufe bagadansu. Sa’an nan za su ce wa duwatsu, “Ku rufe mu!” Ga tuddai kuma, “Ku fāɗo a kanmu!”
9 Fra Gibeas dager av har du syndet, Israel! Der er de blitt stående, uten at krigen mot nidingene har nådd dem i Gibea.
“Tun daga kwanakin Gibeya, kun yi zunubi, ya Isra’ila, a can kuwa kuka ci gaba. Yaƙi bai cimma masu aikata mugunta a Gibeya ba?
10 Efter min lyst vil jeg tukte dem, og folkeslag skal samles imot dem, når jeg binder dem fast til begge deres misgjerninger.
Sa’ad da na ga dama, zan hukunta su; al’ummai za su taru su yi gāba da su don su daure su saboda zunubansu da suka riɓanya.
11 Efra'im er en opøvd kvige, som gjerne vil treske, men jeg legger et åk på dens fagre hals; jeg vil spenne Efra'im for, Juda skal pløie, Jakob skal harve.
Efraim horarriyar karsana ce mai son sussuka; saboda haka zan sa karkiya a kyakkyawan wuyanta. Zan bi da Efraim, Dole Yahuda yă yi noma, dole kuma Yaƙub yă ja garman noma.
12 Så eder en sæd, som rettferdigheten krever, få eder en høst efter kjærlighetens bud, bryt eder nytt land! For nu er det tiden til å søke Herren, til han kommer og lar rettferdighet regne over eder.
Ku shuka wa kanku adalci, ku girbe’ya’yan jinƙai marar ƙarewa, ku kuma nome ƙasar da ba a nome ba; gama lokaci ne na neman Ubangiji, sai ya zo ya zubo adalci a kanku.
13 I har pløid ugudelighet, I har høstet urett, I har ett løgnens frukt; for du har satt din lit til din ferd og til dine mange helter.
Amma kun shuka mugunta, kuka girbe mugu kuka ci’ya’yan ruɗu. Domin kun dogara da ƙarfinku da kuma a jarumawanku masu yawa,
14 Derfor skal det reise sig et krigsbulder blandt dine stammer, og alle dine festninger skal ødelegges, likesom Salman ødela Bet-Arbel på stridens dag, da både mor og barn blev knust.
hayaniyar yaƙi za tă tashi gāba da mutanenku, saboda a ragargaza kagaranku, kamar yadda Shalman ya ragargaza Bet-Arbel a ranar yaƙi, sa’ad da aka fyaɗa uwaye tare da’ya’yansu da ƙasa.
15 Sådant skal Betel føre over eder for eders store ondskaps skyld; når det lysner til dag, er det ute, aldeles ute med Israels konge.
Haka zai faru da kai, ya Betel, domin muguntarka ta yi yawa. Sa’ad da wannan rana ta zo, za a hallaka sarkin Isra’ila ƙaƙaf.