< Hebreerne 6 >

1 La oss derfor gå forbi barnelærdommen om Kristus og skride frem mot det fullkomne, så vi ikke atter legger grunnvollen med omvendelse fra døde gjerninger og tro på Gud,
Dole mu yi ƙoƙarin zama balagaggu mu kuma fara tunani game da abubuwan da suka fi koyarwan nan mai sauƙi game da Kiristi. Bai kamata mu ci gaba da magana game da me ya sa dole mu juye daga ayyukan da suke kawo mutuwa da kuma me ya sa za mu kasance da bangaskiya a cikin Allah ba.
2 med lære om dåp og håndspåleggelse, om dødes opstandelse og evig dom (aiōnios g166)
Kuma bai kamata mu ci gaba da koyar da umarnai game da baftisma, ɗibiya hannuwa, tashin matattu, da kuma madawwamin hukunci ba. (aiōnios g166)
3 Og dette vil vi gjøre, om Gud gir lov til det.
Da yardar Allah, za mu ci gaba ga ƙarin ganewa.
4 For det er umulig at de som engang er blitt oplyst og har smakt den himmelske gave og fått del i den Hellige Ånd
Waɗanda suka taɓa samun haske, waɗanda suka ɗanɗana kyauta ta sama, waɗanda suka sami rabo cikin Ruhu Mai Tsarki,
5 og har smakt Guds gode ord og den kommende verdens krefter, (aiōn g165)
waɗanda suka ɗanɗana daɗin maganar Allah da kuma ikokin zamani mai zuwa, (aiōn g165)
6 og så faller fra, atter kan fornyes til omvendelse, da de på ny korsfester Guds Sønn for sig og gjør ham til spott.
ba ya yiwuwa a sāke kawo su ga tuba in suka kauce, domin suna sāke gicciye Ɗan Allah ke nan suna kuma kunyata shi a gaban jama’a.
7 For den jord som drikker regnet som ofte faller på den, og som bærer gagnlig grøde for dem den dyrkes for, den får velsignelse fra Gud;
Ƙasar da take shan ruwan sama da yake fāɗi a kanta kullum da kuma take ba da hatsin da yake da amfani ga waɗanda ake noma dominsu, takan sami albarkar Allah.
8 men bærer den torner og tistler, da er den uduelig og forbannelse nær, og enden med den er å brennes.
Amma ƙasar da take ba da ƙaya da sarƙaƙƙiya ba ta da amfani tana kuma cikin hatsarin la’ana. A ƙarshe za a ƙone ta.
9 Men om eder, I elskede, er vi visse på det som bedre er, og som hører til frelse, enda vi taler således.
Abokaina, ko da yake muna irin maganan nan, mun tabbata kuna yi abubuwan nan masu kyau da waɗanda suka sami ceto suke yi.
10 For Gud er ikke urettferdig, så han skulde glemme eders verk og den kjærlighet I har vist mot hans navn, idet I har tjent og ennu tjener de hellige.
Allah ba marar adalci ba ne. Ba zai manta da aikinku da kuma ƙaunar da kuka nuna masa wajen taimakon mutanensa da kuma ci gaba da taimakonsu da kuke yi ba.
11 Men vi ønsker at enhver av eder må vise den samme iver for den fulle visshet i håpet inntil enden,
Muna so kowannenku yă nuna ƙwazon nan har zuwa ƙarshe, domin ku tabbatar da begenku.
12 forat I ikke skal bli trege, men efterfølge dem som ved tro og tålmod arver løftene.
Ba ma so ku zama masu ƙyuya, sai dai ku yi koyi da waɗanda ta wurin bangaskiya da haƙuri suka gāji abin da aka yi alkawari.
13 For da Gud gav Abraham løftet, svor han ved sig selv, eftersom han ingen større hadde å sverge ved, og sa:
Babu wanda ya fi Allah, saboda haka sa’ad da ya yi alkawari ga Ibrahim, sai ya rantse da sunansa,
14 Sannelig, jeg vil rikelig velsigne dig og storlig mangfoldiggjøre dig;
cewa, “Tabbatacce zan albarkace ka in kuma ba ka zuriya mai yawa.”
15 og da han således hadde ventet tålmodig, opnådde han det som var lovt.
Haka kuwa bayan Ibrahim ya jira da haƙuri, sai ya karɓi abin da aka yi alkawari.
16 For mennesker sverger jo ved den større, og eden er dem en ende på all motsigelse, til stadfestelse.
In mutane za su yi rantsuwa sukan yi haka da wanda ya fi su ne, rantsuwar kuwa takan tabbatar da abin da aka faɗa ta kuma kawo ƙarshen dukan gardama.
17 Derfor, da Gud vilde enn mere vise løftets arvinger hvor uryggelig hans vilje var, gikk han imellem med en ed,
Saboda haka da Allah ya so yă bayyana nufinsa marar canjawa a sarari ga magādan abin da aka yi alkawari, sai ya tabbatar da shi da rantsuwa.
18 forat vi ved to uryggelige ting, hvori Gud umulig kunde lyve, skulde ha en sterk trøst, vi som har tatt vår tilflukt til å gripe det håp som venter oss,
Allah ba ya karya! Haka ma alkawuransa da rantsuwarsa abubuwa biyu ne da ba a iya canjawa. Mun gudu zuwa wurin Allah domin kāriya. Ya kamata alkawuransa su ƙarfafawa sosai mu riƙe begen nan da yake gabanmu.
19 det vi har som et anker for sjelen, et som er trygt og fast og når innenfor forhenget,
Muna da wannan bege kamar anka na rai, kafaffe da kuma tabbatacce. Yana shiga tsattsarkan wuri na can ciki a bayan labule,
20 hvor Jesus gikk inn som forløper for oss, idet han blev yppersteprest til evig tid efter Melkisedeks vis. (aiōn g165)
inda Yesu, wanda ya sha gabanmu, ya shiga a madadinmu. Ya zama babban firist na har abada, bisa ga tsarin Melkizedek. (aiōn g165)

< Hebreerne 6 >