< Hebreerne 3 >

1 Derfor, hellige brødre, I som har fått del i et himmelsk kall, gi akt på den apostel og yppersteprest som vi bekjenner, Jesus,
Saboda haka,’yan’uwa tsarkaka, waɗanda suke da rabo a kiran nan na sama, ku kafa tunaninku a kan Yesu, manzo da kuma babban firist wanda muke shaidawa.
2 han som var tro mot den som gjorde ham dertil, likesom og Moses var i hele hans hus.
Ya yi aminci ga wanda ya naɗa shi, kamar yadda Musa ya yi aminci ga dukan gidan Allah.
3 For denne er aktet så meget større ære verd enn Moses, som den som har gjort huset, har større ære enn huset selv.
An ga Yesu ya cancanci girma fiye da Musa, kamar yadda mai ginin gida ya fi gidan daraja.
4 Hvert hus blir jo gjort av nogen; men den som har gjort alt, er Gud;
Gama kowane gida yana da wanda ya gina shi, amma maginin dukan abu Allah ne.
5 og Moses var vel tro i hele hans hus som tjener til å vidne om det som skulde tales,
Musa ya yi aminci a matsayin bawa cikin dukan gidan Allah, yana ba da shaida a kan abubuwan da za a faɗa nan gaba.
6 men Kristus som Sønn over hans hus, og hans hus er vi, såfremt vi holder vår frimodighet og det håp som vi roser oss av, fast inntil enden.
Amma Kiristi mai aminci ne kamar ɗa a gidan Allah. Mu kuwa gidansa ne, in muka tsaya gabanmu gadi da kuma begen da muke taƙama a kai.
7 Derfor, som den Hellige Ånd sier: Idag, om I hører hans røst,
Kamar dai yadda Ruhu Mai Tsarki ya ce, “Yau, in kuka ji muryarsa,
8 da forherd ikke eders hjerter som ved forbitrelsen, på fristelsesdagen i ørkenen,
kada ku taurare zukatanku, yadda kuka yi a tawayen nan, a lokacin gwaji a hamada,
9 hvor eders fedre fristet mig ved å sette mig på prøve, enda de så mine gjerninger i firti år;
inda kakanninku suka gwada ni, suka kuma gwada ni, ko da yake a cikin shekaru arba’in sun ga abin da na yi.
10 derfor harmedes jeg på denne slekt og sa: De farer alltid vill i hjertet; men de kjente ikke mine veier,
Shi ya sa na yi fushi da wancan zamani, na kuma ce, ‘Kullum zukatansu a karkace suke, ba su kuma san hanyoyina ba.’
11 så jeg svor i min vrede: Sannelig, de skal ikke komme inn til min hvile!
Saboda haka na yi rantsuwa a cikin fushina, ‘Ba za su taɓa shiga hutuna ba.’”
12 Se til, brødre, at det ikke i nogen av eder er et ondt, vantro hjerte, så han faller fra den levende Gud;
Ku lura fa,’yan’uwa, cewa kada waninku yă kasance da zuciya mai zunubi marar bangaskiya da takan juye daga bin Allah mai rai.
13 men forman hverandre hver dag, så lenge det heter idag, forat ikke nogen av eder skal forherdes ved syndens svik;
Sai dai ku ƙarfafa juna kullum, muddin akwai lokacin da ana ce da shi Yau, don kada waninku yă zama mai taurin zuciya ta wurin ruɗun zunubi.
14 for vi har fått del med Kristus, såfremt vi holder vår første fulle visshet fast inntil enden.
Mu masu tarayya ne da Kiristi idan mun riƙe bangaskiyarmu da ƙarfi daga farko har zuwa ƙarshe.
15 Når det sies: Idag, om I hører hans røst, da forherd ikke eders hjerter som ved forbitrelsen,
Kamar yadda aka faɗa cewa, “Yau, in kuka ji muryarsa, kada ku taurare zukatanku kamar yadda kuka yi a tawayen nan.”
16 hvem var det da vel som hørte den og dog forbitret ham? var det ikke alle de som gikk ut av Egypten ved Moses?
Su wane ne suka ji suka kuma yi tawaye? Ba su ne duk waɗanda Musa ya bi da su daga Masar ba?
17 Og hvem var det han harmedes på i firti år? var det ikke på dem som hadde syndet, så deres kropper falt i ørkenen?
Da su wane ne kuwa ya yi fushi har shekaru arba’in? Ba da waɗanda suka yi zunubi, waɗanda suka mutu a hamada ba?
18 Og om hvem var det han svor at de ikke skulde komme inn til hans hvile, uten om dem som ikke hadde villet tro?
Kuma ga su wane ne Allah ya rantse cewa ba za su taɓa shiga hutunsa ba, in ba ga marasa biyayyan nan ba?
19 Så ser vi da at det var for vantros skyld de ikke kunde komme inn.
Saboda haka mun ga cewa ba su iya shiga ba, saboda rashin bangaskiyarsu ne.

< Hebreerne 3 >