< 1 Mosebok 9 >

1 Og Gud velsignet Noah og hans sønner, og sa til dem: Vær fruktbare og bli mange og opfyll jorden!
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 Og frykt og redsel for eder skal være over alle dyr på jorden og over alle fugler under himmelen, over alt det som rører sig på jorden, og over alle fiskene i havet; i eders hånd er de gitt.
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Alt det som rører sig og lever, skal I ha til føde; likesom jeg gav eder de grønne urter, gir jeg eder alt dette.
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 Men kjøtt med dets sjel i, det er dets blod, skal I ikke ete.
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 Men for eders eget blod vil jeg kreve hevn; av hvert dyr vil jeg kreve hevn for det, og av mennesket, av enhvers bror, vil jeg kreve hevn for menneskets liv.
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 Den som utøser menneskets blod, ved mennesket skal hans blod utøses; for i Guds billede skapte han mennesket.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 Og vær I fruktbare og bli mange, vrimle på jorden og bli mange på den!
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 Og Gud sa til Noah og til hans sønner, som var med ham:
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 Nu vil jeg oprette min pakt med eder og med eders efterkommere,
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 og med alt levende som er hos eder, både fugler og fe og alle de ville dyr som er hos eder, alt som gikk ut av arken, alt som lever på jorden.
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 Jeg opretter min pakt med eder, og aldri mere skal alt kjød utryddes ved vannflom, og aldri mere skal der komme en vannflom som ødelegger jorden.
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 Og Gud sa: Dette er tegnet på den pakt som jeg gjør mellem mig og eder og alt levende som er hos eder, til evige tider:
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 Min bue setter jeg i skyen, og den skal være et tegn på pakten mellem mig og jorden.
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 Og når jeg fører skyer over jorden, og buen sees i skyen,
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 da vil jeg komme i hu den pakt som er mellem mig og eder og alt levende av alt kjød, og vannet skal aldri mere bli en flom som ødelegger alt kjød.
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 Og buen skal stå i skyen, og jeg vil se på den og komme i hu den evige pakt mellem Gud og alt levende av alt kjød som er på jorden.
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 Og Gud sa til Noah: Dette er tegnet på den pakt jeg har oprettet mellem mig og alt kjød som er på jorden.
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 Noahs sønner, som gikk ut av arken, var Sem, Kam og Jafet; og Kam var far til Kana'an.
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 Disse tre var Noahs sønner, og fra dem bredte menneskene sig ut over hele jorden.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 Og Noah var jorddyrker, og han var den første som plantet en vingård.
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 Og han drakk av vinen og blev drukken, og han klædde sig naken inne i sitt telt.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 Og da Kam, Kana'ans far, så sin far ligge naken, fortalte han det til begge sine brødre, som var utenfor.
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 Da tok Sem og Jafet et klæde og la det på sine skuldrer og gikk baklengs inn og dekket over sin fars blusel; og de vendte sine øine bort, så de ikke så sin fars blusel.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 Da så Noah våknet av sitt rus, fikk han vite hvad hans yngste sønn hadde gjort imot ham.
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 Da sa han: Forbannet være Kana'an! trælers træl skal han være for sine brødre.
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 Så sa han: Lovet være Herren, Sems Gud, og Kana'an være deres træl!
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 Gud gjøre det vidt for Jafet, han skal bo i Sems telter, og Kana'an være deres træl!
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 Efter vannflommen levde Noah ennu tre hundre og femti år.
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 Og alle Noahs dager blev ni hundre og femti år; så døde han.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.

< 1 Mosebok 9 >