< 1 Mosebok 38 >

1 På denne tid drog Juda ned fra det sted hvor hans brødre bodde, og han tok inn til en mann i Adullam, som hette Hira.
A wannan lokaci, Yahuda ya bar’yan’uwansa ya gangara don yă zauna da mutumin Adullam, mai suna Hira.
2 Der så Juda datteren til en kana'anittisk mann som hette Sua; og han tok henne til hustru og gikk inn til henne.
A can Yahuda ya sadu da’yar wani Bakan’ane, mai suna Shuwa. Ya aure ta, ya kuma kwana da ita;
3 Og hun blev fruktsommelig og fødte en sønn og kalte ham Er.
ta yi ciki, ta kuma haifi ɗa, wanda aka kira Er.
4 Så blev hun atter fruktsommelig og fødte en sønn, og hun kalte ham Onan.
Ta sāke yin ciki, ta haifi wani ɗa, ta kira shi Onan.
5 Siden fødte hun ennu en sønn og kalte ham Sela; da han blev født, var Juda i Kesib.
Ta kuma haifi wani ɗa har yanzu, aka kuwa ba shi suna Shela. A Kezib ne ta haife shi.
6 Og Juda tok en hustru til Er, sin førstefødte sønn; hun hette Tamar.
Sai Yahuda ya auro wa Er mata, ɗansa na fari, sunanta Tamar.
7 Men Er, Judas førstefødte, mishaget Herren, og Herren lot ham dø.
Amma Er, ɗan farin Yahuda mugu ne a fuskar Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi.
8 Da sa Juda til Onan: Gå inn til din brors hustru, og ta henne til ekte i din brors sted og opreis din bror avkom.
Sa’an nan Yahuda ya ce wa Onan, “Ka kwana da matar ɗan’uwanka ka cika wajibinka gare ta a matsayin ɗan’uwan miji, don ka samar wa ɗan’uwanka’ya’ya.”
9 Men Onan visste at avkommet ikke skulde høre ham til; når han derfor gikk inn til sin brors hustru, spilte han sæden på jorden for ikke å gi sin bror avkom.
Amma Onan ya san cewa’ya’yan ba za su zama nasa ba; saboda haka a duk sa’ad da ya kwana da matar ɗan’uwansa, sai yă zub da maniyyinsa a ƙasa don kada yă samar wa ɗan’uwansa’ya’ya.
10 Men det var ondt i Herrens øine det han gjorde, og han lot også ham dø.
Abin nan da ya yi mugunta ce a gaban Ubangiji, saboda haka Ubangiji ya kashe shi, shi ma.
11 Da sa Juda til Tamar, sin sønnekone: Bo som enke i din fars hus, til Sela, min sønn, er blitt voksen! For han tenkte: Ellers kommer også han til å dø, som hans brødre. Så drog Tamar hjem og bodde i sin fars hus.
Sai Yahuda ya ce wa surukarsa Tamar, “Ki yi zama kamar gwauruwa a gidan mahaifinki sai ɗana Shela ya yi girma.” Gama ya yi tunani, “Shi ma zai mutu, kamar’yan’uwansa.” Saboda haka Tamar ta je ta zauna a gidan mahaifinta.
12 Da nu en lengere tid var gått, døde Suas datter, Judas hustru, og da sørgetiden var over, gikk Juda op til Timna, til dem som klippet hans får, og hans venn Hira fra Adullam var med ham.
Bayan an daɗe sai matar Yahuda,’yar Shuwa ta rasu. Sa’ad da Yahuda ya gama makoki, sai ya haura zuwa Timna, zuwa wurin mutanen da suke askin tumakinsa, abokinsa Hira mutumin Adullam kuwa ya tafi tare da shi.
13 Da det nu blev fortalt Tamar at hennes svigerfar var på vei op til Timna for å klippe sine får,
Sa’ad da aka faɗa wa Tamar cewa, “Surukinki yana kan hanyarsa zuwa Timna don askin tumakinsa,”
14 tok hun sine enkeklær av og la et slør om sig og hyllet sig inn i det og satte sig ved inngangen til Ena'im, på veien til Timna; for hun så at Sela var blitt voksen, og at hun allikevel ikke var gitt ham til hustru.
sai ta tuɓe rigunan gwaurancinta ta rufe kanta da lulluɓi don ta ɓad da kamanninta, sa’an nan ta je ta zauna a ƙofar shigar Enayim, wadda take a hanyar zuwa Timna. Gama ta lura cewa ko da yake Shela yanzu ya yi girma, ba a ba da ita gare shi ta zama matarsa ba.
15 Da Juda så henne, tenkte han det var en skjøge; for hun hadde tilhyllet sitt ansikt.
Sa’ad da Yahuda ya gan ta, ya yi tsammani karuwa ce, gama ta lulluɓe fuskarta.
16 Så bøide han av fra veien og gikk bort til henne og sa: Kom, la mig gå inn til dig! For han visste ikke at det var hans sønnekone. Da sa hun: Hvad vil du gi mig for å gå inn til mig?
Bai san cewa ita surukarsa ce ba, sai ya ratse zuwa wurinta a gefen hanya ya ce, “Zo mana, in kwana da ke.” Sai ta ce, “Me za ka ba ni in na kwana da kai?”
17 Han svarte: Jeg vil sende dig et kje av min buskap. Da sa hun: Ja, dersom du vil gi mig et pant, til du sender mig det.
Ya ce, “Zan aika miki da ɗan akuya daga garkena.” Sai ta ce, “Za ka ba ni wani abu jingina, kafin ka aika da shi?”
18 Han sa: Hvad skal jeg gi dig til pant? Hun svarte: Ditt signet og din snor og staven som du har i hånden. Det gav han henne og gikk så inn til henne, og hun blev fruktsommelig med ham.
Ya ce, “Wace jingina zan ba ki?” Sai ta amsa, “Hatiminka da ka rataye a wuya da kuma sandan da yake a hannunka.” Ya ba da su gare ta, ya kuma kwana da ita, sai ta yi ciki.
19 Og hun stod op og gikk sin vei, og hun la sitt slør av sig og tok på sig sine enkeklær.
Bayan ta tafi, sai ta tuɓe lulluɓin, ta sāke sa tufafin gwaurancinta.
20 Og Juda sendte kjeet med sin venn fra Adullam for å få pantet tilbake av kvinnen; men han fant henne ikke.
Ana cikin haka sai Yahuda ya aika da ɗan akuya ta hannun abokinsa mutumin Adullam don yă karɓo masa jinginar daga wurin macen, amma bai same ta a can ba.
21 Og han spurte folkene der på stedet og sa: Hvor er skjøgen, hun i Ena'im, ved veien? De sa: Det har ikke vært nogen skjøge her.
Ya tambayi mutanen da suke zama a can ya ce, “Ina karuwar haikalin da take a bakin hanya a Enayim?” Sai suka ce, “Ba a taɓa kasance da karuwar haikali a nan ba.”
22 Så kom han tilbake til Juda og sa: Jeg fant henne ikke, og tilmed sa folkene der på stedet: Det har ikke vært nogen skjøge her.
Saboda haka sai ya koma zuwa wurin Yahuda ya ce, “Ban same ta ba. Ban da haka ma, mutanen da suke zama a can, sun ce, ‘Ba a taɓa kasance da wata karuwar haikali a nan ba.’”
23 Da sa Juda: La henne ha det, så vi ikke skal få skam av denne sak! Kjeet har jeg jo sendt henne, men du fant henne ikke.
Sa’an nan Yahuda ya ce, “Bari tă riƙe kayan kiɗa garin nema mu zama abin dariya. Ni kam, na aika da tunkiyar amma ba a same ta ba.”
24 Så gikk det omkring tre måneder; da kom folk og sa til Juda: Tamar, din sønnekone, har drevet hor, og nu er hun også blitt fruktsommelig i hor. Og Juda sa: Før henne ut, hun skal brennes!
Bayan misalin wata uku sai aka faɗa wa Yahuda cewa, “Tamar, surukarka ta yi laifin karuwanci, a sakamakon haka yanzu ta yi ciki.” Yahuda ya ce, “A fid da ita, a ƙone!”
25 Men da hun blev ført ut, sendte hun bud til sin svigerfar og lot si: Det er med den mann som eier disse ting, jeg er blitt fruktsommelig. Og hun sa: Se efter hvem som eier dette signet og disse snorer og denne stav!
Yayinda ake fitar da ita, sai ta aika saƙo zuwa wurin surukinta, ta ce, “Mutumin da yake da waɗannan kayan ne ya yi mini ciki.” Ta kuma ƙara da cewa, “Duba ko za ka gane da hatimin nan, da abin ɗamaran nan, da kuma sandan nan, ko na wane ne?”
26 Og Juda kjente dem igjen og sa: Hun er i sin gode rett mot mig fordi jeg ikke har gitt henne til min sønn Sela. Og han hadde ikke siden omgang med henne.
Yahuda ya gane su, sai ya ce, “Ai, ta fi ni gaskiya, da yake ban ba da ita ga ɗana Shela ba.” Bai kuwa ƙara kwana da ita ba.
27 Da den tid kom at hun skulde føde, se, da var det tvillinger i hennes liv.
Sa’ad da lokaci ya yi da za tă haihu, ashe, tagwaye’yan maza ne suke cikinta.
28 Og i det samme hun fødte, stakk den ene hånden frem; da tok jordmoren og bandt en rød tråd om hans hånd og sa: Denne kom først frem.
Yayinda take haihuwa, ɗaya daga cikinsu ya fid da hannunsa; sai ungonzomar ta ɗauki jan zare ta ɗaura a hannun, ta ce, “Wannan ne ya fito da farko.”
29 Men så drog han sin hånd tilbake, og da kom hans bror frem, og hun sa: Hvor du har brutt dig frem! Og de kalte ham Peres.
Amma sa’ad da ya janye hannunsa, sai ɗan’uwansa ya fito, sai ta ce, “Wato, haka ne ka keta ka fito!” Sai aka ba shi suna Ferez.
30 Så kom hans bror frem, han som hadde den røde tråd om hånden; ham kalte de Serah.
Sa’an nan ɗan’uwansa wanda yake da jan zare a hannunsa ya fito, aka kuma ba shi suna Zera.

< 1 Mosebok 38 >