< 1 Mosebok 12 >

1 Og Herren sa til Abram: Dra bort fra ditt land og fra din slekt og fra din fars hus til det land som jeg vil vise dig!
Ubangiji ya ce wa Abram, “Tashi ka bar ƙasarka, da mutanenka, da iyalin mahaifinka, ka tafi ƙasar da zan nuna maka.
2 Og jeg vil gjøre dig til et stort folk; jeg vil velsigne dig og gjøre ditt navn stort, og du skal bli en velsignelse!
“Zan mai da kai al’umma mai girma, zan kuma albarkace ka; zan sa sunanka yă zama mai girma, ka kuma zama sanadin albarka.
3 Og jeg vil velsigne dem som velsigner dig, og den som forbanner dig, vil jeg forbanne; og i dig skal alle jordens slekter velsignes
Zan albarkaci duk wanda ya albarkace ka, in kuma la’anci duk wanda ya la’anta ka, dukan mutanen duniya za su sami albarka ta wurinka.”
4 Så drog Abram bort som Herren hadde sagt til ham, og Lot drog med ham. Og Abram var fem og sytti år gammel da han drog ut fra Karan.
Saboda haka Abram ya tashi yadda Ubangiji ya faɗa masa; Lot ma ya tafi tare da shi. Abram yana da shekaru 75, sa’ad da ya tashi daga Haran.
5 Og Abram tok med sig Sarai, sin hustru, og Lot, sin brorsønn, og all deres eiendom som de hadde vunnet, og de folk som de hadde fått i Karan; og de drog ut for å reise til Kana'ans land, og de kom til Kana'ans land.
Abram ya ɗauki matarsa Saira da Lot ɗan ɗan’uwansa, da dukan mallakar da suka tattara, da kuma mutanen da suka samu a Haran, suka kama hanya zuwa ƙasar Kan’ana.
6 Og Abram drog gjennem landet til Sikem-bygden, til Mores terebintelund; og kana'anittene bodde dengang der i landet.
Abram ya ratsa ƙasar har zuwa wurin babban itace na More a Shekem. A lokacin Kan’aniyawa suna a ƙasar.
7 Da åpenbarte Herren sig for Abram og sa: Din ætt vil jeg gi dette land. Og han bygget der et alter for Herren, som hadde åpenbaret sig for ham.
Ubangiji ya bayyana ga Abram ya ce, “Ga zuriyarka ne zan ba da wannan ƙasa.” Saboda haka Abram ya gina bagade a can ga Ubangiji, wanda ya bayyana gare shi.
8 Derfra flyttet han til fjellene østenfor Betel og slo op sitt telt med Betel i vest og Ai i øst; og han bygget der et alter for Herren og påkalte Herrens navn.
Daga can, ya ci gaba zuwa wajen tuddai a gabashin Betel ya kafa tentinsa, Betel yana yamma, Ai, kuma a gabas. A can ya gina bagade ga Ubangiji ya kuma kira bisa sunan Ubangiji.
9 Og Abram drog efter hvert videre til sydlandet.
Sa’an nan Abram ya tashi ya ci gaba da tafiya zuwa wajen Negeb.
10 Så blev det hungersnød i landet; og Abram drog ned til Egypten for å opholde sig der, for hungersnøden var stor i landet.
To, a lokacin, an yi yunwa a ƙasar, sai Abram ya gangara zuwa Masar don yă zauna a can na ɗan lokaci, domin yunwa ta yi tsanani.
11 Og da han ikke hadde langt igjen til Egypten, sa han til Sarai, sin hustru: Jeg vet jo at du er en vakker kvinne.
Yayinda yana gab da shiga Masar, sai ya ce wa matarsa Saira, “Na sani ke kyakkyawar mace ce.
12 Når nu egypterne får se dig, vil de si: Dette er hans hustru, og så slår de mig ihjel og lar dig leve.
Sa’ad da Masarawa suka ganki, za su ce, ‘Wannan matarsa ce.’ Za su kuwa kashe ni, su bar ki da rai.
13 Kjære, si at du er min søster, så det kan gå mig vel, og mitt liv kan bli spart for din skyld!
Saboda haka ki ce ke’yar’uwata ce, domin ta dalilinki a mutunta ni, a kuma bar ni da rai.”
14 Da nu Abram kom til Egypten, så egypterne at kvinnen var meget vakker.
Sa’ad da Abram ya isa Masar, Masarawa suka ga cewa Saira kyakkyawa mace ce ƙwarai.
15 Også Faraos høvdinger så henne og roste henne for Farao, og så blev kvinnen hentet til Faraos hus.
Sa’ad da fadawan Fir’auna suka gan ta kuwa, sai suka yabe ta wajen Fir’auna, aka kuwa kawo ta cikin fadarsa.
16 Og han gjorde vel imot Abram for hennes skyld, og han fikk både småfe og storfe og asener og træler og trælkvinner og aseninner og kameler.
Ya mutunta Abram sosai saboda ita, Abram kuwa ya mallaki tumaki da shanu, da jakuna maza da mata, da bayi maza da mata, da kuma raƙuma.
17 Men Herren hjemsøkte Farao og hans hus med store plager for Abrams hustru Sarais skyld.
Amma Ubangiji ya wahalar da Fir’auna da gidansa da cututtuka masu zafi saboda Saira, matar Abram.
18 Da kalte Farao Abram til sig og sa: Hvad er det du har gjort imot mig? Hvorfor lot du mig ikke vite at hun er din hustru?
Saboda haka Fir’auna ya kira Abram ya ce, “Me ke nan ka yi mini? Me ya sa ba ka faɗa mini cewa ita matarka ce ba?
19 Hvorfor sa du: Hun er min søster, så jeg tok henne til hustru? Se, her har du din hustru, ta henne og gå!
Don me ka ruɗe ni cewa, ‘Ita’yar’uwata ce,’ har na ɗauke ta tă zama matata? To, ga matarka. Ɗauke ta ka tafi.”
20 Og Farao gav nogen menn befaling til å følge ham på veien med hans hustru og alt det han eide.
Sa’an nan Fir’auna ya yi wa mutanensa umarni a kan Abram, suka kuwa sallame shi tare da matarsa da kuma dukan abin da yake da shi.

< 1 Mosebok 12 >