< Galaterne 6 >

1 Brødre! om også et menneske blir overlistet av nogen synd, da hjelp ham til rette, I åndelige, med saktmodighets ånd; men se til dig selv at ikke du og blir fristet!
’Yan’uwa, in an kama wani yana cikin yin zunubi, ku da kuke masu ruhaniya ya kamata ku komo da shi a kan hanya a hankali. Amma ku lura da kanku, domin kada maimakon dawowa da ɗan’uwanku, ku ma ku fāɗi cikin jarraba.
2 Bær hverandres byrder, og opfyll på den måte Kristi lov!
Ku ɗauki nawayar juna, a haka kuwa za ku cika dokar Kiristi.
3 For dersom nogen tykkes sig å være noget og er dog intet, da dårer han sig selv.
In wani yana tsammani shi wani abu ne alhali kuwa shi ba kome ba, ruɗin kansa yake yi.
4 Men enhver prøve sin egen gjerning, og da skal han ha sin ros bare efter det han selv er, og ikke efter det som næsten er;
Kowa yă auna ayyukansa. A sa’an nan ne zai iya yin taƙama da kansa, ba tare da kwatanta kansa da wani ba,
5 for hver skal bære sin egen byrde.
gama kowa zai ɗauki kayansa.
6 Den som oplæres i ordet, skal dele alt godt med den som lærer ham.
Duk haka, wanda aka koya wa maganar Kiristi, bari yă raba abubuwan nan na alheri tare da wanda ya koyar da shi.
7 Far ikke vill! Gud lar sig ikke spotte; for det som et menneske sår, det skal han og høste.
Kada a ruɗe ku. Ba a yi wa Allah ba’a. Mutum yakan girbe abin da ya shuka ne.
8 For den som sår i sitt kjød, skal høste fordervelse av kjødet; men den som sår i Ånden, skal høste evig liv av Ånden. (aiōnios g166)
Wanda ya yi shuki don yă gamshi mutuntakarsa, daga wannan mutuntaka zai girbi hallaka. Wanda ya yi shuki domin yă gamshi Ruhu, daga Ruhu zai girbi rai madawwami. (aiōnios g166)
9 Men la oss gjøre det gode og ikke bli trette! for vi skal høste i sin tid, såfremt vi ikke går trett.
Kada mu gaji da yin nagarta, gama a daidai lokaci za mu girbe amfani, in ba mu fid da zuciya ba.
10 La oss derfor, mens vi har leilighet til det, gjøre det gode mot alle, men mest mot troens egne folk!
Saboda haka, in da hali, bari mu aikata nagarta ga dukan mutane, musamman ga waɗanda suke na iyalin masu bi.
11 Se, med hvor store bokstaver jeg skriver til eder med min egen hånd!
Ku dubi irin manya-manyan harufan da na yi amfani da su yayinda nake rubuta muku da hannuna!
12 Så mange som vil ta sig godt ut i kjødet, disse er det som tvinger eder til å la eder omskjære, bare for ikke å bli forfulgt for Kristi korses skyld.
Waɗanda suke son nuna bajinta a fili suna ƙoƙari su tilasta muku ku yi kaciya ne. Dalilin kaɗai da suke yin haka shi ne don gudu kada a tsananta musu saboda gicciyen Kiristi ne.
13 For ikke engang de som lar sig omskjære, holder selv loven; men de vil at I skal la eder omskjære, forat de kan rose sig av eders kjød.
Kai, su masu kaciya ma ba su kiyaye Doka ba, duk da haka suna so a yi muku kaciya don su yi taƙama kan an yi muku kaciya.
14 Men det være langt fra mig å rose mig uten av vår Herre Jesu Kristi kors; for ved det er verden blitt korsfestet for mig og jeg for verden.
Kada in taɓa yin taƙama ga kome sai dai a cikin gicciyen Ubangijinmu Yesu Kiristi, wanda ta wurinsa aka gicciye duniya a gare ni, aka kuma gicciye ni ga duniya.
15 For hverken omskjærelse eller forhud er noget, men bare en ny skapning.
Kaciya ko rashin kaciya ba wani abu ba ne; abin da yake da amfani shi ne sabuwar halitta.
16 Og så mange som går frem efter denne rettesnor, fred og miskunn være over dem og over Guds Israel!
Salama da jinƙai su tabbata ga dukan waɗanda suke bin wannan ƙa’ida, har ma ga Isra’ila na Allah.
17 Herefter volde ingen mig uleilighet! for jeg bærer Jesu merketegn på mitt legeme.
A ƙarshe, kada kowa yă ƙara damuna, gama ina ɗauke da raunuka masu nuna ni bawan Ubangiji Yesu ne.
18 Vår Herre Jesu Kristi nåde være med eders ånd, brødre! Amen.
’Yan’uwa! Alherin Ubangijinmu Yesu Kiristi yă kasance tare da ruhunku. Amin.

< Galaterne 6 >