< Galaterne 4 >
1 Men jeg sier: Så lenge arvingen er barn, er det ingen forskjell mellem ham og en træl, enda han er herre over alt sammen;
Ina cewa muddin magaji yaro ne, babu bambancin sa da bawa, ko da yake shine mai mallakan dukan kadarorin.
2 men han er under formyndere og husholdere inntil den tid som hans far forut har fastsatt.
A maimakon haka, yana karkashin masu jagora da amintattu har sai lokacin da mahaifinsa ya ajiye.
3 Således var også vi, dengang vi var barn, trælbundet under verdens barnelærdom;
Hakannan mu ma, lokaci da muke yara, an rike mu cikin kangi na tushin ka'idojin wannan duniya.
4 men da tidens fylde kom, utsendte Gud sin Sønn, født av en kvinne, født under loven,
Amma da lokacin ya yi daidai, Allah ya aiko da dansa, haihuwar mace, haihuwar karkashin shari'a.
5 forat han skulde kjøpe dem fri som var under loven, forat vi skulde få barnekår.
Ya yi haka ne domin ya fanshi wadanda ke a karkashin shari'a, domin mu karbi diyanci a matsayin 'ya'ya.
6 Og fordi I er sønner, har Gud sendt sin Sønns Ånd i våre hjerter, som roper: Abba, Fader!
Domin ku 'ya'ya ne, Allah ya aiko da Ruhun Dansa cikin zuciyarmu, Ruhun wanda ke kirar, “Abba, Uba.”
7 Så er du da ikke lenger træl, men sønn; men er du sønn, da er du og arving ved Gud.
Saboda wannan dalilin kai ba kuma bawa ba ne amma da. Idan kai da ne, hakannan kuma kai ma magaji ne ta wurin Allah.
8 Men dengang da I ikke kjente Gud, trælet I under de guder som i virkeligheten ikke er guder;
Duk da haka a da, da ba ku san Allah ba, bayi ne ku ga alloli wadanda ainihi ba alloli ba ne ko kadan.
9 men nu, da I kjenner Gud, ja det som mere er, er kjent av Gud, hvorledes kan I da vende om igjen til den skrøpelige og fattige barnelærdom? vil I da på ny igjen træle under den?
Amma yanzu da kuka san Allah, ko kuma, yanzu da Allah ya san ku, me ya sa kuke sake komawa zuwa ga tushen ka'idodin nan mara karfi da amfani? Kuna so ku sake komawa zaman bayi kuma daga farko?
10 I tar vare på dager og måneder og tider og år;
Kuna kiyaye ranaku na musamman, sabobin watanni, lokatai, da shekaru.
11 jeg frykter for eder at jeg kanskje forgjeves har gjort mig møie med eder.
Ina ji maku tsoro. Ina tsoro cewa kamar na yi aiki cikinku a wofi.
12 Vær som jeg! for jeg er jo som I. Brødre! jeg ber eder. I har ingen urett gjort mig;
Ina rokon ku 'yan'uwa, ku zama kamar yadda nake, domin ni ma na zama kamar ku. Ba ku yi mani laifin komai ba.
13 men I vet at det var på grunn av skrøpelighet i mitt kjød at jeg første gang kom til å forkynne evangeliet for eder;
Amma kun sani cewa saboda rashin lafiya ne na yi maku shelar bishara da farko.
14 og til tross for den fristelse som voldtes eder ved mitt kjød, ringeaktet og avskydde I mig ikke. I tok imot mig som en Guds engel, ja, som Kristus Jesus.
Ko da yake halin da nake ciki cikin jiki a zahiri ya sa ku cikin gwaji, ba ku raina ni ba ko kuma kuka watsar da ni. A maimakon haka, kun karbe ni kamar mala'ikan Allah, kamar ni Almasihu Yesu ne da kansa.
15 Hvor I dengang priste eder salige! for jeg gir eder det vidnesbyrd at hadde det vært mulig, så hadde I revet eders øine ut og gitt mig dem.
Saboda haka, yanzu ina murnar taku? Domin ina shaidar ku, idan mai yiwuwa ne, da kun kwakulo idanunku, kun ba ni.
16 Så er jeg da blitt eders fiende ved å si eder sannheten!
To kenan, na zama makiyin ku ne saboda na gaya maku gaskiya?
17 De legger sig efter eder med en iver som ikke er god; men de vil stenge eder ute, forat I skal være ivrige for dem.
Suna neman ku da himma ba domin wani alheri ba ne. Suna so su raba ni da ku domin ku bi su.
18 Men det er godt å vise iver i det gode alltid, og ikke bare når jeg er til stede hos eder.
Yana da kyau ko yaushe a yi himma domin dalilai masu kyau, ba kuma kawai sa'adda ina tare da ku ba.
19 Mine barn, som jeg atter føder med smerte, inntil Kristus vinner skikkelse i eder!
'Ya'yana kanana, sabili da ku ina cikin zafin nakuda kuma sai Almasihu ya samu kafuwa cikinku.
20 Jeg skulde ønske å være til stede hos eder nu og omskifte min røst; for jeg er rådvill med eder.
Da ma a ce ina tare da ku yanzu in canza muryata, domin ina damuwa a kanku kwarai.
21 Si mig, I som vil være under loven: Hører I ikke loven?
Ku gaya mani, ku da kuke marmarin ku zo karkashin shari'a, ba ku ji abin da shari'ar ta ce ba?
22 Det er jo skrevet at Abraham hadde to sønner, én med trælkvinnen og én med den frie kvinne;
A rubuce yake cewa, Ibrahim yana da 'ya'ya maza biyu, daya dan baiwa ne, dayan kuma dan 'yantaciyar mace ne.
23 men trælkvinnens sønn er født efter kjødet, den frie kvinnes derimot ifølge løftet.
Abin lura anan, dan baiwar an haife shi ta hanyar mutuntaka ne, amma dan 'yantaciyar macen, an haife shi ta wurin alkawari ne.
24 I dette ligger en dypere mening under; for disse kvinner er to pakter, den ene fra berget Sinai, og den føder barn til trældom; dette er Hagar.
Ana iya bayyana abubuwan nan a hanyar kwatanci kamar haka, wadannan mata na kama da alkawarai ne guda biyu. Dayan alkawarin daga dutsen Sinayi ne. Ta haifi 'ya'ya da ke bayi ne su. Ita ce Hajaratu.
25 For Hagar er berget Sinai i Arabia, og svarer til det Jerusalem som nu er; for det er i trældom med sine barn.
Yanzu fa, Hajaratu ita ce dutsen Sinayi da ke Arebiya. Misali ce na Urushalima na yanzu, domin tana cikin bauta tare da 'ya'yanta.
26 Men det Jerusalem som er der oppe, er fritt, og det er vår mor;
Amma Urushalima da ke bisa 'yantacciya ce, ita ce mahaifiyarmu.
27 for det er skrevet: Vær glad, du ufruktbare, du som ikke føder! bryt ut og rop, du som ikke har veer! for den enslige kvinnes barn er mange flere enn hennes som har mannen.
Kamar yadda yake a rubuce, “Ki yi murna, ke bakarariya, ke da ba ki taba haihuwa ba. Ki yi shewa na farinciki, ke da ba ki dandana haihuwan da ba. Domin 'ya'yan bakarariya da yawa suke, fiye da ta mace mai miji.”
28 Men vi, brødre, er løftets barn, likesom Isak.
Yanzu fa, 'yan'uwa, kamar yadda Ishaku yake, haka muke, wato 'ya'yan alkawari.
29 Men likesom dengang han som var født efter kjødet, forfulgte ham som var født efter Ånden, således og nu.
A lokacin can, shi wanda aka haife shi ta hanyar mutuntaka ya tsananta wa wanda aka haife shi ta hanyar Ruhu. Haka yake har yanzu.
30 Men hvad sier Skriften? Driv ut trælkvinnen og hennes sønn! for trælkvinnens sønn skal ingenlunde arve med den frie kvinnes sønn.
Amma menene nassi ya ce? “Ka kori baiwar nan tare da danta. Domin dan baiwar nan ba za ya ci gado tare da dan macen nan da ke 'yantacciya ba.”
31 Derfor, brødre, er vi ikke trælkvinnens barn, men den frie kvinnes.
Saboda haka 'yan'uwa, mu ba 'ya'yan baiwa ba ne, a maimakon haka, mu 'ya'yan macen nan ne da ke 'yantacciya.