< Esekiel 46 >

1 Så sier Herren, Israels Gud: Den indre forgårds port, den som vender mot øst, skal være lukket de seks arbeidsdager; men på sabbatens dag skal den åpnes, og likeså på nymånedagen.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a rufe ƙofa ta fili na can cikin da take fuskantar gabas ranaku shida na aiki, amma a ranar Asabbaci da kuma a ranar ganin Sabuwar Wata a buɗe ta.
2 Og fyrsten skal da gå inn gjennem portens forhall utenfra og stå ved portens dørstolpe; prestene skal ofre hans brennoffer og hans takkoffer, og han skal tilbede på portens treskel og så gå ut igjen; men porten skal ikke lukkes før om aftenen.
Sarki zai shiga daga waje ta shirayin hanyar shiga yă tsaya a madogarar ƙofa. Firistoci za su miƙa hadayarsa ta ƙonawa da hadayunsa na salama. Zai yi sujada a madogarar ƙofar hanyar shiga sa’an nan ya fita, amma ba za a rufe ƙofar ba sai da yamma.
3 Og folket i landet skal på sabbatene og nymånedagene tilbede for Herrens åsyn ved inngangen til denne port.
A Asabbatai da kuma a Sabuwar Wata mutanen ƙasar za su yi sujada a gaban Ubangiji a mashigin wannan hanyar shiga.
4 Og brennofferet som fyrsten skal ofre til Herren på sabbatens dag, skal være seks lam uten lyte og en vær uten lyte,
Hadaya ta ƙonawar da sarki ya kawo wa Ubangiji a ranar Asabbaci’yan raguna shida ne da rago guda, dukansu marasa lahani.
5 og som matoffer en efa til væren, og som matoffer til lammene så meget som han finner for godt å gi, og en hin olje til hver efa.
Hadayar garin da aka bayar tare da ragon efa guda ne, hadayar garin da’yan ragunan yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
6 Og på nymånedagen en ung okse uten lyte og seks lam og en vær; uten lyte skal de være.
A ranar Sabuwar Wata zai miƙa ɗan bijimi,’yan raguna guda shida da kuma rago guda, dukansu marasa lahani.
7 Og som matoffer skal han ofre en efa til oksen og en efa til væren, og til lammene så meget som han har råd til, og en hin olje til hver efa.
Zai tanada a matsayin hadaya ta gari, efa guda tare da bijimi, efa guda tare da’yan raguna, da kuma’yan raguna yadda ya ga dama, tare da kwalabar mai don kowace efa.
8 Og når fyrsten går inn, skal han gå inn gjennem portens forhall, og samme vei skal han gå ut igjen.
Sa’ad da sarki zai shiga, zai shiga ta shirayin hanyar shiga, zai kuma fita ta nan.
9 Men når folket i landet går inn for Herrens åsyn på høitidene, skal den som går inn igjennem nordporten for å tilbede, gå ut igjennem sydporten, og den som går inn igjennem sydporten, gå ut igjennem porten mot nord; han skal ikke vende tilbake gjennem den port som han gikk inn gjennem, men de skal gå ut rett frem for sig.
“‘Sa’ad da mutanen ƙasar suka zo gaban Ubangiji a ƙayyadaddun bukukkuwa, duk wanda ya shiga ta ƙofar arewa don yă yi sujada sai ya fita ta ƙofar kudu; kuma duk wanda ya shiga ta ƙofar kudu sai ya fita ta ƙofar arewa. Ba wanda zai koma ta ƙofar da ya shiga, amma kowa zai fita a ƙofar ɗaura da wadda ya shiga.
10 Og fyrsten skal gå inn blandt de andre, når de går inn; og når de går ut, skal de gå ut sammen.
Sarki zai kasance a cikinsu, zai shiga sa’ad da suke shiga ya kuma fita sa’ad da suka fita.
11 Og på festene og høitidene skal matofferet være en efa til hver okse og en efa til hver vær, og til lammene så meget som han finner for godt å gi, og en hin olje til hver efa.
“‘A bukukkuwa da ƙayyadaddun bukukkuwa, hadaya ta gari zai zama efa tare da bijimi, efa da rago, da kuma’yan raguna da ya ga dama, haɗe da kwalabar mai.
12 Når fyrsten vil ofre et frivillig offer - et brennoffer eller takkoffere som frivillig offer til Herren, da skal de åpne for ham den port som vender mot øst, og han skal ofre sitt brennoffer og sine takkoffer således som han gjør det på sabbatens dag; og så skal han gå ut igjen, og når han er gått ut, skal porten lukkes.
Sa’ad da sarki ya ba da hadaya ta yardar rai ga Ubangiji, ko hadaya ta ƙonawa ce ko hadayun salama ne, sai a buɗe masa ƙofar da take fuskantar gabas. Zai miƙa hadayarsa ta ƙonawa ko hadayarsa ta salama yadda yakan yi a ranar Asabbaci. Sa’an nan ya fita, bayan kuma ya fita, sai a rufe ƙofar.
13 Som brennoffer til Herren skal du hver dag ofre et årsgammelt lam uten lyte; hver morgen skal du ofre det.
“‘Kullum za ku tanada ɗan rago bana ɗaya marar lahani don hadaya ta ƙonawa ga Ubangiji; kowace safiya za ku tanada shi.
14 Og som matoffer dertil skal du hver morgen ofre en sjettedel efa og en tredjedel hin olje til å væte melet med; det er et matoffer for Herren - forskrifter som skal gjelde evig, for all tid.
Tare da shi za ku tanada hadaya ta gari kowace safiya, da ya haɗa da kashi ɗaya bisa shida na efa tare da kashi ɗaya bisa uku na mai ga garin da aka cuɗa. Miƙawar wannan hadaya ta gari ga Ubangiji dawwammamiyar farilla ce.
15 Således skal de hver morgen ofre lammet og matofferet og oljen; det skal være et stadig brennoffer.
Saboda haka za a tanada ɗan rago da hadaya ta gari da kuma mai kowace safiya don hadaya ta ƙonawa ta kullum.
16 Så sier Herren, Israels Gud: Når fyrsten gir nogen av sine sønner en gave, så er det hans arv; det skal tilhøre hans sønner, det er deres arv og eie.
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa in sarkin ya ba wa ɗaya daga cikin’ya’yansa kyauta daga gādonsa, zai kuwa zama na zuriyar; zai kuwa zama mallakarsu ta wurin gādo.
17 Men når han gir en gave av sin arv til en av sine tjenere, så skal det tilhøre ham inntil frihetsåret, men så komme tilbake til fyrsten; bare hans sønner skal hans arv tilhøre.
In kuma ya ba wa ɗaya daga cikin bayinsa kyauta daga gadonsa, bawan zai iya riƙe shi sai shekarar’yantarwa; sa’an nan ya mayar wa sarkin. Gādon sarki na’ya’yansa maza ne kaɗai; na su ne.
18 Fyrsten må ikke ta noget av folkets arv, så han driver dem bort fra deres eiendom; av sin egen eiendom skal han la sine sønner arve, så mitt folk ikke skal bli spredt ved å miste sine eiendommer.
Kada sarki ya ƙwace gādon mutane, yana korinsu daga mallakarsu. Zai ba wa’ya’yansa maza gādonsu daga cikin mallakarsa, don kada a raba wani daga mutanena da mallakarsa.’”
19 Så førte han mig gjennem den inngang som var ved siden av porten, til de hellige kammer som var bestemt for prestene, og som vendte mot nord, og se, der var en plass ytterst mot vest.
Sa’an nan mutumin ya fitar da ni ta ƙofar shiga a gefen ƙofar zuwa tsarkakakkun ɗakuna waɗanda suke fuskantar arewa, waɗanda suke na firistoci, ya kuma nuna mini wani wuri daga can ƙurewar yamma.
20 Og han sa til mig: Dette er den plass hvor prestene skal koke skyldofferet og syndofferet, og hvor de skal bake matofferet, så de ikke har nødig å bære det ut i den ytre forgård og således hellige folket.
Ya ce mini, “Wannan shi ne wurin da firistoci za su dafa hadaya don laifi, da hadaya don zunubi, a nan ne kuma za su toya hadaya ta gari, domin kada su kai su a filin da yake waje, su tsarkake mutane.”
21 Så lot han mig gå ut i den ytre forgård, og førte mig omkring til forgårdens fire hjørner, og se, der var en mindre gård i hvert hjørne av forgården.
Sa’an nan ya kawo ni filin da yake waje ya kuma bi da ni kewaye da kusurwoyi huɗunsa, na kuma ga kowace kusurwa na wani fili.
22 I forgårdens fire hjørner var det lukkede gårder, firti alen lange og tretti alen brede; de fire gårder i hjørnene hadde samme mål.
A kusurwoyi huɗu na filin da yake waje akwai waɗansu filaye a haɗe, tsawonsu kamu arba’in fāɗinsu kuwa kamu talatin; kowane fili a kusurwoyi huɗun nan girmansu ɗaya ne.
23 Og det gikk en muret ring rundt om i dem, rundt om i alle fire, og det var gjort kokesteder under de murede ringer rundt om.
Kewaye da cikin kowane filin huɗun nan akwai ginin dutse, da murhu da aka gina a kewaye a ƙarƙashin ginin.
24 Og han sa til mig: Dette er de kokehus hvor husets tjenere skal koke folkets slaktoffer.
Sai ya ce mini, “Waɗannan su ne ɗakunan dahuwa inda masu hidima a haikali za su dafa hadayun da jama’a.”

< Esekiel 46 >