< Esekiel 38 >

1 Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 Menneskesønn! Vend ditt åsyn mot Gog i Magogs land, fyrsten over Ros, Mesek og Tubal, og spå imot ham!
“Ɗan mutum, ka fuskanci Gog, na ƙasar Magog, babban sarkin Meshek da Tubal; ka yi annabci a kansa
3 Og du skal si: Så sier Herren, Israels Gud: Se, jeg kommer over dig, Gog, fyrste over Ros, Mesek og Tubal!
ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
4 Og jeg vil vende dig om og legge kroker i dine kjever og føre dig ut med hele din hær, hester og ryttere, alle sammen prektig klædd, en stor skare med store og små skjold, alle sammen med sverd i hånd.
Zan juyar da kai, in sa ƙugiyoyi a muƙamuƙanka in fitar da kai tare da dukan sojojinka, dawakanka, mahayan dawakanka saye da makamai, da kuma jama’a mai girma masu riƙe da garkuwoyi manya da ƙanana, dukansu da takuba a zāre.
5 Persere, etiopere og puteere er med dem, alle sammen med skjold og hjelm;
Farisa, Kush da Fut za su kasance tare da su, duka riƙe da garkuwoyi da hulunan kwano,
6 Gomer og alle dets skarer, Togarma-folket i det ytterste Norden og alle dets skarer, mange folkeslag er med dig.
haka ma Gomer da dukan sojojinsa, da Bet Togarma daga can arewa tare da dukan sojojinsa, al’ummai masu yawa tare da kai.
7 Rust dig og gjør alt ferdig, du og alle dine skarer, som har samlet sig hos dig, og du skal være deres fører.
“‘Ka shirya; ka kintsa, kai da dukan jama’arka da suka taru kewaye da kai, ka kuma zama mai ba su umarni.
8 Når lang tid er gått, kommer turen til dig; ved årenes ende skal du komme til et land som er utfridd fra sverdet, og hvis folk er samlet fra mange folkeslag, op på Israels fjell som stadig hadde ligget øde; men nu er det ført ut fra folkene, og de bor der trygt alle sammen.
Bayan kwanaki masu yawa za a kira ka. A shekaru masu zuwa za ka kai hari a ƙasar da ta farfaɗo daga yaƙi, wadda aka tattara mutanenta daga al’ummai masu yawa zuwa duwatsun Isra’ila, dā kango ne sosai. An fitar da su daga al’ummai, yanzu kuwa dukansu suna zama lafiya.
9 Dit skal du dra op; som en storm skal du komme, som en sky skal du være til å skjule landet, du og alle dine skarer og mange folkeslag med dig.
Kai da dukan sojojinka da kuma al’ummai masu yawa da suke tare da kai za ku haura, kuna cin gaba kamar hadari; za ku zama kamar girgijen da yake rufewa ƙasa.
10 Så sier Herren, Israels Gud: På den dag skal tanker stige op i ditt hjerte, og du skal tenke ut et ondt råd
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, tunani zai shiga cikin zuciyarka za ka kuma ƙirƙiro muguwar dabara.
11 og si: Jeg vil dra op imot et land med åpne byer, jeg vil komme over fredelige folk, som bor trygt, som alle sammen bor uten murer og hverken har bom eller porter -
Za ka ce, “Zan kai hari wa ƙasar da ƙauyukanta ba su da katanga; zan fāɗa wa mutanen da suke zamansu kurum cikin salama, dukansu suna zama babu katanga babu ƙofofi ko ƙyamare.
12 for å rane og røve og ta hærfang, for å vende din hånd mot ruiner som er bygget op igjen, og mot et folk som er sanket sammen fra folkene, som har samlet sig fe og gods, som bor på jordens navle
Zan washe in kwashe ganima in kuma juye hannuna gāba da kufai da aka sāke zaunar da mutanen da aka tattara daga al’ummai, masu yawan shanu da kayayyaki, masu zama a tsakiyar ƙasa.”
13 Sjeba og Dedan og kjøbmennene fra Tarsis og alle deres unge løver skal si til dig: Kommer du for å rane og røve? Har du samlet dine skarer for å vinne hærfang, for å føre bort sølv og gull, for å ta fe og gods, for å gjøre et stort bytte?
Sheba da Dedan da’yan kasuwar Tarshish da dukan ƙauyukanta za su ce maka, “Ka zo ka kwashe ganima ne? Ka tattara jama’arka don ka yi waso, ka kuma kwashe azurfa da zinariya, ka kwashe shanu da kayayyaki ka kuma ƙwace ganima mai yawa?”’
14 Derfor skal du spå, menneskesønn, og si til Gog: Så sier Herren, Israels Gud: Se, på den tid da mitt folk Israel bor trygt, får du nok vite det.
“Saboda haka ɗan mutum, ka yi annabci ka ce wa Gog, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa a ranar, sa’ad da mutanena Isra’ila suna zaman lafiya, ba za ka sani ba?
15 Da skal du komme fra ditt land, fra det ytterste Norden, du og mange folkeslag med dig, alle sammen ridende på hester, en stor skare og en tallrik hær,
Za ka zo daga wurinka a can arewa, kai da al’ummai masu yawa tare da kai, dukansu suna hawan dawakai, jama’a mai yawa, babbar runduna.
16 og du skal dra op imot mitt folk Israel som en sky og skjule landet; i de siste dager skal det skje, da lar jeg dig komme over mitt land, forat folkene skal lære mig å kjenne, når jeg for deres øine åpenbarer min hellighet på dig, Gog!
Za ka ci gaba a kan mutanena Isra’ila kamar yadda girgijen yakan rufe ƙasa. A kwanaki masu zuwa, ya Gog, zan kawo ka, ka yi yaƙi da ƙasata, domin al’ummai su san ni sa’ad da na nuna kaina mai tsarki ta wurinka a gabansu.
17 Så sier Herren, Israels Gud: Er det dig jeg har talt om i fordums dager ved mine tjenere, Israels profeter, de som spådde i de dager, år efter år, at jeg vilde la dig komme over dem?
“‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ba kai ba ne na yi magana da kai a kwanakin dā ta wurin bayina annabawan Isra’ila? A lokacin sun yi annabci shekaru masu yawa cewa zan kawo ka, ka yaƙe su.
18 Men på den samme dag, den dag Gog kommer over Israels land, sier Herren, Israels Gud, da skal min harme stige op i mitt åsyn.
Ga abin da zai faru a ranar. Sa’ad da Gog ya fāɗa wa ƙasar Isra’ila, fushina mai zafi zai ƙuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
19 Og i min nidkjærhet, i min brennende vrede sier jeg: Sannelig, på den samme dag skal det komme et stort jordskjelv over Israels land.
Cikin kishina da hasalata mai zafi zan furta cewa a wannan lokaci za a yi babbar girgizar ƙasa a ƙasar Isra’ila.
20 Og havets fisker og himmelens fugler og markens dyr og alt det kryp som rører sig på jorden, og alle de mennesker som bor på jorden, skal skjelve for mitt åsyn, og fjellene skal ramle og bergveggene styrte ned, og hver en mur skal falle til jorden.
Kifin teku, tsuntsayen sarari, namun jeji, kowace halitta mai rarrafe da kuma dukan mutane a duniya za su yi rawar jiki a gabana. Za a tumɓuke duwatsu, a ragargaza tsaunuka, kuma kowane bango zai fāɗi ƙasa.
21 Og jeg vil kalle på sverdet imot ham på alle mine fjell, sier Herren, Israels Gud; den enes sverd skal vendes mot den andre.
Zan kira takobi a kan Gog a dukan duwatsuna, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Kowane takobin mutum zai yi gāba da ɗan’uwansa.
22 Og jeg vil gå i rette med ham med pest og med blod, og et skyllregn og haglstener, ild og svovel vil jeg la regne ned over ham og hans skarer og over de mange folkeslag som er med ham.
Zan yi hukunci a kansa da annoba da kuma zub da jini; zan yi ruwa mai yawa da ƙanƙara da kibiritu mai cin wuta a kansa da a kan sojojinsa da kuma a kan al’ummai masu yawa da suke tare da shi.
23 Og jeg vil åpenbare min storhet og min hellighet og gi mig til kjenne for mange folks øine, og de skal kjenne at jeg er Herren.
Ta haka zan nuna girmana da kuma tsarkina, zan sanar da kaina a gaban al’ummai masu yawa. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’

< Esekiel 38 >