< Esekiel 11 >

1 Og et vær løftet mig op og førte mig til den østre port i Herrens hus, den som vender mot øst, og ved inngangen til porten så jeg fem og tyve menn og midt iblandt dem Ja'asanja, Assurs sønn, og Pelatja, Benajas sønn, som var høvdinger blandt folket.
Sa’an nan Ruhu ya ɗaga ni sama ya kawo ni ƙofar gidan Ubangiji wadda take fuskantar gabas. Can a mashigi zuwa ƙofar akwai mutum ashirin da biyar, na kuma ga a cikinsu akwai Ya’azaniya ɗan Azzur da Felatiya ɗan Benahiya, shugabannin jama’a.
2 Og Herren sa til mig: Menneskesønn! Dette er de menn som tenker ut urett og gir onde råd i denne stad,
Ubangiji ya ce mini, “Ɗan mutum, waɗannan su ne mutanen da suke ƙulla mugunta suna kuma ba da muguwa shawara a cikin wannan birni.
3 de som sier: Det blir ikke så snart tale om å bygge hus; den er gryten, og vi er kjøttet.
Suna cewa, ‘Lokaci bai yi kusa da za a gina gidaje ba? Wannan birni yana tukunyar dahuwa, mu ne kuwa naman.’
4 Derfor, spå mot dem, spå du menneskesønn!
Saboda haka yi annabci a kansu; yi annabci, ɗan mutum.”
5 Og Herrens Ånd falt på mig, og han sa til mig: Si: Så sier Herren: Således har I sagt, I av Israels hus, og de tanker som stiger op i eders ånd, dem kjenner jeg.
Sai Ruhun Ubangiji ya sauko a kaina, ya kuma faɗa mini in ce, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, haka kuke cewa, ya gidan Isra’ila, amma na san abin da yake a zuciyarku.
6 Mange er de som I har drept i denne stad; I har fylt dens gater med drepte.
Kun kashe mutane da yawa a wannan birni kuka kuma cika titunanta da gawawwaki.
7 Derfor sier Herren, Israels Gud, så: De som I har drept og latt ligge midt i staden, de er kjøttet, og den er gryten; men I skal føres ut av den.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa gawawwakin da kuka zubar a can su ne naman, wannan birni kuwa ita ce tukunya, amma zan kore ku daga cikinta.
8 I frykter for sverdet, og sverdet vil jeg la komme over eder, sier Herren, Israels Gud.
Kuna jin tsoron takobi, kuma takobi ne zan kawo muku, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
9 Jeg vil føre eder ut av den og gi eder i fremmedes hånd, og jeg vil holde dom over eder.
Zan kore ku daga birnin in miƙa ku a hannuwan baƙi in kuma azabtar da ku.
10 For sverdet skal I falle; ved Israels grense vil jeg dømme eder, og I skal kjenne at jeg er Herren.
Za ku mutu ta wurin takobi, zan kuma hukunta ku a iyakokin Isra’ila. Sa’an nan za ku san cewa ni ne Ubangiji.
11 Den skal ikke være en gryte for eder, og I skal ikke være kjøttet i den; ved Israels grense vil jeg dømme eder.
Wannan birni ba za tă zama muku tukunya ba, ba kuwa za ku zama nama a cikinta ba; zan hukunta ku a iyakokin Isra’ila.
12 Og I skal kjenne at jeg er Herren, hvis bud I ikke har fulgt, og hvis lover I ikke har holdt; men I har holdt eder efter de hedningefolks lover som bor rundt omkring eder.
Za ku kuwa san cewa ni ne Ubangiji, gama ba ku bi ƙa’idodina ba balle ku kiyaye dokokina, amma kuka bi hanyoyin al’ummai kewaye da ku.”
13 Mens jeg holdt på å spå, døde Pelatja, Benajas sønn, og jeg falt på mitt ansikt og ropte med høi røst og sa: Akk, Herre, Herre! Vil du aldeles gjøre ende på det som er igjen av Israel?
Yanzu yayinda nake yin annabci, sai Felatiya ɗan Benahiya ya mutu. Sai na fāɗi rubda ciki na kuma yi kuka da babbar murya na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka raguwar Isra’ila ƙaƙaf ne?”
14 Og Herrens ord kom til mig, og det lød så:
Sai maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
15 Menneskesønn! Dine brødre, dine brødre, dine nære frender og hele Israels hus, hele folket, er det til hvem Jerusalems innbyggere sier: Hold eder langt borte fra Herren! Oss er landet gitt til eiendom.
“Ɗan mutum,’yan’uwanka,’yan’uwanka waɗanda suke danginka na cikinka da kuma dukan gidan Isra’ila su ne waɗanda mutanen Urushalima suka ce, ‘Su ne da nisa daga Ubangiji; an ba mu wannan ƙasa ta zama mallakarmu.’
16 Derfor skal du si: Så sier Herren, Israels Gud: Da jeg lot dem fare langt bort iblandt hedningefolkene, da jeg spredte dem i landene, blev jeg en kort tid en helligdom for dem i de land de var kommet til.
“Saboda haka ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ko da yake na kore su zuwa cikin al’ummai na kuma warwatsa su cikin ƙasashe, duk da haka na zama wuri mai tsarki a gare su a ƙasashen da suka tafi.’
17 Derfor skal du si: Så sier Herren, Israels Gud: Jeg vil samle eder fra folkene og sanke eder fra de land som I er spredt i, og jeg vil gi eder Israels land.
“Saboda haka, ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan tattaro ku daga al’ummai in kuma dawo da ku daga ƙasashen da aka warwatsa ku, zan kuwa sāke mayar muku da ƙasar Isra’ila.’
18 Og når de kommer dit, da skal de få bort derfra alle de avskyeligheter og vederstyggeligheter som finnes der.
“Za su dawo gare ta su kawar da dukan mugayen siffofi da gumaka masu banƙyama.
19 Og jeg vil gi dem ett hjerte, og en ny ånd vil jeg gi i deres indre; jeg vil ta bort stenhjertet av deres kjød og gi dem et kjødhjerte,
Zan ba su zuciya ɗaya in kuma sa sabon ruhu a cikinsu; zan fid da zuciyar dutse daga gare su in kuma ba su zuciya ta nama.
20 så de skal følge mine bud og holde mine lover og gjøre efter dem; og de skal være mitt folk, og jeg vil være deres Gud.
Sa’an nan za su bi ƙa’idodina su kuma yi hankali ga kiyaye dokokina. Za su zama mutanena, ni kuwa zan zama Allahnsu.
21 Men de hvis hjerte følger deres avskyeligheter og vederstyggeligheter, deres gjerninger vil jeg la komme over deres eget hode, sier Herren, Israels Gud.
Amma game da waɗanda zukatansu suka karkata ga bin mugayen siffofi da gumakan banƙyama, zan sāka musu gwargwadon ayyukansu, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”
22 Da løftet kjerubene sine vinger, og hjulene fulgte med, og Israels Guds herlighet var ovenover dem.
Sa’an nan kerubobi, tare da da’irori kusa da su, suka buɗe fikafikansu, ɗaukakar Allah kuwa tana a bisansu.
23 Og Herrens herlighet steg op fra staden, og den blev stående på det berg som er østenfor staden.
Ɗaukakar Ubangiji ta haura daga cikin birnin ta sauka a bisa dutse gabas da shi.
24 Og et vær løftet mig op og førte mig i synet ved Guds Ånd til Kaldea, til de bortførte; og synet som jeg hadde sett, steg op fra mig.
Ruhu ya ɗaga ni sama ya kuma kawo ni ga masu zaman bauta a ƙasar Babilon cikin wahayin da Ruhun Allah ya bayar. Sa’an nan wahayin da na gani ya rabu da ni,
25 Og jeg talte til de bortførte alle de ord som Herren hadde latt mig se.
na kuwa faɗa wa masu zaman bautan dukan abin da Ubangiji ya nuna mini.

< Esekiel 11 >