< 2 Mosebok 10 >

1 Og Herren sa til Moses: Gå inn til Farao! For det er jeg som har forherdet hans hjerte og hans tjeneres hjerte, forat jeg kan gjøre disse mine tegn midt iblandt dem,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Je wurin Fir’auna, gama na riga na taurare zuciyarsa da kuma zukatan fadawansa domin in aikata waɗannan mu’ujizai nawa a tsakiyarsu,
2 og forat du skal fortelle din sønn og din sønnesønn hvad jeg har gjort mot egypterne, og hvad tegn jeg har gjort iblandt dem, så I skal kjenne at jeg er Herren.
don kuma ku gaya wa’ya’yanku da jikokinku yadda na tsananta wa Masarawa, da kuma yadda na aikata mu’ujizai a cikinsu, don ku sani ni ne Ubangiji.”
3 Så gikk Moses og Aron inn til Farao og sa til ham: Så sier Herren, hebreernes Gud: Hvor lenge vil du la være å ydmyke dig for mig? La mitt folk fare, så de kan tjene mig!
Sai Musa da Haruna suka tafi wurin Fir’auna suka ce masa, “Ga abin da Ubangiji, Allah na Ibraniyawa ya ce, ‘Har yaushe za ka ƙi ƙasƙantar da kanka a gabana? Ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
4 For dersom du nekter å la mitt folk fare, da vil jeg imorgen la gresshopper komme over ditt land.
In ka ƙi ka bari su tafi, gobe zan aiko da fāra a ƙasarka.
5 Og de skal dekke landet, så ingen kan se jorden, og de skal ete op hvert eneste grand av det som blev tilovers for eder efter haglet, og de skal avete hvert tre som vokser på eders marker.
Za su rufe fuskar ƙasar, har da ba za a iya ganin ƙasa ba. Za su cinye ɗan sauran abin da ya rage muku daga ɓarnar ƙanƙara, za su cinye dukan itatuwan da suke girma a gonakinku.
6 Og de skal fylle dine hus og alle dine tjeneres hus og alle egypternes hus, så hverken dine fedre eller dine fedres fedre har sett noget slikt fra den tid de blev til på jorden, og til denne dag. Dermed vendte han sig om og gikk ut fra Farao.
Za su cika gidajenka, da na fadawanka, da na dukan Masarawa, abin da iyayenka da kakanninka ba su taɓa gani ba, tun daga ranar da suka sami kansu a duniya, har yă zuwa yau.’” Sa’an nan Musa ya juya, ya rabu da Fir’auna.
7 Da sa Faraos tjenere til ham: Hvor lenge skal denne mann være en snare for oss? La mennene fare, så de kan tjene Herren sin Gud! Ser du ikke ennu at Egypten blir ødelagt?
Fadawan Fir’auna suka ce masa, “Har yaushe mutumin nan zai zama mana tarko? Ka bar mutanen su tafi domin su yi wa Ubangiji Allahnsu sujada. Har yanzu ba ka san cewa Masar ta lalace ba?”
8 Så blev Moses og Aron hentet tilbake til Farao, og han sa til dem: Gå avsted, tjen Herren eders Gud! Men hvem er det som skal fare?
Sa’an nan aka dawo da Musa da Haruna wurin Fir’auna. Sai ya ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji Allahnku sujada. Amma wa da wa za su tafi?”
9 Moses svarte: Vi vil fare alle, både unge og gamle; både våre sønner og våre døtre vil vi ha med, både vårt småfe og vårt storfe; for vi skal holde høitid for Herren.
Musa ya amsa, “Za mu tafi tare da ƙanananmu, da tsofaffinmu, da’ya’yanmu maza da mata, da kuma garkunanmu na shanu da tumaki, gama dole ne mu yi bikin ga Ubangiji.”
10 Da sa han til dem: Herren være med eder, så visst som jeg lar eder og eders små barn fare! Se der om I ikke har ondt i sinne!
Fir’auna ya ce, “Ubangiji ya taimaka bisa ga niyyarku, amma matanku da ƙanananku ba za su tafi ba! A fili yake kuna da niyyar mugunta.
11 Nei, ikke så! I menn kan fare og tjene Herren! For det var jo det I bad om. Dermed drev de dem ut fra Farao.
Sam! Wannan ba zai taɓa yiwu ba, sai ko maza kaɗai su tafi su yi wa Ubangiji sujada, gama abin da kuke so ke nan.” Sa’an nan aka kori Musa da Haruna daga gaban Fir’auna.
12 Da sa Herren til Moses: Rekk ut din hånd over Egyptens land, så skal gresshoppene komme inn over Egyptens land og ete op alle urter i landet, alt det haglet har levnet.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka a bisa Masar domin fāra su sauko bisa ƙasar, su ci duk abin da yake girma a gonaki, duk abin da ƙanƙara ta rage.”
13 Så rakte Moses ut sin stav over Egyptens land, og Herren lot en østenvind komme over landet hele den dag og hele natten; da det blev morgen, førte østenvinden gresshoppene med sig.
Saboda haka Musa ya miƙa sandansa bisa Masar, Ubangiji kuwa ya sa iskar gabas ta hura a kan ƙasar dukan dare da kuma dukan yini. Da safe kuwa iskar ta kawo fāra;
14 Og gresshoppene kom inn over hele Egyptens land og slo sig ned i hele Egypten i store mengder; aldri hadde det før vært en slik gresshoppesverm, og aldri vil det komme nogen slik mere.
suka mamaye ƙasar duka, suka sauka a ko’ina a ƙasar. Ba a taɓa ganin annobar fāra haka ba, ba kuwa za a ƙara ganin fāra kamar haka ba.
15 De dekket hele landet, så landet blev mørkt, og de åt op alle urter i landet og all frukt på trærne som haglet hadde levnet, og det blev intet grønt tilbake på trærne eller på markens urter i hele Egyptens land.
Suka rufe ƙasar har ta zama baƙi. Suka cinye abin da ƙanƙara ta rage, kowane tsiron da yake girma a gonaki, da dukan’ya’yan itatuwa. Babu ɗanyen abin da ya ragu a kan itatuwa ko tsire-tsire a dukan ƙasar Masar.
16 Da skyndte Farao sig og sendte bud efter Moses og Aron og sa: Jeg har syndet mot Herren eders Gud og mot eder.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna da gaggawa ya ce, “Na yi wa Ubangiji Allahnku zunubi, na kuma yi muku.
17 Men forlat mig nu min synd denne ene gang, og bed til Herren eders Gud at han bare vil avvende denne død fra mig!
Yanzu ku gafarta mini zunubina a wannan karo, ku kuma yi addu’a ga Ubangiji Allahnku yă ɗauke wannan muguwar annoba daga gare ni.”
18 Og han gikk ut igjen fra Farao og bad til Herren.
Sai Musa ya bar Fir’auna ya kuma yi addu’a ga Ubangiji.
19 Og Herren vendte vinden, så det blev en meget sterk vestenvind, og den førte gresshoppene bort og kastet dem ned i det Røde Hav; det blev ikke én gresshoppe tilbake i hele Egyptens land.
Sai Ubangiji ya canja iska zuwa iska mai ƙarfi ta yamma wadda ta ɗibi fārar zuwa Jan Teku. Babu fāran da suka rage a wani wuri a Masar.
20 Men Herren forherdet Faraos hjerte, så han ikke lot Israels barn fare.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, bai kuwa bar Isra’ilawa suka tafi ba.
21 Og Herren sa til Moses: Rekk din hånd op mot himmelen, og det skal bli mørke over Egyptens land, et mørke så tykt at en kan ta på det.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Miƙa hannunka sama domin a yi duhu a bisa Masar, duhun da za a iya taɓawa.”
22 Så rakte Moses sin hånd op mot himmelen, og det blev et tykt mørke i hele Egyptens land i tre dager.
Sai Musa ya miƙa hannunsa sama, aka kuma yi duhu baƙi ƙirin bisa dukan ƙasar Masar na kwana uku.
23 Den ene kunde ikke se den andre, og ingen torde flytte sig fra sin plass i tre dager; men hos alle Israels barn var det lyst der de bodde.
Ba wanda ya iya gani wani ko yă bar wurinsa na kwana uku. Amma dukan Isra’ilawa sun kasance da haske a inda suke zama.
24 Da kalte Farao Moses til sig og sa: Gå avsted, tjen Herren! Bare eders småfe og eders storfe skal bli tilbake; også eders små barn kan få dra med eder.
Sai Fir’auna ya aika aka kira Musa, ya kuma ce, “Ku tafi, ku yi wa Ubangiji sujada. Matanku da yaranku ma za su iya tafiya tare da ku; sai dai ku bar garkunanku na shanu da tumaki.”
25 Men Moses sa: Du må også la oss få slaktoffer og brennoffer med, så vi kan ofre til Herren vår Gud;
Amma Musa ya ce, “Dole ka bari mu kasance da hadayu, da kuma hadayu na ƙonawa waɗanda za mu miƙa wa Ubangiji Allahnmu.
26 også vår buskap må være med oss, ikke en klov må bli igjen; for det er det vi må ta av når vi skal tjene Herren vår Gud, og vi vet ikke hvad vi skal ofre til Herren før vi kommer dit.
Dole dabbobinmu ma su tafi tare da mu; ko kofato ma, ba za a bari a baya ba. A cikinsu ne za mu ɗibi abin da za mu yi wa Ubangiji Allahnmu sujada. Ba mu kuma san irin abin da za mu miƙa wa Ubangiji ba, sai mun kai can.”
27 Men Herren forherdet Faraos hjerte, så han ikke vilde la dem fare.
Amma Ubangiji ya taurare zuciyar Fir’auna, har bai yarda yă sake su ba.
28 Og Farao sa til Moses: Gå fra mig, vokt dig, kom ikke mere for mine øine! For på den dag du kommer for mine øine, skal du dø!
Fir’auna ya ce wa Musa, “Fita, ka ba ni wuri! Ka mai da hankali, kada ka ƙara bayyana a gabana, gama ran da ka sāke ganin fuskata, a ran nan za ka mutu.”
29 Moses svarte: Du har talt rett; jeg skal aldri mere komme for dine øine.
Musa ya amsa, “Madalla, kamar yadda ka faɗa, ba zan ƙara bayyana a gabanka ba.”

< 2 Mosebok 10 >