< Efeserne 6 >
1 I barn! vær lydige mot eders foreldre i Herren! for dette er rett.
Ku’ya’ya, ku yi biyayya ga iyayenku, gama ku na Ubangiji, abin da ya dace ku yi ke nan.
2 Hedre din far og din mor - dette er det første bud med løfte -
Doka ta farko wadda aka haɗa da alkawari ita ce, “Ka girmama mahaifinka da mahaifiyarka,
3 forat det må gå dig vel, og du må lenge leve i landet.
don ka zauna lafiya, ka kuma yi tsawon rai a duniya.”
4 Og I fedre! egg ikke eders barn til vrede, men fostre dem op i Herrens tukt og formaning!
Ku kuma iyaye, kada ku tsokane’ya’yanku. Ku yi musu reno mai kyau. Ku koyar da su, ku kuma gargaɗe su game da Ubangiji.
5 I tjenere! vær lydige mot eders herrer efter kjødet, med frykt og beven, i eders hjertes enfold, som mot Kristus,
Ku bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku na duniya. Ku nuna musu halin bangirma, kuna kuma yin musu biyayya cikin dukan abu, da zuciya ɗaya kamar ga Kiristi kuke yi.
6 ikke med øientjeneste, som de som vil tekkes mennesker, men som Kristi tjenere, så I gjør Guds vilje av hjertet
Ku yi aiki sosai, ba don kawai ku gamshe su sa’ad da suke kallonku ba. Da yake ku bayin Kiristi ne, ku aikata nufin Allah da dukan zuciyarku.
7 og med villig hu tjener som for Herren og ikke som for mennesker,
Ku yi aikinku da kyakkyawar niyya, sai ka ce ga Ubangiji kuke yi, ba mutane ba.
8 da I vet at hvad godt enhver gjør, det skal han få igjen av Herren, enten han er tjener eller fri.
Gama kun san cewa Ubangiji zai ba da lada ga kowa gwargwadon kowane aiki nagarin da ya yi, ko shi bawa ne, ko’yantacce.
9 Og I herrer! gjør likeså mot dem, så I lar være å true, da I vet at både deres og eders Herre er i himlene, og han gjør ikke forskjell på folk.
Ku kuma masu bayi, dole ku bi da bayinku da kyau. Ku daina ba su tsoro. Ku tuna, ku da su, Maigida ɗaya kuke da shi a sama, kuma ba ya nuna bambanci.
10 For øvrig - bli sterke i Herren og i hans veldes kraft!
A ƙarshe, bari ƙarfin ikon Ubangiji yă ba ku ƙarfi.
11 Iklæ eder Guds fulle rustning, så I kan stå eder mot djevelens listige angrep;
Ku yafa dukan kayan yaƙin da Allah yake bayarwa, don ku iya kāre kanku daga dabarun Shaiɗan.
12 for vi har ikke kamp mot blod og kjød, men mot makter, mot myndigheter, mot verdens herrer i dette mørke, mot ondskapens ånde-hær i himmelrummet. (aiōn )
Gama ba da mutane da suke nama da jini ne muke yaƙi ba. Muna yaƙi ne da ikoki, da hukumomi, da masu mulkin duhu, da kuma a ikokin da suke cikin a sararin sama. (aiōn )
13 Ta derfor Guds fulle rustning på, så I kan gjøre motstand på den onde dag og stå efter å ha overvunnet alt.
Saboda haka sai ku yafa dukan kayan yaƙi na Allah, domin sa’ad da ranar mugun nan ta zo, ku iya yin tsayin daka, bayan kuma kuka gama kome, ku dāge.
14 Så stå da omgjordet om eders lend med sannhet, og iklædd rettferdighetens brynje,
Saboda haka fa ku dāge, ku sa gaskiya tă zama ɗamararku, adalci yă zama sulkenku,
15 Og ombundet på føttene med den ferdighet til kamp som fredens evangelium gir,
shirin kai bisharar salama yă zama kamar takalmi a ƙafafunku.
16 og grip foruten alt dette troens skjold, hvormed I skal kunne slukke alle den ondes brennende piler,
Ban da waɗannan kuma, ku ɗauki garkuwar bangaskiya, wadda za ku iya kashe dukan kibiyoyin wutar Mugun nan da ita.
17 og ta frelsens hjelm og Åndens sverd, som er Guds ord,
Ku kuma ɗauki hular kwano na ceto, da takobin Ruhu, wato, Maganar Allah.
18 idet I til enhver tid beder i Ånden med all bønn og påkallelse, og er årvåkne deri med all vedholdenhet og bønn for alle de hellige,
A koyaushe ku kasance kuna addu’a da roƙo ta wurin ikon Ruhu ba fasawa. A kan wannan manufa ku zauna a faɗake da matuƙar naci, kuna yin wa dukan mutanen Ubangiji addu’a.
19 og også for mig, at det må gis mig ord når jeg oplater min munn, så jeg med frimodighet kan kunngjøre evangeliets hemmelighet,
Ku kuma yi addu’a domina, don duk sa’ad da na buɗe bakina, in sami kalmomi babu tsoro, don in sanar da asirin bishara,
20 for hvis skyld jeg er sendebud i lenker, at jeg må tale med frimodighet derom, således som jeg bør tale.
wadda nake jakadanta cikin sarƙoƙi. Ku yi addu’a don in iya yin shelarta babu tsoro, yadda ya kamata in yi.
21 Men forat også I skal kjenne min tilstand, hvorledes jeg har det, skal Tykikus fortelle eder alt, han den elskede bror og tro tjener i Herren,
Tikikus, ƙaunataccen ɗan’uwa da kuma amintaccen bawa cikin Ubangiji, zai faɗa muku kome, domin ku ma ku san yadda nake, da kuma abin da nake yi.
22 som jeg just derfor sender til eder at I skal få vite hvorledes det er med oss, og at han skal trøste eders hjerter.
Na aike shi gare ku musamman don wannan, domin ku san yadda muke, yă kuma ƙarfafa ku.
23 Fred være med brødrene, og kjærlighet med tro, fra Gud Fader og den Herre Jesus Kristus!
’Yan’uwa, salama tare da ƙauna da kuma bangaskiya daga Allah Uba da Ubangiji Yesu Kiristi su kasance tare da ku.
24 Nåden være med alle dem som elsker vår Herre Jesus Kristus i uforgjengelighet!
Alheri yă tabbata ga dukan masu ƙaunar Ubangiji Yesu Kiristi da ƙauna marar ƙarewa.