< 5 Mosebok 18 >

1 De levittiske prester, hele Levi stamme, skal ikke ha nogen del eller arv med Israel; av Herrens ildoffer og av hans arv skal de leve,
Firistocin da suke Lawiyawa, tabbatacce dukan kabilar Lawi, ba za su sami rabo ko gādo tare da Isra’ila ba. Za su yi rayuwa a kan hadayun da aka kawo wa Ubangiji da wuta ne, gama wannan ne gādonsu.
2 men nogen arv skal de ikke ha blandt sine brødre; Herren er deres arv, således som han har sagt til dem.
Ba za su sami gādo a cikin’yan’uwansu ba; Ubangiji ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
3 Og dette skal være prestenes rettighet av folket - av dem som ofrer et slaktoffer, enten av storfeet eller av småfeet: De skal gi presten bogen og kjevene og vommen.
To, ga rabon da jama’a za su ba firistoci daga hadayun da suka miƙa ta bijimi ne, ko ta tunkiya ce; sai su ba firistoci kafaɗar, kumatun, da kuma kayan cikin.
4 Førstegrøden av ditt korn, av din most og av din olje og den første ull av dine får skal du gi ham.
Za ku ba su nunan fari na hatsinku, da sabon ruwan inabinku, da manku, da kuma gashi na fari daga askin da kuka yi na tumakinku.
5 For ham har Herren din Gud utvalgt av alle dine stammer, forat han skal stå og tjene i Herrens navn, han og hans sønner, alle dager.
Gama Ubangiji Allahnku ya zaɓe su da zuriyarsu daga cikin dukan kabilanku don su tsaya su yi hidima a cikin sunan Ubangiji har abada.
6 Når en levitt kommer fra en av dine byer rundt om i Israel, hvor han opholder sig, til det sted Herren utvelger - og komme kan han om han har lyst til det -
Idan Balawe ya tashi daga wani garinku, wurin da yake da zama a Isra’ila, ya tafi a wurin da Ubangiji ya zaɓa, zai iya dawo a duk lokacin da ya ga dama.
7 og han så gjør tjeneste i Herrens, sin Guds navn, likesom alle hans brødre, de andre levitter som står der for Herrens åsyn,
Zai iya yin hidima a cikin sunan Ubangiji Allahnsa kamar dukan sauran’yan’uwansa Lawiyawa waɗanda suke hidima a can, a gaban Ubangiji.
8 så skal de alle nyte like del av gavene, bortsett fra hvad han kan ha fått ved salg av sine fedrene eiendeler.
Zai sami rabo daidai da sauran, ko da yake ya karɓi kuɗin mallaka na iyali da ya sayar.
9 Når du kommer til det land Herren din Gud gir dig, da skal du ikke ta efter disse folks vederstyggelige skikker.
Sa’ad da kuka shiga ƙasar da Ubangiji Allahnku yake ba ku, kada ku kwaikwayi hanyoyin banƙyama na al’ummai da suke can.
10 Det skal ikke finnes hos dig nogen som lar sin sønn eller datter gå gjennem ilden, eller som gir sig av med spådomskunster, eller som spår av skyene eller tyder varsler eller er en trollmann,
Kada a sami wani a cikinku da ya miƙa ɗansa, ko’yarsa a wuta, ko a sami mai duba, ko mai maita, ko mai fassara gaibi, ko mai sihiri,
11 ingen heksemester, ingen som spør en dødningemaner, ingen sannsiger, ingen som gjør spørsmål til de døde.
ko boka, ko mabiya, ko maye, ko mai sha’ani da matattu.
12 For enhver som gjør slikt, er en vederstyggelighet for Herren, og for disse vederstyggelige tings skyld er det Herren din Gud driver dem bort for dig.
Duk wanda yake yin waɗannan abubuwa, shi abin ƙyama ne ga Ubangiji, saboda waɗannan abubuwa banƙyama ne kuwa Ubangiji Allahnku ya kori waɗancan al’ummai kafin ku.
13 Ustraffelig skal du være for Herren din Gud.
Dole ku zama marasa zargi a gaban Ubangiji Allahnku.
14 For disse folk som du skal drive ut, de hører på dem som spår av skyene, og på sannsigere; men dig har Herren din Gud ikke tillatt slikt.
Al’ummai da za ku kora sukan saurari waɗannan masu maita, ko masu duba. Amma ku, Ubangiji Allahnku bai yarda muku ku yi haka ba.
15 En profet av din midte, av dine brødre, likesom mig, skal Herren din Gud opreise dig; på ham skal I høre -
Ubangiji Allahnku zai tayar muku da wani annabi kamar ni daga cikin’yan’uwanku. Dole ku saurare shi.
16 aldeles som du bad Herren din Gud om ved Horeb den dag I var samlet der og du sa: Jeg kan ikke lenger høre på Herrens, min Guds røst, og denne store ild kan jeg ikke lenger se på, for da må jeg dø.
Gama abin da kuka nema daga Ubangiji Allahnku ke nan a Horeb, a ranar taro, sa’ad da kuka ce, “Kada ka bari mu ji muryar Ubangiji Allahnmu, ko mu ƙara ganin wuta mai girma, in ba haka ba, za mu mutu.”
17 Da sa Herren til mig: De har talt vel i det de har sagt.
Sai Ubangiji ya ce mini, “Abin da suka faɗa yana da kyau.
18 En profet vil jeg opreise for dem av deres brødres midte, likesom dig, og jeg vil legge mine ord i hans munn, og han skal tale til dem alt det jeg byder ham.
Zan tayar musu da wani annabi kamar ka daga cikin’yan’uwansu; zan sa kalmomina a cikin bakinsa, zai kuma faɗa musu kome da na umarce shi.
19 Og enhver som ikke hører på mine ord, som han skal tale i mitt navn, ham vil jeg kreve til regnskap for det.
Duk wanda bai saurari kalmomina da annabin nan yake magana da sunana ba, ni kaina zan nemi hakki a kan mutumin.
20 Men den profet som i overmot drister sig til å tale noget i mitt navn som jeg ikke har befalt ham å tale, eller som taler i andre guders navn, den profet skal dø.
Amma duk annabin da ya ɗauka cewa yana magana da sunana a kan wani abin da ban umarce shi ya faɗa ba, ko kuwa wani annabin da ya yi magana da sunan waɗansu alloli, dole a kashe shi.”
21 Og om du sier ved dig selv: Hvad skal vi kjenne det ord på som Herren ikke har talt? -
Mai yiwuwa ku ce wa kanku, “Yaya za mu san cewa wannan saƙo ba Ubangiji ne ya faɗa ba?”
22 (da skal du vite: ) Når det ord profeten taler i Herrens navn, ikke skjer og ikke går i opfyllelse, da er det et ord som Herren ikke har talt; det er et ord som profeten i overmot har dristet sig til å tale, og du skal ikke være redd ham.
In abin da annabin ya furta da sunan Ubangiji bai faru ba, ko bai zama gaskiya ba, saƙo ne da Ubangiji bai faɗa ba ke nan. Wannan annabi ya yi rashin hankali ne kawai. Kada ku ji tsoronsa.

< 5 Mosebok 18 >