< Apostlenes-gjerninge 8 >
1 Og Saulus samtykte i mordet på ham. Men på den dag blev det en stor forfølgelse mot menigheten i Jerusalem, og de blev alle adspredt over Judeas og Samarias land, undtagen apostlene.
Shawulu kuwa yana can, yana tabbatar da mutuwarsa. A wannan rana wani babban tsanani ya auka wa ikkilisiyar da take a Urushalima, sai duka suka warwatsu ko’ina a Yahudiya da Samariya, manzanni kaɗai ne suka rage.
2 Men nogen gudfryktige menn begravde Stefanus og holdt en stor veklage over ham.
Mutane masu tsoron Allah suka binne Istifanus suka kuma yi makoki ƙwarai dominsa.
3 Men Saulus herjet menigheten, og gikk inn i hus efter hus og drog ut både menn og kvinner og lot dem kaste i fengsel.
Amma Shawulu ya fara hallaka ikkilisiya. Yana shiga gida-gida, yana jan maza da mata yana jefa su cikin kurkuku.
4 De som nu var adspredt, drog omkring og forkynte evangeliets ord.
Waɗanda aka wartsar suka yi ta wa’azin maganar a duk inda suka tafi.
5 Filip kom da ned til en by i Samaria og forkynte Kristus for dem.
Filibus ya gangara zuwa wani birni a Samariya ya kuma yi shelar Kiristi a can.
6 Og folket gav samdrektig akt på det som blev sagt av Filip, idet de hørte og så de tegn som han gjorde.
Sa’ad da taron mutane suka ji Filibus suka kuma ga abubuwan banmamakin da ya yi, sai duk suka mai da hankali sosai ga abin da ya faɗa.
7 For det var mange som hadde urene ånder, og de fór ut av dem med høie skrik, og mange verkbrudne og vanføre blev helbredet.
Mugayen ruhohi suka fiffito suna kururuwa daga cikin mutane da yawa, shanyayyu da guragu masu yawa suka sami warkarwa.
8 Og det blev stor glede der i byen.
Saboda haka aka yi farin ciki ƙwarai a birnin.
9 Men der var en mann ved navn Simon, som før hadde gitt sig av med trolldom i byen og satt folket i Samaria i den største forundring, for han sa sig selv å være stor;
To, akwai wani mutum mai suna Siman wanda ya kwana biyu yana yin sihiri a birnin har ya ba wa duk mutanen Samariya mamaki. Ya kuma yi taƙama cewa shi wani mai girma ne,
10 ham gav de akt på, både små og store, de sa: Han er Guds kraft som kalles den store.
dukan mutane kuwa, manyan da ƙanana, suka mai da hankali gare shi suka kuma ce, “Mutumin nan shi ne ikon Allah da aka sani a matsayin Iko Mai Girma”
11 Men de gav akt på ham fordi han i lang tid hadde satt dem i forundring ved sine trolldomskunster.
Suka bi shi domin ya daɗe yana ba su mamaki da sihirinsa.
12 Men da de nu trodde Filip, som forkynte dem evangeliet om Guds rike og Jesu Kristi navn, så lot de sig døpe, både menn og kvinner.
Amma da suka gaskata da Filibus sa’ad da yake wa’azin labari mai daɗi na mulkin Allah da kuma sunan Yesu Kiristi, sai aka yi musu baftisma, maza da mata.
13 Og Simon tok ved troen han også, og da han var blitt døpt, holdt han sig nær til Filip, og da han så de kraftige gjerninger og tegn som blev gjort, blev han ute av sig selv av forundring.
Siman kansa ya gaskata aka kuma yi masa baftisma. Ya kuma bi Filibus ko’ina, yana mamakin manyan alamu da ayyukan banmamakin da ya gani.
14 Da nu apostlene i Jerusalem fikk høre at Samaria hadde tatt imot Guds ord, sendte de Peter og Johannes til dem;
Sa’ad da manzannin da suke a Urushalima suka ji cewa Samariya ta karɓi maganar Allah, sai suka aika musu da Bitrus da Yohanna.
15 disse kom ned og bad for dem, forat de skulde få den Hellige Ånd;
Da suka iso, sai suka yi musu addu’a domin su karɓi Ruhu Mai Tsarki,
16 for Ånden var ennu ikke falt på nogen av dem, de var bare døpt til den Herre Jesu navn.
domin Ruhu Mai Tsarki bai riga ya sauka wa waninsu ba tukuna, an dai yi musu baftisma ne kawai a cikin sunan Ubangiji Yesu.
17 De la da sine hender på dem, og de fikk den Hellige Ånd.
Sa’an nan Bitrus da Yohanna suka ɗibiya hannuwansu a kansu, suka kuwa karɓi Ruhu Mai Tsarki.
18 Men da Simon så at Ånden blev gitt ved apostlenes håndspåleggelse, kom han til dem med penger og sa:
Sa’ad da Siman ya ga cewa ana ba da Ruhu ta wurin ɗibiya hannuwan manzannin, sai ya miƙa musu kuɗi,
19 Gi også mig denne makt at den som jeg legger mine hender på, må få den Hellige Ånd!
ya ce, “Ni ma ku ba ni wannan iyawa don kowa na ɗibiya wa hannuwana yă karɓi Ruhu Mai Tsarki.”
20 Men Peter sa til ham: Ditt sølv være forbannet, både det og du selv, fordi du tenkte å kjøpe Guds gave for penger!
Bitrus ya amsa ya ce, “Bari kuɗinka ya hallaka tare da kai, domin ka yi tsammani za ka iya saya kyautar Allah da kuɗi!
21 Du har ikke del eller lodd i dette ord; for ditt hjerte er ikke rett for Gud.
Ba ruwanka da wannan hidimar, domin zuciyarka ba daidai take a gaban Allah ba.
22 Omvend dig derfor fra denne din ondskap, og bed Herren om måskje ditt hjertes tanke måtte forlates dig!
Ka tuba daga wannan mugunta ka kuma yi addu’a ga Ubangiji. Wataƙila zai gafarta maka don irin tunanin da yake a zuciyarka.
23 For jeg ser at du ligger i bitterhets galle og urettferdighets bånd.
Gama na lura kana cike da ɗacin rai kana kuma daure cikin zunubi.”
24 Da svarte Simon: Bed I for mig til Herren, forat ikke noget av det I har sagt, skal komme over mig!
Sai Siman ya amsa ya ce, “Ku yi addu’a ga Ubangiji saboda ni don kada ko ɗaya daga cikin abin da ka faɗa ya same ni.”
25 Efterat de nu hadde vidnet og talt Herrens ord, vendte de tilbake til Jerusalem, og de forkynte evangeliet i mange av samaritanenes byer.
Sa’ad da suka yi shaidar suka kuma yi shelar maganar Ubangiji, sai Bitrus da Yohanna suka koma Urushalima, suna wa’azin bishara a ƙauyukan Samariya masu yawa.
26 Men en Herrens engel talte til Filip og sa: Stå op og gå mot syd, på den vei som går ned fra Jerusalem til Gasa! Denne vei er øde.
To wani mala’ikan Ubangiji ya ce wa Filibus, “Ka yi kudu zuwa hanyar, hanyar hamada, da ta gangara daga Urushalima zuwa Gaza.”
27 Han stod da op og gikk dit; og se, der var en etioper, en hoffmann, en høi embedsmann hos Kandake, etiopernes dronning, en som var satt over hele hennes skatt; han var kommet til Jerusalem for å tilbede,
Saboda haka ya kama hanya, a kan hanyarsa kuwa sai ya sadu da wani mutumin Itiyofiya, wanda yake bābā, hafsa mai muhimmanci wanda yake lura da dukan ma’ajin Kandas (wanda yake nufin “sarauniyar mutanen Itiyofiya”). Mutumin nan ya tafi Urushalima ne domin yin sujada,
28 og han var nu på hjemveien, og satt på sin vogn og leste profeten Esaias.
a kan hanyarsa ta komawa gida kuwa yana zaune bisan keken yaƙinsa yana karatun littafin annabin Ishaya.
29 Og Ånden sa til Filip: Gå bort til denne vogn og hold dig nær ved den!
Sai Ruhu ya ce wa Filibus, “Matsa wurin kekunan yaƙin nan ka yi kusa da ita.”
30 Filip løp da til, og hørte at han leste profeten Esaias, og sa: Skjønner du det du leser?
Sai Filibus ya ruga zuwa wajen keken yaƙin ya kuma ji mutumin yana karatun littafin annabin Ishaya. Filibus ya yi tambaya ya ce, “Ka fahimci abin da kake karantawa?”
31 Han svarte: Hvorledes skulde jeg vel kunne det uten at nogen veileder mig? Og han bad Filip stige op og sette sig hos ham.
Sai ya ce, “Ina fa zan iya, in ba dai wani ya fassara mini ba?” Saboda haka sai ya gayyaci Filibus yă hau yă zauna tare da shi.
32 Men det stykke av Skriften som han leste, var dette: Som et får blev han ført bort for å slaktes, og lik et lam som er stumt for den som klipper det, således åpner han ikke sin munn;
Bābān yana karanta wannan Nassin, “An ja shi kamar tunkiya zuwa mayanka, kuma kamar ɗan rago a hannun mai askin gashinsa yake shiru, haka kuwa bai buɗe bakinsa ba.
33 i hans fornedrelse blev dommen over ham borttatt, og hvem kan fortelle om hans ætt? for hans liv blir tatt bort fra jorden.
A cikin wulaƙacinsa aka hana masa gaskiya. Wa zai iya yin zancen zuriyarsa? Gama an ɗauke ransa daga duniya.”
34 Hoffmannen tok da til orde og sa til Filip: Jeg ber dig: om hvem sier profeten dette? om sig selv eller om nogen annen?
Sai bābān ya tambayi Filibus ya ce, “Ka gaya mini, ina roƙonka, annabin yana magana a kan wane ne, kansa ne, ko kuwa wani dabam?”
35 Da oplot Filip sin munn, og idet han gikk ut fra dette skriftsted, forkynte han ham evangeliet om Jesus.
Sa’an nan Filibus ya fara da wannan Nassi ɗin ya kuma faɗa masa labari mai daɗi game da Yesu.
36 Og som de drog frem på veien, kom de til et sted hvor det var vann, og hoffmannen sa: Se, her er vann; hvad er til hinder for at jeg blir døpt?
Yayinda suke cikin tafiya a kan hanya, sai suka iso wani wurin ruwa bābān nan ya ce, “Duba, ga ruwa. Me zai hana a yi mini baftisma?”
37 Og Filip sa: Tror du av hele ditt hjerte, så kan det skje. Men han svarte og sa: Jeg tror at Jesus Kristus er Guds Sønn.
38 Og han bød vognen holde, og de steg ned i vannet, både Filip og hoffmannen, og han døpte ham.
Ya kuwa ba da umarni a tsai da keken yaƙin. Sa’an nan da Filibus da bābān suka gangara zuwa cikin ruwan Filibus kuwa ya yi masa baftisma.
39 Men da de steg op av vannet, rykte Herrens Ånd Filip bort, og hoffmannen så ham ikke lenger; for han drog sin vei med glede.
Sa’ad da suka fita daga cikin ruwan, sai Ruhun Ubangiji ya fyauce Filibus, bābān kuwa bai ƙara ganinsa ba, amma ya ci gaba da tafiyarsa yana farin ciki.
40 Men Filip blev funnet i Asdod, og han drog omkring og forkynte evangeliet i alle byene, inntil han kom til Cesarea.
Filibus kuwa ya fito a Azotus, ya yi ta zagawa, yana wa’azin bishara a dukan garuruwan sai da ya kai Kaisariya.