< Apostlenes-gjerninge 24 >

1 Fem dager efter kom ypperstepresten Ananias der ned med nogen av de eldste og en taler, Tertullus; disse fremførte sin klage imot Paulus for landshøvdingen.
Bayan kwana biyar sai Ananiyas babban firist ya tafi Kaisariya tare da waɗansu daga cikin dattawa da kuma wani lauya mai suna Tertullus, suka kawo ƙararsu game da Bulus a gaban gwamna.
2 Han blev da kalt frem, og Tertullus begynte på klagen imot ham og sa:
Sa’ad da aka shigo da Bulus, sai Tertullus ya shiga kai ƙararsa a gaban Felis yana cewa, “Mun daɗe muna zaman lafiya a ƙarƙashinka, hangen nesanka kuma ya kawo gyare-gyare a wannan ƙasa.
3 Da vi har dig å takke for megen fred, og da ved din omsorg forbedringer i alle måter og på alle steder blir dette folk til del, så skjønner vi på dette, mektigste Feliks, med all takksigelse.
Ko’ina da kuma a kowace hanya, ya mafifici Felis, mun amince da wannan da godiya marar iyaka.
4 Men forat jeg ikke skal hefte dig for lenge, ber jeg dig at du efter din mildhet vil høre på nogen få ord av oss.
Amma don kada in ƙara gajiyar da kai, ina roƙonka ka yi haƙuri ka saurari ɗan taƙaitaccen jawabinmu.
5 For vi har funnet at denne mann er en pest og en opvigler blandt alle jøder rundt om i verden og en leder for nasareernes sekt;
“Mun tarar da wannan mutum fitinanne ne, yana tā-da-na-zaune-tsaye a tsakanin Yahudawa ko’ina a duniya. Shi shugaban ɗarikar Nazarawa
6 han har endog søkt å vanhellige templet. Vi grep ham derfor og vilde dømme ham efter vår lov;
har ma ya yi ƙoƙari ya ƙazantar da haikali; shi ya sa muka kama shi.
7 men Lysias, den øverste høvedsmann, kom til og tok ham med makt og vold ut av våre hender,
8 og han bød hans anklagere å komme til dig; og av ham kan du selv, om du gransker saken, få kunnskap om alt det som vi fører klagemål imot ham for.
Ta wurin bincika shi da kanka za ka gane gaskiyar game da dukan waɗannan zargin da muke kawo a kansa.”
9 Men også jødene holdt med ham og sa at så var det.
Yahudawa ma suka goyi bayan zargin, suna tabbatar cewa waɗannan abubuwa haka suke.
10 Men Paulus svarte, da landshøvdingen gav ham et tegn at han kunde tale: Da jeg vet at du i mange år har vært dommer for dette folk, fører jeg frimodig mitt forsvar,
Da gwamna ya yi masa alama yă yi magana, sai Bulus ya amsa ya ce, “Na san cewa ka yi shekaru da yawa kana mulki a wannan ƙasa; saboda haka ina farin ciki in kāre kaina.
11 eftersom du kan få visshet for at det ikke er mere enn tolv dager siden jeg drog op til Jerusalem for å tilbede.
Da sauƙi za ka iya tabbatar cewa, bai fi kwana goma sha biyu da suka wuce ne na tafi Urushalima, domin yin sujada ba.
12 Og hverken i templet eller i synagogene eller omkring i byen har de funnet at jeg talte til nogen eller opviglet folket;
Masu zargina ba su same ni ina gardama da kowa a haikali, ko kuma ina tā da hankalin jama’a a majami’u ko kuwa wani wuri dabam a cikin birni ba.
13 heller ikke kan de godtgjøre for dig disse sine klager imot mig.
Ba kuwa za su iya tabbatar maka ƙarar da suke yi yanzu a kaina ba.
14 Men det vedgår jeg for dig at efter den Guds vei som de kaller en sekt-lære, tjener jeg så mine fedres Gud at jeg tror alt det som er skrevet i loven og i profetene,
Amma na yarda cewa ina bauta wa Allah na kakanninmu a matsayin mai bin Hanyar da suke kira ɗarika. Na gaskata dukan abin da ya amince da Doka da yake kuma a rubuce cikin Annabawa,
15 og har det håp til Gud, som også disse selv venter på, at en opstandelse forestår både av rettferdige og av urettferdige.
ina kuma da irin bege ɗaya ga Allah yadda mutanen nan suke da shi, cewa akwai tashin matattu masu adalci da masu mugunta duka.
16 Derfor legger jeg selv vinn på alltid å ha en uskadd samvittighet for Gud og mennesker.
Saboda haka, ina ƙoƙari kullum in kasance da lamiri mai tsabta a gaban Allah da mutane.
17 Da nu flere år var gått, kom jeg for å føre milde gaver til mitt folk og for å ofre,
“Bayan’yan shekaru da dama da ba na nan, sai na dawo Urushalima don in kawo wa mutanena kyautai saboda matalauta in kuma yi sadaka.
18 og under dette fant de mig i templet, efterat jeg hadde renset mig, uten opløp og uten opstyr; men det var nogen jøder fra Asia,
Ni tsarkake ne sa’ad da suka same ni cikin filin haikalin ina yin haka. Babu taro tare da ni, ba kuwa ina tā da hankali ba.
19 og disse burde trede frem for dig og komme med sin klage om de hadde noget å si på mig.
Amma akwai waɗansu Yahudawa daga lardin Asiya, waɗanda ya kamata suna a nan a gabanka su kawo ƙara in suna da wani a kaina.
20 Eller la disse selv si hvad skyld de fant hos mig dengang jeg stod for rådet,
Ko kuwa waɗannan da suke a nan su faɗi laifin da suka same ni da shi sa’ad da na tsaya a gaban Majalisa,
21 uten det skulde være for dette ene ord som jeg ropte da jeg stod iblandt dem: For de dødes opstandelse står jeg idag for retten iblandt eder.
sai ko wannan abu ɗaya kaɗai da na ɗaga murya na faɗi yayinda nake tsaye a gabansu cewa, ‘A game da tashin matattu ake mini shari’a a gabanku yau.’”
22 Men Feliks utsatte saken, da han hadde nøiere kjennskap til Guds vei, og han sa: Når høvedsmannen Lysias kommer her ned, skal jeg prøve eders sak.
Sai Felis, wanda yake da cikakken sani game da Hanyar, ya ɗaga sauraron ƙarar. Ya ce, “In Lisiyas shugaban ƙungiyar soja ya iso, zan yanke muku shari’a.”
23 Og han bød høvedsmannen at han skulde holdes i varetekt og ha ro, og at ingen av hans egne skulde hindres fra å være ham til tjeneste.
Ya yi wa jarumin umarni yă tsare Bulus amma yă ba shi’yanci yă kuma bar abokansa su lura da bukatunsa.
24 Da nogen dager var gått, kom Feliks med sin hustru Drusilla, som var en jødinne, og han sendte bud efter Paulus og hørte ham om troen på Kristus.
Bayan’yan kwanaki da dama sai Felis ya zo da matarsa Durusilla, mutuniyar Yahuda. Sai ya aika a zo da Bulus ya kuma saurare shi da yake magana game da bangaskiya cikin Kiristi Yesu.
25 Men da han talte om rettferd og avhold og den kommende dom, blev Feliks forferdet og sa: Gå bort for denne gang! når jeg får god tid, vil jeg kalle dig til mig igjen.
Da Bulus ya ci gaba jawabi a kan adalci, kamunkai da kuma hukunci mai zuwa, sai Felis ya tsorata ya ce, “Yanzu kam, ya isa haka! Kana iya tafi. In na sami zarafi, zan kira ka.”
26 Han håpet også på at han skulde få penger av Paulus; derfor sendte han også oftere bud efter ham og talte med ham.
A wani fanni yana sa rai cewa Bulus zai ba shi toshiyar baki, saboda haka ya yi ta aika a kira masa Bulus yă yi magana da shi.
27 Da to år var omme, fikk Feliks til eftermann Porcius Festus, og da Feliks gjerne vilde vinne takk av jødene, lot han Paulus bundet efter sig.
Da shekaru biyu suka wuce, sai Forsiyus Festus, ya gāji Felis, amma domin Felis ya so yă biya wa Yahudawa bukata, sai ya bar Bulus a kurkuku.

< Apostlenes-gjerninge 24 >