< Apostlenes-gjerninge 20 >
1 Da nu opstyret hadde lagt sig, kalte Paulus disiplene til sig og for mante dem og bød dem farvel; så drog han avsted for å fare til Makedonia.
Sa’ad da hayaniyar ta kwanta, sai Bulus ya aika a kira almajiran, kuma bayan ya ƙarfafa su, sai ya yi bankwana ya tafi Makidoniya.
2 Efterat han nu hadde reist gjennem disse landskaper og hadde formant dem med mange ord, kom han til Grekenland;
Ya ratsa wurin yana ƙarfafa mutanen da kalmomi masu yawa, a ƙarshe kuma ya kai Giris,
3 der blev han i tre måneder, og fordi jødene lurte på ham da han var i ferd med å seile til Syria, satte han sig fore å vende tilbake gjennem Makedonia.
inda ya zauna wata uku. Da yake Yahudawa sun ƙulla masa makirci, a lokacin da yake shirin tashi cikin jirgin ruwa zuwa Suriya, sai ya yanka shawara yă koma ta Makidoniya.
4 Han hadde da følge til Asia av Sopater, Pyrrus' sønn, fra Berøa, og blandt tessalonikerne av Aristarkus og Sekundus, og av Gajus fra Derbe og Timoteus, og av Tykikus og Trofimus fra Asia.
Sai Sofater ɗan Fairrus daga Bereya, Aristarkus da Sekundus daga Tessalonika, Gayus daga Derbe, Timoti ma, da Tikikus da Turofimus daga lardin Asiya suka tafi tare da shi.
5 Disse drog i forveien og bidde på oss i Troas;
Waɗannan mutane suka sha gaba suka kuma jira mu a Toruwas.
6 men vi seilte ut fra Filippi efter de usyrede brøds dager, og kom fem dager efter til dem i Troas; der blev vi i syv dager.
Amma muka tashi daga Filibbi a jirgin ruwa bayan Bikin Burodi Marar Yisti bayan kuma kwana biyar muka sadu da sauran a Toruwas, inda muka zauna kwana bakwai.
7 På den første dag i uken var vi samlet for å bryte brødet; Paulus holdt da samtaler med dem, for han skulde fare derfra den næste dag, og han drog sin tale ut like til midt på natten.
A ranar farko ta mako muka taru wuri ɗaya don gutsuttsura burodi. Bulus ya yi wa mutane magana, don yana niyyar tashi kashegari, sai ya yi ta yin magana har tsakar dare.
8 Det var mange lamper i salen hvor vi var samlet.
Akwai fitilu da yawa a ɗakin gidan saman da muka taru.
9 Men en ung mann ved navn Eutykus satt i vinduet og var falt i dyp søvn, da Paulus talte med dem i lang tid, og i søvne styrtet han ut og falt ned fra tredje stokkverk, Og blev tatt død op.
Akwai wani saurayi zaune a taga mai suna Yitikus, wanda barci mai nauyi ya ɗauke shi yayinda Bulus yake ta tsawaita magana. Sa’ad da yake barci, sai ya fāɗi daga gidan sama a hawa ta uku aka kuma ɗauke shi matacce.
10 Men Paulus gikk ned og kastet sig over ham og favnet ham og sa: Vær ikke urolige! hans sjel er i ham.
Sai Bulus ya sauka, ya miƙe a kan saurayin ya rungume shi ya ce, “Kada ku damu, yana da rai!”
11 Så gikk han op igjen og brøt brødet og åt av det; og efterat han hadde talt lenge med dem, like til daggry, drog han avsted.
Sai ya koma ɗakin da yake a gidan sama, ya gutsuttsura burodi ya kuma ci. Bayan ya yi magana har gari ya waye, sai ya tafi.
12 De førte da gutten levende bort og blev høilig trøstet.
Mutanen suka ɗauki saurayin da rai zuwa gida suka kuma ta’azantu ƙwarai da gaske.
13 Vi hadde imens gått ombord i skibet og seilte til Assus, hvor vi skulde ta Paulus ombord; for det hadde han pålagt oss; selv vilde han gå til fots.
Mu kuwa muka ci gaba zuwa jirgin ruwan muka tashi muka nufi Assos inda za mu ɗauki Bulus. Ya yi wannan shirin don zai tafi can da ƙafa.
14 Da han nu møtte oss i Assus, tok vi ham ombord, og kom til Mitylene,
Da ya same mu a Assos, sai muka ɗauke shi a jirgin ruwan muka zo Mitilen.
15 Og derfra seilte vi videre og kom den næste dag bent ut for Kios; annen dag gikk vi innom Samos og lå over i Trogillium, og kom dagen efter til Milet.
Kashegari muka tashi cikin jirgin ruwa daga can muka zo gefen Kiyos. Kwana ɗaya bayan wannan, sai muka ƙetare zuwa Samos, kashegari kuma muka iso Miletus.
16 For Paulus hadde satt sig fore å seile Efesus forbi, så han ikke skulde bli heftet i Asia; for han hastet for å nå frem til Jerusalem til pinsedag, om det var ham mulig.
Bulus ya yanke shawara yă wuce Afisa a jirgin ruwa don kada yă ɓata lokaci a lardin Asiya, gama yana sauri yă kai Urushalima, in ya yiwu ma, a ranar Fentekos.
17 Fra Milet sendte han da bud til Efesus og kalte menighetens eldste til sig.
Daga Miletus, Bulus ya aika zuwa Afisa a kira dattawan ikkilisiya.
18 Da de var kommet til ham, sa han til dem: I vet hvordan min ferd iblandt eder var hele tiden fra den første dag jeg kom til Asia,
Da suka iso, sai ya ce musu, “Kun san irin zaman da na yi tun lokacin da na zauna da ku, daga ranar farkon da na zo cikin lardin Asiya.
19 at jeg tjente Herren med all ydmykhet og under tårer og prøvelser som jeg måtte utstå ved jødenes efterstrebelser;
Na bauta wa Ubangiji da matuƙar tawali’u har da hawaye, da gwagwarmaya iri-irin da na sha game da makircin Yahudawa.
20 hvorledes jeg ikke holdt tilbake noget av det som kunde være eder til gagn, men forkynte eder det og lærte eder det offentlig og i husene,
Kun san cewa ban yi wata-wata yin muku wa’azi game da duk abin da zai amfane ku ba amma na koyar da ku a fili da kuma gida-gida.
21 idet jeg vidnet både for jøder og for grekere om omvendelsen til Gud og troen på vår Herre Jesus Kristus.
Na yi shela ga Yahudawa da Hellenawa cewa dole su juye ga Allah cikin tuba su kuma amince da Ubangijinmu Yesu.
22 Og nu se, bundet av Ånden drar jeg til Jerusalem, og vet ikke hvad som skal møte mig der,
“Yanzu kuma Ruhu ya tilasta ni, za ni Urushalima, ba tare da sanin abin da zai faru da ni a can ba.
23 men bare at den Hellige Ånd i by efter by vidner for mig og sier at bånd og trengsler venter mig.
Na dai san cewa a kowace birni Ruhu Mai Tsarki yakan gargaɗe ni cewa kurkuku da shan wuya suna jirana.
24 Men for mig selv akter jeg ikke mitt liv et ord verdt, når jeg bare kan fullende mitt løp og den tjeneste som jeg fikk av den Herre Jesus: å vidne om Guds nådes evangelium.
Amma ni ban ɗauki raina a bakin kome ba, in dai zan iya gama tserena in kuma kammala aikin da Ubangiji Yesu ya ba ni aikin shaida bisharar alherin Allah.
25 Og nu, se, jeg vet at I aldri mere skal se mitt åsyn, alle I som jeg gikk omkring iblandt og forkynte riket.
“Yanzu na san cewa ba ko ɗaya daga cikinku wanda na zazzaga ina muku wa’azin mulkin Allah da zai sāke ganina.
26 Derfor vidner jeg for eder på denne dag at jeg er ren for alles blod;
Saboda haka, ina muku shela a yau cewa ba ni da alhakin kowa a kaina.
27 for jeg holdt ikke noget tilbake, men forkynte eder hele Guds råd.
Gama ban yi wata-wata a sanar muku dukan nufin Allah ba.
28 Så gi da akt på eder selv, og på hele den hjord som den Hellige Ånd satte eder til tilsynsmenn i, for å vokte Guds menighet, som han vant sig ved sitt eget blod!
Ku lura da kanku da dukan garken da Ruhu Mai Tsarki ya sa ku ku zama masu kula da shi. Ku zama masu kiwon ikkilisiyar Allah, wadda ya saya da jininsa.
29 Jeg vet at efter min bortgang skal det komme glupende ulver inn blandt eder, som ikke skåner hjorden;
Na san cewa bayan na tafi, mugayen kyarketai za su shigo cikinku ba za su kuwa ƙyale garken ba.
30 ja, blandt eder selv skal det fremstå menn som fører forvendt tale for å lokke disiplene efter sig.
Ko cikinku ma mutane za su taso su karkatar da gaskiya don su jawo wa kansu almajirai.
31 Våk derfor, og kom i hu at jeg i tre år ikke holdt op, hverken natt eller dag, å formane hver eneste en med tårer!
Saboda haka ku zauna a faɗake! Ku tuna cewa shekara uku, dare da rana ban taɓa fasa yin wa kowannenku gargaɗi ba, har da hawaye.
32 Og nu overgir jeg eder til Gud og hans nådes ord, han som er mektig til å opbygge eder og gi eder arvelodd blandt alle dem som er blitt helliget.
“To, yanzu na danƙa ku ga Allah da kuma ga maganar alherinsa, wadda za tă iya gina ku ta kuma ba ku gādo a cikin dukan waɗanda aka tsarkake.
33 Jeg attrådde ikke sølv eller gull eller klær av nogen;
Ban yi ƙyashin azurfa ko zinariya ko tufafin kowa ba.
34 I vet selv at det jeg selv trengte, og de som var med mig, det har disse hender arbeidet for.
Ku kanku kun san cewa hannuwan nan nawa sun biya mini bukatuna da kuma na abokan aikina.
35 I alle deler viste jeg eder at således bør vi ved strevsomt arbeid ta oss av de skrøpelige og komme den Herre Jesu ord i hu, som han selv har sagt: Det er saligere å gi enn å ta.
Cikin kowane abin da na yi, na nuna muku cewa da irin wannan aiki tuƙuru don mu taimaki marasa ƙarfi, muna tunawa da kalmomin da Ubangiji Yesu kansa ya ce, ‘Bayarwa ta fi karɓa albarka.’”
36 Da han hadde sagt dette, falt han på kne og bad sammen med dem alle.
Da ya faɗi haka, ya durƙusa tare da dukansu ya yi addu’a.
37 De brast da alle i sterk gråt, og de falt Paulus om halsen og kysset ham;
Sai dukansu suka yi kuka suka rungume shi, suka kuma yi masa sumba.
38 men mest sørget de over det ord han hadde sagt, at de aldri mere skulde se hans åsyn. Derefter fulgte de ham til skibet.
Abin da ya fi sa su baƙin ciki shi ne maganarsa da ya ce, ba za su ƙara ganin fuskarsa ba. Sai suka raka shi zuwa wajen jirgin ruwa.