< Apostlenes-gjerninge 14 >
1 I Ikonium skjedde det da at de sammen gikk inn i jødenes synagoge og talte således at en stor mengde både av jøder og av grekere kom til troen.
A lokacin da Bulus da Barnaba sun shiga garin Ikoniya suka shiga majami'an Yahudawa suka yi wa'azi yadda har mutane da yawa daga cikin Yahudawa da Hellinawa suka ba da gaskiya.
2 Men de jøder som ikke vilde tro, opegget hedningenes sinn og satte ondt i dem mot brødrene.
Amma Yahudawa da basu yi biyayya ba, suka zuga al'umman har suka yi fushi da 'yan'uwan.
3 De blev nu en lang tid der og talte frimodig i Herren, som gav sitt nådesord vidnesbyrd, idet han lot tegn og under skje ved deres hender.
Suka zauna a wurin na tsawon lokaci, suna yni maganarsu gabagadi da ikon Ubangiji, yana kuma shaidar sakon alherinsa. Ya yi wannan ta wurin alamu da al'ajibai ta hannun Bulus da Barnaba.
4 Og mengden i byen delte sig; nogen holdt med jødene, andre med apostlene.
Saboda haka mutanen garin sun rabu: wadansun su suka bi ra'ayin Yahudawa, wasu kuwa sun bi manzannin.
5 Men da nu både hedningene og jødene med deres styresmenn stormet frem og vilde mishandle dem og stene dem,
Al'umman garin da Yahudawa sun nemi jan hankali shugabanninsu, don su wulakanta Bulus da Barnaba, su jajjefe su,
6 og de merket dette, flydde de til byene i Lykaonia, Lystra og Derbe, og landet deromkring,
da suka gane haka suka gudu zuwa biranen Likoniya, Listira da Darbe, da garuruwa wadanda ke kewaye da su,
7 og forkynte evangeliet der.
a can suka yi wa'azin bishara.
8 Og i Lystra satt det en mann som ikke hadde makt i føttene, da han var vanfør fra mors liv av, og som aldri hadde kunnet gå.
A Listira akwai wani wanda ke zaune bai taba tashi da kafafunsa ba, don shi gurgu ne tun daga haihuwa.
9 Han hørte Paulus tale; denne så skarpt på ham, og da han så at han hadde tro til å bli helbredet, sa han med høi røst:
Wannan mutumin ya ji Bulus yana magana. Bulus ya kafa masa ido, ya gane mutumin na da bangaskiya da za a warkar da shi. Sai ya ce masa da murya mai karfi, “Tashi ka tsaya akan kafafunka”
10 Reis dig og stå oprett på dine føtter! Og han sprang op og gikk omkring.
Sai mutumin ya yi tsalle ya fara tafiya da kafafunsa, yana yawo.
11 Men da folket så det som Paulus hadde gjort, ropte de med høi røst på lykaonisk og sa: Gudene er blitt mennesker lik og er kommet ned til oss.
Da jama'an garin sun ga abin da Bulus ya yi, suka tada muryarsu suna cewa da Likoniyanci, “Ai alloli sun ziyarce mu daga sama, da kamanin mutane.”
12 Og de kalte Barnabas Jupiter og Paulus Merkur, fordi han var den som førte ordet.
Suna kiran Barnaba da sunan “Zafsa,” Bulus kuwa suka kira shi da sunan “Hamisa” domin shine yafi yin magana.
13 Og presten ved det Jupitertempel som var utenfor byen, kom til porten med okser og kranser og vilde ofre sammen med folket.
Sai firist din zafsa wanda dakin yin masa sujada na kofar birni; ya kawo bijimai biyu da furannin da aka saka su kamar gammo; shi da jama'arsa suna so su yi masa hadaya.
14 Men da apostlene Barnabas og Paulus hørte dette, sønderrev de sine klær og sprang ut til hopen
Amma da manzannin, wato Barnaba da Bulus, su ka ji labarin, suka yage rigunansu, suka hanzarta zuwa gun taron mutanen.
15 og ropte: I menn! hvad er det I gjør? Også vi er mennesker under samme vilkår som I, og vi forkynner eder evangeliet at I skal vende eder bort fra disse falske guder til den levende Gud, han som gjorde himmelen og jorden og havet og alt som i dem er,
Suna ta cewa, “Kuji! Ku mutane don me kuke wannan abin? Mu fa mutane ne kamarku. Mun kawo maku labari mai dadi ne, da cewa, ku rabu da abubuwa marar amfani, ku koma ga Allah mai rai, wanda ya hallici sama da kasa da teku da dukan abubuwa da ke cikinsu.
16 han som i de fremfarne tider lot alle hedningefolkene vandre sine egne veier,
A da dai ya bar mutane su yi abinda suka ga dama.
17 enda han ikke lot sig uten vidnesbyrd, idet han gjorde godt, gav eder regn og fruktbare tider fra himmelen, og mettet eders hjerter med føde og glede.
Duk da haka, bai bar kansa ba tare da shaida ba, don yana bada abubuwa masu kyau, yana ba ku ruwan sama, lokatai masu albarka, ya cika ranku da abinci da farin ciki.”
18 Og ved å si dette fikk de med nød og neppe hindret folket fra å ofre til dem.
Duk da wadannan kalmomin da kyar, Bulus da Barnaba suka iya tsayar da su daga yi masu hadaya.
19 Men det kom jøder til fra Antiokia og Ikonium og overtalte folket, og de stenet Paulus og slepte ham utenfor byen, da de trodde at han var død;
Amma wasu Yahudawa daga Antakiya da wasunsu daga Ikoniya suka rinjayi tarun jama'ar. Suka jajjefi Bulus suka ja shi zuwa wajen garin, suna ganin kamar ya mutu.
20 men mens disiplene flokket sig omkring ham, stod han op og gikk inn i byen. Den næste dag drog han med Barnabas avsted til Derbe.
Duk da haka da almajirai suka kewaye shi a tsaitsaye, sai ya tashi ya koma cikin garin. Washegari, ya tafi Darba tare Barnaba.
21 Og efterat de hadde forkynt evangeliet der i byen og gjort mange disipler, vendte de tilbake til Lystra og Ikonium og Antiokia,
Bayan sun yi wa'azin bishara a wannan birnin suka kuma sami almajirai da yawa, suka dawo Listira, da Ikoniya da Antikiya.
22 idet de styrket disiplenes sjeler og formante dem til å holde fast ved troen og sa: Vi må gå inn i Guds rike gjennem mange trengsler.
Suna karfafa zuciyar almajiran su rike bangaskiyarsu, su ci gaba da ita, suna ce masu, “Ta wurin jimrewa mai yawa zamu shiga mulkin Allah, don haka dole ne mu sha wahala.”
23 Og efterat de hadde valgt eldste for dem i hver menighet, overgav de dem med bønn og faste til den Herre som de hadde satt sin tro til.
Da suka zabar masu dattawa a kowace iklisiya, sai suka yi addu'oi da azumi, suka mika su ga Ubangiji, ga wanda suka gaskanta a gareshi.
24 Efterat de så hadde draget igjennem Pisidia, kom de til Pamfylia,
Sa'annan sun bi ta Bisidiya suka kai Bamfiliya.
25 og da de hadde talt ordet i Perge, drog de ned til Attalia,
Da suka yi maganarsu a Biriya, sun wuce zuwa har Italiya.
26 og seilte derfra til Antiokia, det sted hvor de var blitt overgitt til Guds nåde for å gjøre den gjerning som de nu hadde fullført.
Ta jirgin ruwa zuwa Antakiya, a nan ne aka mika su ga alherin Allah don aikin da suka gama a yanzu.
27 Da de nu kom dit, samlet de menigheten og fortalte hvor store ting Gud hadde gjort ved dem, og at han hadde åpnet troens dør for hedningene.
Da isowarsu Antakiya sun tara 'yan iklisiya a wuri daya, sun ba da labarin dukan abin da Allah ya yi ta wurinsu. Da yadda Ya bude kofa a wurin al'ummai ta bangaskiya.
28 Og så blev de en ikke så kort tid hos disiplene.
Sun zauna tare da almajiran na tsawon lokaci.