< 2 Samuel 23 >

1 Dette er Davids siste ord: Så sier David, Isais sønn, så sier mannen som høit var satt, Jakobs Guds salvede og Israels liflige sanger:
Waɗannan su ne kalmomin Dawuda na ƙarshe. “Abubuwan da Dawuda ɗan Yesse ya yi magana a kai, abubuwan da mutumin da Mafi Ɗaukaka ya girmama. Mutumin da Allah na Yaƙub ya zaɓa yă zama sarki, wanda kuma yake mawaƙi waƙoƙin Isra’ila.
2 Herrens Ånd taler gjennem mig, og hans ord er på min tunge.
“Ruhun Ubangiji ya yi magana ta wurina; maganarsa tana a harshena.
3 Israels Gud har talt, til mig har Israels klippe sagt: Der skal være en hersker over menneskene, en rettferdig, en hersker i gudsfrykt;
Allah na Isra’ila ya yi magana, Dutsen Isra’ila ya ce mini, ‘Sa’ad da wani ya yi mulkin mutane da adalci, sa’ad da ya yi mulki da tsoron Allah,
4 han skal være lik morgenens lys når solen går op, en morgen uten skyer, når ved solskinn og ved regn gresset spirer frem av jorden.
yana kama da hasken safiya a safiya marar girgije, kamar haske bayan ruwan sama da yakan sa ciyawa ta tsiro daga ƙasa.’
5 For har ikke mitt hus det således med Gud? En evig pakt har han jo gjort med mig, ordnet i alle deler og trygget; all min frelse og alt hvad ham behager - skulde han ikke la det gro frem?
“Ashe, gidana bai daidaita da Allah ba? Ashe, Allah bai yi madawwamiyar yarjejjeniya da ni shiryayye da ɗaurarre a kowane sashi ba? Ba zai kawo ga cikar cetona yă kuma biya duk bukatuna ba?
6 Men de onde, de er alle sammen lik torner som ryddes bort, som folk ikke tar i med hånden,
Amma za a jefar da masu mugunta duka kamar ƙayayyuwan da ba a tattara da hannu.
7 men kommer nogen nær dem, så væbner han sig med jern og spydskaft, og med ild brennes de op der hvor de står.
Duk wanda ya taɓa ƙaya yakan yi amfani da wani ƙarfe ne ko sandar māshi; akan ƙone su inda suke a zube.”
8 Dette er navnene på Davids helter: Joseb-Bassebet, takmonitten, høvedsmann for drabantene; han svang sin lanse over åtte hundre falne på én gang.
Waɗannan su ne sunayen jarumawan Dawuda. Yosheb-Basshebet, mutumin Takemon ɗaya daga cikin shugabanni Uku; ya ɗaga māshinsa ya kashe mutum ɗari takwas a lokaci guda.
9 Efter ham kom Eleasar, sønn av Dodo, sønn av Ahohi; han var en av de tre helter som var med David da de hånte filistrene som var samlet der til strid. Da så Israels menn drog sig tilbake,
Na biye da shi a matsayi cikin jarumawa ukun nan, shi ne Eleyazar ɗan Dodo, mutumin Aho. Eleyazar ya kasance tare da Dawuda sa’ad da suka fuskanci Filistiyawa waɗanda suka taru a Fas Dammim don yaƙi. Mutanen Isra’ila suka gudu,
10 reiste han sig og hugg inn på filistrene, til hans hånd blev så trett at den hang fast ved sverdet. Den dag gav Herren dem en stor seier, og da folket vendte om og fulgte ham, hadde de ikke annet å gjøre enn å plyndre de falne.
amma ya yi tsayi daka, ya bugi Filistiyawa sai da hannunsa ya gaji har ya liƙe wa māshinsa. Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara a ranar. Sauran sojoji suka komo wurin Eleyazar, don kawai su washe ganima.
11 Efter ham kom Samma, sønn av Age, hararitten. Filistrene hadde engang samlet sig til en hel flokk, og der var det et jorde som var fullt av linser. Da nu folket flyktet for filistrene,
Na biye da Agiyi a matsayi, shi ne Shamma ɗan Agi, mutumin Harar. Sa’ad da Filistiyawa suka taru a wani wurin da take gona cike da waken barewa, sai rundunar Isra’ila suka gudu daga Filistiyawa.
12 stilte han sig midt på jordet og berget det og slo filistrene, og Herren gav dem en stor seier.
Amma Shamma ya yi tsayi daka a tsakiyar gonar. Ya kāre ta, ya kuma bugi Filistiyawa, Ubangiji kuwa ya sa aka yi babban nasara.
13 Engang da det led mot høsten, drog tre av de tretti høvdinger ned og kom til David i hulen ved Adullam. Filisterflokken lå i leir i Refa'imdalen.
A lokacin girbi, uku daga cikin shugabanni talatin suka gangaro zuwa wurin Dawuda a kogon Adullam. A lokacin kuwa sojojin Filistiyawa sun kafa sansani a Kwarin Refayim.
14 David var dengang selv i borgen, og filistrenes forpost var i Betlehem.
Dawuda kuwa yana a mafaka. Wata ƙungiyar sojojin Filistiyawa kuma suna Betlehem.
15 Så kom det en brå lyst over David, og han sa: Hvem lar mig få vann å drikke av den brønn som er ved porten i Betlehem?
Dawuda ya ji ƙishirwa, sai ya ce, “Kash, da a ce wani yă samo mini ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem mana!”
16 Da brøt de tre helter sig igjennem filistrenes leir og øste vann op av brønnen ved Betlehems port og tok det med sig og kom til David med det; men han vilde ikke drikke det - han øste det ut for Herren.
Sai jarumawa ukun nan suka yi kukan ƙura, suka sheƙa a guje suka ratsa cikin sansanin Filistiyawa, suka ɗebo ruwa daga rijiyar da take kusa da bakin ƙofar Betlehem, suka kawo wa Dawuda. Amma Dawuda ya ƙi yă sha; a maimako sai ya zuba shi a gaban Ubangiji.
17 Og han sa: Det være langt fra mig, Herre, å gjøre dette! Skulde jeg drikke de menns blod som gikk avsted med fare for sitt liv? Og han vilde ikke drikke det. Dette gjorde de tre helter.
Sai ya ce, “Ubangiji yă sawwaƙe, in yi sha! Ba jinin mutanen da suka tafi a bakin ransu ba ne?” Dawuda kuwa bai sha ruwan ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
18 Så var det Abisai, bror til Joab, sønn av Seruja; han var høvedsmann for drabantene. Han svang sitt spyd over tre hundre falne; og han hadde et navn blandt de tre.
Abishai, ɗan’uwan Yowab, ɗan Zeruhiya shi shugaban Ukun nan. Ya ɗauki māshinsa ya kashe mutane ɗari uku, ta haka ya zama sananne kamar Ukun nan.
19 Fremfor de tretti var han visstnok æret og blev deres høvding; men til de tre nådde han ikke op.
Ashe, ba a girmama shi fiye da Ukun ba? Ya zama komandansu, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
20 Så var det Benaja, sønn av Jojada, som var sønn av en djerv seierrik stridsmann fra Kabse'el; han slo Moabs to løvehelter. En dag det hadde snedd, steg han ned i en brønn og slo ihjel en løve.
Benahiya, ɗan Yehohiyada mutumin Kabzeyel shi ma jarumi ne sosai, ya yi nasarori masu yawa. Ya bugi ƙwararrun jarumawan Mowab guda biyu. Ya kuma shiga rami wata ranar da ake ƙanƙara, ya kashe zaki.
21 Likeledes slo han ihjel en egypter, en kjempestor mann; egypteren hadde et spyd i hånden; men han gikk ned mot ham med sin stav og rev spydet ut av hånden på egypteren og drepte ham med hans eget spyd.
Ya kuma buge wani jibgaggen mutumin Masar. Duk da māshin da mutumin Masar yana riƙe a hannunsa, Benahiya ya kai masa hari da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannunsa, ya kuma kashe shi da māshin.
22 Dette gjorde Benaja, Jojadas sønn; han hadde et navn blandt de tre helter.
Irin nasarorin da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma jarumi ne sosai kamar jarumawan nan uku.
23 Fremfor de tretti var han æret, men til de tre nådde han ikke op. David gav ham plass blandt sine fortrolige rådgivere.
Aka fi ba shi girma fiye da talatin ɗin nan, amma ba ya cikin ukun. Dawuda ya sa shi yă zama ɗaya daga cikin masu tsaron lafiyarsa.
24 Asael, Joabs bror, var blandt de tretti; likeså Elhanan, sønn av Dodo, fra Betlehem,
Cikin talatin ɗin kuwa akwai, Asahel, ɗan’uwan Yowab, Elhanan, ɗan Dodo mutumin Betlehem,
25 haroditten Samma; haroditten Elika;
Shamma, mutumin Harod, Elika, mutumin Harod,
26 paltitten Heles; teko'itten Ira, sønn av Ikkes;
Helez, mutumin Falti, Ira, ɗan Ikkesh mutumin Tekowa,
27 anatotitten Abieser; husatitten Mebunnai;
Abiyezer, mutumin Anatot, da Mebunnai, mutumin Husha,
28 ahohitten Salmon; netofatitten Maharai;
Zalmon, mutumin Aho, da Maharai, mutumin Netofa,
29 netofatitten Heleb, sønn av Ba'ana; Ittai, sønn av Ribai, fra Gibea i Benjamins stamme;
Heleb, ɗan Ba’ana daga Netofa, Ittai, ɗan Ribai mutumin Gibeya a Benyamin,
30 piratonitten Benaja; Hiddai fra Ga'as-dalene;
Benahiya, mutumin Firaton, da Hiddai, daga rafuffukan Ga’ash,
31 arbatitten Abi-Albon; barhumitten Asmavet;
Abi-Albon, mutumin Arba, da Azmawet, mutumin Bahurim,
32 sa'albonitten Eljahba; Bene-Jasen; Jonatan;
Eliyaba, mutumin Sha’albo,’Ya’yan Yashen, Yonatan,
33 hararitten Samma; araritten Akiam, sønn av Sarar;
ɗan Shamma mutumin Harar, da Ahiyam, ɗan Sharar mutumin Harod.
34 Elifelet, sønn av Ahasbai, ma'akatittens sønn; gilonitten Eliam, sønn av Akitofel;
Elifelet, ɗan Ahasbai mutumin Ma’aka, Eliyam, ɗan Ahitofel mutumin Gilo,
35 karmelitten Hesro; arbitten Pa'arai;
Hezro, mutumin Karmel, Fa’arai, mutumin Arbi,
36 Jigal, sønn av Natan, fra Soba; gaditten Bani;
Igal, ɗan Natan mutumin Zoba, ɗan Hagiri,
37 ammonitten Selek; be'erotitten Naharai, Joabs, Serujas sønns våbensvenn;
Zelek, mutumin Ammon Naharai, mutumin Beyerot mai ɗaukan wa Yowab, ɗan Zeruhiya makamai,
38 jitritten Ira; jitritten Gared;
Ira, mutumin Itra. Gareb, mutumin Itra,
39 hetitten Uria - i alt syv og tretti.
da kuma Uriya, mutumin Hitti. Su talatin da bakwai ne duka.

< 2 Samuel 23 >