< 2 Korintierne 11 >

1 Gid I vilde tåle litt dårskap av mig! Dog, I skal tåle mig.
Ina fata za ku yi haƙuri da’yar wautata. Amma, ai, kun riga kun yi haƙuri.
2 For jeg er nidkjær for eder med Guds nidkjærhet; jeg trolovet eder jo med én mann, for å fremstille en ren jomfru for Kristus;
Ina kishinku da kishi irin na Allah. Na yi muku alkawarin aure ga miji ɗaya, Kiristi, domin in miƙa ku a gare shi kamar budurwa zalla.
3 men jeg frykter for at likesom slangen dåret Eva med sin list, således skal også eders tanker forderves og vendes bort fra den enfoldige troskap mot Kristus.
Sai dai ina tsoro kada yă zama, kamar yadda maciji ya yaudari Hawwa’u da makircinsa, ku ma a bauɗar da hankalinku daga sahihiyar biyayya amintacciya ga Kiristi.
4 For om det kommer en til eder og forkynner en annen Jesus, som vi ikke har forkynt, eller I får en annen ånd, som I ikke før har fått, eller et annet evangelium, som I ikke før har mottatt, da vil I gjerne tåle det!
Gama in wani ya zo wurinku yana wa’azin wani Yesu dabam da wanda muka yi wa’azinsa, ko kuma in kun karɓi wani ruhu dabam da wanda kuka karɓa, ko wata bishara dabam da wadda kuka karɓa, ya nuna kun yarda da su ke nan cikin sauƙinkai.
5 For jeg mener at jeg ikke i noget stykke står tilbake for de såre store apostler;
Amma a ganina waɗancan da kuke ce da su “manyan manzanni” ba su fi ni da wani abu ba.
6 men er jeg enn ulærd i tale, så er jeg det dog ikke i kunnskap; tvert imot har vi alltid lagt den for dagen for eder i alle stykker.
Mai yiwuwa ni ba horarre ba ne a magana, amma ina da sani. Mun kuwa bayyana muku wannan a sarari, ta kowace hanya.
7 Eller gjorde jeg synd da jeg ydmyket mig selv forat I skulde ophøies, idet jeg uten vederlag forkynte eder Guds evangelium?
Laifi ke nan ne na yi da na ƙasƙantar da kaina, don a ɗaga ku zuwa babban matsayi ta wurin yin muku wa’azin bisharar Allah kyauta?
8 Andre menigheter skattla jeg, idet jeg tok lønn av dem for å tjene eder, og da jeg var hos eder og kom i trang, falt jeg ikke nogen til byrde;
Na yi wa waɗansu ikkilisiyoyi ƙwace ta wurin karɓar taimako daga wurinsu, domin in yi muku hidima.
9 for det jeg manglet, det utfylte brødrene som kom fra Makedonia, og i alle måter har jeg holdt mig og vil holde mig fra å falle eder til byrde.
Sa’ad da nake tare da ku kuma nake zaman rashi, ban nawaita wa kowa ba, gama’yan’uwan da suka zo daga Makidoniya sun biya bukata. Na kiyaye kaina daga nawaita muku ta kowace hanya, zan kuma ci gaba da yin haka.
10 Så sant Kristi sannhet er i mig: Denne ros skal ikke frarøves mig i Akaias bygder!
Ba shakka, kamar yadda gaskiyar Kiristi take a cikina, babu wani a yankunan Akayya da zai iya hana yin taƙaman nan tawa.
11 Hvorfor? fordi jeg ikke elsker eder? Det vet Gud!
Don me? Don ba na ƙaunar ku ne? Allah dai ya sani ina ƙaunarku!
12 men det jeg gjør, vil jeg og herefter gjøre for å avskjære dem leiligheten som søker en leilighet, forat de skal finnes like med oss i det som de roser sig av.
Zan kuma ci gaba da yin abin da nake yi, domin in toshe kafar mutanen nan da suke fariya, suna nema mu daidaita da su.
13 For disse er falske apostler, svikefulle arbeidere, som skaper sig om til apostler for Kristus.
Gama irin waɗannan mutane manzannin ƙarya ne, ma’aikata ne masu ruɗi, sun ɓad da kamanni kamar su manzannin Kiristi ne.
14 Og det er intet under; for Satan selv skaper sig om til en lysets engel;
Ba abin mamaki ba ne, gama Shaiɗan kansa ma yana ɓad da kamanni kamar shi mala’ikan haske ne.
15 derfor er det ikke noget stort om og hans tjenere skaper sig om til rettferdighets tjenere; men deres ende skal være efter deres gjerninger.
Don haka, ba abin mamaki ba ne, in bayin Shaiɗan sun ɓad da kamanni kamar su bayin adalci ne. A ƙarshe, za a sāka musu gwargwadon ayyukansu.
16 Atter sier jeg: Ingen akte mig for en dåre! men selv om så er, da ta imot mig, om enn som en dåre, forat også jeg kan få rose mig litt!
Ina sāke faɗa, kada wani yă ɗauka ni wawa ne. Amma in kun ɗauke ni haka, to, sai ku karɓe ni kamar yadda kuke karɓan wawa, domin in ɗan in yi taƙama.
17 Det jeg her taler, det taler jeg ikke efter Herrens vilje, men som i dårskap, idet jeg roser mig så tillitsfullt.
A wannan taƙamata ba na magana yadda Ubangiji zai yi ba ne, sai dai magana ce irin ta wawa.
18 Eftersom mange roser sig på kjødelig vis, vil jeg og rose mig.
Da yake mutane da yawa suna taƙama irin ta duniya, ni ma haka zan yi.
19 For I tåler jo gjerne dårene, I som er så kloke;
Ku kam kuna da wayo sosai, har kuna jimre wa wawaye da murna!
20 I tåler det jo om nogen gjør eder til træler, om nogen opeter eder, om nogen fanger eder, om nogen ophøier sig over eder, om nogen slår eder i ansiktet!
Gaskiyar ita ce, kuna haƙuri da duk wanda ya sa ku bauta ko ya cuce ku ko ya more ku ko ya nuna muku isa ko kuma ya mare ku a fuska.
21 Med skam sier jeg det, fordi vi har vært svake; men det som nogen gjør sig stor av - jeg taler i dårskap - det gjør også jeg mig stor av.
Ina jin kunya in ce mun nuna kāsawa da ba mu yi waɗannan abubuwan ba! Abin da wani yake da ƙarfin hali yin taƙama a kai, shi ne ni ma nake ƙarfin hali yin taƙama a kai. Ina magana kamar wawa ne.
22 Er de hebreere? Jeg og. Er de israelitter? Jeg og. Er de Abrahams ætt? Jeg og.
In su Ibraniyawa ne, ni ma haka. In su Isra’ilawa ne, ni ma haka. In su zuriyar Ibrahim ne, ni ma haka.
23 Er de Kristi tjenere? Jeg taler i vanvidd: Jeg er det mere; jeg har arbeidet mere, fått flere slag, vært flere ganger i fengsel, ofte i dødsfare.
In su bayin Kiristi ne, ni na fi su ma, ina magana kamar ruɗaɗɗe ne fa! Ai, na fi su shan fama ƙwarai da gaske, da shan dauri, na sha dūka marar iyaka, na sha hatsarin mutuwa iri-iri.
24 Av jødene har jeg fem ganger fått firti slag på ett nær;
Sau biyar Yahudawa suka yi mini bulala arba’in ɗaya babu.
25 tre ganger blev jeg hudstrøket, én gang stenet, tre ganger led jeg skibbrudd, et døgn har jeg vært i dypet.
Sau uku aka bulale ni da bulalar ƙarfe, sau ɗaya aka jajjefe ni da duwatsu, sau uku jirgin ruwa ya ragargaje ina ciki, na kwana na kuma yini ruwan teku yana tafiya da ni.
26 Ofte har jeg vært på reiser, i farer i elver, i farer blandt røvere, i farer fra mitt folk, i farer fra hedninger, i farer i by, i farer i ørken, i farer på hav, i farer blandt falske brødre,
Na yi tafiye-tafiye da yawa, na sha hatsari a koguna, na sha hatsarin’yan fashi, na sha hatsari a hannun kabilarmu, na sha hatsari a hannun al’ummai, na sha hatsari a birane, na sha hatsari a jeji, na sha hatsari a teku, na kuma sha hatsarin’yan’uwa na ƙarya.
27 i strev og møie, ofte i nattevåk, i hunger og tørst, ofte i faste, i kulde og nakenhet.
Na yi fama, na shan wuya, ga kuma rashin barci sau da yawa. Na san abin da ake nufin da jin yunwa da ƙishirwa, sau da yawa kuwa na kasance da rashin abinci, na sha sanyi da zaman tsirara.
28 Foruten alt annet har jeg ennu det daglige overløp, omsorgen for alle menighetene.
Ban da waɗannan abubuwa, kowace rana ina ɗauke da nauyin kula da dukan ikkilisiyoyi.
29 Hvem er skrøpelig uten at og jeg blir skrøpelig? hvem voldes anstøt uten at det brenner i mig?
Wane ne ya rasa ƙarfi, da ban ji shi a jikina ba? Wane ne ya fāɗi cikin zunubi, da ban ji zafin wannan ba?
30 Må jeg endelig rose mig, da vil jeg rose mig av det som hører min skrøpelighet til.
In ma lalle ne in yi taƙama, to, sai in yi taƙama da abubuwan da suka nuna rashin ƙarfina.
31 Gud og vår Herre Jesu Kristi Fader, han som er velsignet i evighet, vet at jeg ikke lyver! (aiōn g165)
Allah Uban Ubangiji Yesu Kiristi, wanda yabo ta tabbata a gare shi har abada, ya san cewa ba ƙarya nake yi ba. (aiōn g165)
32 I Damaskus holdt kong Aretas' landshøvding vakt om damaskenernes by for å gripe mig,
A Damaskus, gwamnan da yake ƙarƙashin Sarki Aretas, ya sa tsare ƙofofin birnin Damaskus, don yă kama ni.
33 og gjennem en glugge på muren blev jeg firt ned i en kurv og slapp bort av hans hender.
Amma aka saukar da ni cikin kwando ta tagar katanga, na kuɓuce masa.

< 2 Korintierne 11 >