< 2 Krønikebok 36 >

1 Landets folk tok og gjorde Joakas, Josias' sønn, til konge i hans fars sted i Jerusalem.
Sai mutanen ƙasar suka ɗauki Yehoyahaz ɗan Yosiya suka naɗa shi sarki a Urushalima yă gāji mahaifinsa.
2 Joakas var tre og tyve år gammel da han blev konge, og han regjerte tre måneder i Jerusalem.
Yehoyahaz yana da shekara ashirin da uku sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku.
3 Men kongen i Egypten avsatte ham, så han ikke lenger var konge i Jerusalem, og lot landet bøte hundre talenter sølv og en talent gull.
Sarkin Masar ya tumɓuke shi a Urushalima, ya tilasta Yahuda su biya haraji talenti ɗari na azurfa da kuma talentin zinariya.
4 Så gjorde kongen i Egypten Neko hans bror Eljakim til konge over Juda og Jerusalem og forandret hans navn til Jojakim, men hans bror Joakas tok han med sig og førte ham til Egypten.
Sarkin Masar ya naɗa Eliyakim, ɗan’uwan Yehoyahaz, sarki a bisa Yahuda da kuma Urushalima, ya kuma canja sunan Eliyakim zuwa Yehohiyakim. Amma Neko ya ɗauki Yehoyahaz ɗan’uwan Eliyakim ya kai Masar.
5 Jojakim var fem og tyve år gammel da han blev konge, og han regjerte elleve år i Jerusalem. Han gjorde hvad ondt var i Herrens, hans Guds øine.
Yehohiyakim yana da shekara ashirin da biyar sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa.
6 Kongen i Babel Nebukadnesar drog op mot ham og lot ham binde med to kobberlenker for å føre ham til Babel.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya hauro ya kara da shi. Ya kama shi, ya daure da sarƙoƙin tagulla, ya kuma kai shi Babilon.
7 Nebukadnesar førte også en del av karene i Herrens hus til Babel og satte dem i sitt tempel i Babel.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kuma kwaso kayayyaki daga haikalin Ubangiji ya sa su a haikalinsa a can.
8 Hvad som ellers er å fortelle om Jojakim og om de vederstyggelige ting han gjorde sig skyldig i, og hvad ondt det ellers fantes hos ham, det er opskrevet i boken om Israels og Judas konger. Og hans sønn Jojakin blev konge i hans sted.
Sauran ayyukan mulkin Yehohiyakim, ayyukan banƙyamar da ya aikata da dukan abubuwan da aka same shi da su, suna a rubuce cikin littafin sarakunan Isra’ila da na Yahuda. Sai Yehohiyacin ɗansa ya gāje shi a matsayin sarki.
9 Jojakin var atten år gammel da han blev konge, og han regjerte tre måneder og ti dager i Jerusalem. Han gjorde hvad ondt var i Herrens øine.
Yehohiyacin yana da shekara goma sha takwas sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima wata uku da kwana goma. Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji.
10 Ved årsskiftet sendte kong Nebukadnesar krigsfolk avsted og lot ham føre til Babel, og med ham de kostbare kar i Herrens hus, og han gjorde hans bror Sedekias til konge over Juda og Jerusalem.
Da bazara, Sarki Nebukadnezzar ya aika a kawo Yehohiyacin, aka kuma kawo shi Babilon, tare da kayayyaki masu daraja daga haikalin Ubangiji, sai Sarki Nebukadnezzar ya naɗa kawunsa Zedekiya, sarki a bisa Yahuda da Urushalima.
11 Sedekias var en og tyve år gammel da han blev konge, og han regjerte elleve år i Jerusalem.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya zama sarki, ya kuma yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya.
12 Han gjorde hvad ondt var i Herrens, hans Guds øine; han ydmyket sig ikke for profeten Jeremias, hvis ord kom fra Herrens munn.
Ya yi abin da yake mugu a gaban Ubangiji Allahnsa kuma bai ƙasƙantar da kansa a gaban Irmiya annabi, wanda ya yi magana kalmar Ubangiji ba.
13 Han gjorde også oprør mot kong Nebukadnesar, som hadde latt ham sverge sig troskap ved Gud; han var hårdnakket og forherdet sitt hjerte, så han ikke vendte om til Herren, Israels Gud.
Ya tayar wa Sarki Nebukadnezzar, wanda ya sa ya yi rantsuwa da sunan Allah. Ya zama mai kunnen ƙashi da kuma taurin zuciya, bai kuwa juye ga Ubangiji, Allah na Isra’ila ba.
14 Også alle prestenes og folkets høvdinger forsyndet sig storlig og fulgte alle hedningefolkenes vederstyggelige skikker, og de gjorde Herrens hus urent, det som han hadde helliget i Jerusalem.
Bugu da ƙari, dukan shugabannin firistoci da mutane suka ƙara zama marasa aminci, suna bin dukan abubuwan banƙyama na al’ummai, suka ƙazantar da haikalin Ubangiji, wanda ya tsarkake a Urushalima.
15 Herren, deres fedres Gud, sendte sine ord til dem ved sine sendebud tidlig og sent; for han ynkedes over sitt folk og over sin bolig.
Sai Ubangiji Allah na kakanninsu, ya yi ta aika da magana gare su ta wurin’yan saƙonsa sau da sau, domin ya ji tausayi mutanensa da mazauninsa.
16 Men de spottet Guds sendebud og foraktet hans ord og hånte hans profeter, inntil Herrens vrede mot sitt folk blev så sterk at det ikke lenger var nogen lægedom.
Amma suka yi wa’yan saƙon Allah ba’a, suka rena maganarsa, suka yi wa annabawansa dariyar reni, har sai da fushin Ubangiji ya tasar a kan mutanensa babu makawa.
17 Da lot han kaldeernes konge dra op mot dem, og han drepte deres unge menn med sverdet i deres hellige hus og sparte hverken unggutter eller jomfruer eller gamle og gråhårede - alle gav han i hans hånd.
Ya bashe su ga sarkin Babiloniyawa wanda ya karkashe samarinsu da takobi a wuri mai tsarki, bai yi juyayin saurayi, ko budurwa, ko tsoho, ko gajiyayye ba. Allah ya bashe su duka ga Nebukadnezzar.
18 Alle karene i Guds hus, både store og små, og skattene i Herrens hus og kongens og hans høvdingers skatter - alt førte han til Babel.
Nebukadnezzar ya kwashe dukan kayayyaki daga haikalin Allah, babba da ƙarami, da ma’ajin haikalin Ubangiji da kuma ma’ajin sarki da na fadawansa zuwa Babilon.
19 De brente op Guds hus og rev ned Jerusalems mur; alle dets palasser brente de op med ild, og alle dets kostbare kar blev ødelagt.
Suka cinna wa haikalin Allah wuta, suka rurrushe katangar Urushalima; suka ƙone dukan fada, suka kuma lalace kome mai amfani da yake can.
20 Dem som sverdet hadde levnet, førte han som fanger til Babel, og de blev hans og hans sønners træler, til perserriket fikk makten,
Waɗanda ba a kashe ba kuwa Nebukadnezzar ya kwashe su, ya kai Babilon, suka zama bayinsa da na’ya’yansa maza har zuwa kahuwar mulkin Farisa.
21 forat Herrens ord i Jeremias' munn skulde bli opfylt - til landet hadde gjort fyldest for sine sabbatsår; alle de dager det lå øde, hadde det hvile - til sytti år var gått til ende.
Ƙasar ta more hutun Asabbacinta; a dukan lokacin zamanta kango ta huta, har sai da shekaru saba’in nan suka cika bisa ga maganar Ubangiji da Irmiya ya faɗi.
22 Så var det i perserkongen Kyros' første år; da vakte Herren, forat hans ord i Jeremias' munn skulde opfylles, slike tanker i perserkongen Kyros' ånd at han lot utrope i hele sitt rike og dessuten kunngjøre ved en skrivelse:
Don a cika maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya, a shekara farko ta Sairus sarkin Farisa, sai Ubangiji ya motsa zuciyar Sairus na Farisa don yă yi shela a dukan masarautarsa, ya kuma sa shi a rubuce cewa,
23 Så sier Kyros, kongen i Persia: Herren, himmelens Gud, har gitt mig alle jordens riker, og han har pålagt mig å bygge ham et hus i Jerusalem i Juda. Er det nogen blandt eder av alt hans folk, så være Herren hans Gud med ham, og han kan dra dit!
“Ga abin da Sairus sarkin Farisa ya ce, “‘Ubangiji Allah na sama, ya ba ni dukan mulkokin duniya, ya kuma naɗa ni in gina masa haikali a Urushalima a Yahuda. Duk wani na mutanensa a cikinku, bari yă haura yă tafi, bari kuma Ubangiji Allahnsa yă kasance tare da shi.’”

< 2 Krønikebok 36 >