< 2 Krønikebok 23 >
1 Men i det syvende år tok Jojada mot til sig og gjorde en pakt med nogen av høvedsmennene over hundre; det var Asarja, Jerohams sønn, og Ismael, Johanans sønn, og Asarja, Obeds sønn, og Ma'aseja, Adajas sønn, og Elisafat, Sikris sønn.
A shekara ta bakwai Yehohiyada ya nuna ƙarfinsa. Ya yi alkawari da shugabanni na ɗari-ɗari, Azariya ɗan Yeroham, Ishmayel ɗan Yehohanan, Azariya ɗan Obed, Ma’asehiya ɗan Adahiya, da Elishafat ɗan Zikri.
2 Så drog de omkring i Juda og samlet levittene fra alle Judas byer og Israels familiehoder; og da de kom til Jerusalem,
Suka ratsa cikin Yahuda suka tattara Lawiyawa da shugabannin iyalan Isra’ilawa daga dukan garuruwa. Sa’ad da suka zo Urushalima,
3 gjorde hele forsamlingen en pakt med kongen i Guds hus, og Jojada sa til dem: Kongens sønn skal nu være konge, således som Herren har sagt om Davids sønner.
dukan taron suka yi alkawari da sarki a haikalin Allah. Yehohiyada ya ce musu, “Ɗan sarki zai yi mulki yadda Ubangiji ya yi alkawari game da zuriyar Dawuda.
4 Hør nu hvad I skal gjøre: Den ene tredjedel av eder, de prester og levitter som tiltreder vakttjenesten på sabbaten, skal stå vakt ved dørtresklene,
Yanzu ga abin da za ku yi, shi ne, kashi ɗaya bisa uku na firistoci da Lawiyawa waɗanda za su yi aiki a Asabbaci su yi tsaro a ƙofofi,
5 og den annen tredjedel ved kongeboligen og den tredje tredjedel ved Jesod-porten, og alt folket i forgårdene ved Herrens hus.
kashi ɗaya bisa ukunku a fadan sarki, kashi ɗaya bisa uku kuma, a Ƙofar Harsashi, sai kuma dukan sauran mutane su kasance a filayen haikalin Ubangiji.
6 Men ingen må komme inn i Herrens hus uten prestene og de av levittene som gjør tjeneste; de kan gå inn, for de er hellige; men alle de andre av folket skal holde sig efter det Herren har foreskrevet.
Babu wanda zai shiga haikalin Ubangiji sai firistoci da Lawiyawan da suke a aiki; za su iya shiga domin su tsarkaku ne, amma sauran mutane za su kiyaye abin da Ubangiji ya sa su yi.
7 Levittene skal stille sig rundt omkring kongen, hver mann med våben i hånd, og den som kommer inn i huset, skal drepes; I skal være om kongen, både når han går inn, Og når han går ut.
Lawiyawa za su tsaya kewaye da sarki, kowane mutum da makamansa a hannunsa. Duk wanda ya shiga haikali sai a kashe shi. Ku tsaya kusa da sarki a duk inda ya tafi.”
8 Levittene og hele Juda gjorde aldeles som presten Jojada hadde befalt; de tok hver sine menn, både dem som tiltrådte på sabbaten, og dem som trådte av på sabbaten; for presten Jojada hadde ikke latt skiftene få hjemlov.
Lawiyawa da dukan mutanen Yahuda suka yi yadda Yehohiyada firist ya umarta. Kowanne ya ɗauki mutanensa, waɗanda suke aiki a Asabbaci da waɗanda suka gama aiki, gama Yehohiyada firist bai bar waɗansu ɓangarori ba.
9 Og presten Jojada gav høvedsmennene de spyd og små og store skjold som hadde tilhørt kong David, og som var i Guds hus.
Sa’an nan ya ba shugabannin māsu da garkuwoyi manya da ƙanana na sarki Dawuda, waɗanda suke cikin haikalin Allah.
10 Og han stilte alt folket op, hver mann med våben i hånd, fra husets høire side til husets venstre side bortimot alteret Og bortimot huset rundt omkring kongen.
Ya kuma sa dukan mutane, kowanne da makaminsa a hannunsa, kewaye da sarki, kusa da bagade da kuma haikali, daga gefen kudu zuwa gefen arewa na haikali.
11 Så førte de kongesønnen ut og satte kronen på ham og overgav ham vidnesbyrdet, og de gjorde ham til konge; og Jojada og hans sønner salvet ham og ropte: Kongen leve!
Yehohiyada da’ya’yansa maza suka fitar da ɗan sarki suka sa rawani a kansa; suka miƙa masa alkawarin, suka kuma yi shelarsa a matsayin sarki. Suka shafe shi suka kuma tā da murya suna cewa, “Ran sarki yă daɗe!”
12 Da Atalja hørte ropet fra folket som sprang frem og hyldet kongen, gikk hun inn i Herrens hus til folket.
Sa’ad da Ataliya ta ji surutun mutane suna gudu suna yabon sarki, sai ta tafi wurinsu a haikalin Ubangiji.
13 Der fikk hun se at kongen stod på sin forhøining i inngangen, og høvedsmennene og trompetblåserne stod hos ham, og hele folkemengden gledet sig og støtte i trompetene, og sangerne var der med sine instrumenter og sang Herrens lov og pris; da sønderrev Atalja sine klær og ropte: Oprør, oprør!
Ta duba, a can kuwa ga sarki, tsaye kusa da ginshiƙinsa a mashigi. Manyan sojoji da masu bushe-bushe suna kusa da sarki, dukan mutanen ƙasar kuwa suna farin ciki suna busa ƙahoni, mawaƙa kuma da kayan kiɗi suna bi da yabo. Sai Ataliya ta yage rigunanta ta yi ihu tana cewa, “Cin amanar ƙasa! Cin amanar ƙasa!”
14 Men presten Jojada lot høvedsmennene, dem som var satt over hæren, gå ut og sa til dem: Før henne ut mellem rekkene, og om nogen følger henne, så skal han drepes med sverd. For presten hadde sagt: I skal ikke drepe henne i Herrens hus.
Yehohiyada firist ya fito da shugabanni waɗanda suke shugabancin rundunar sojoji, ya ce musu, “Ku fitar da ita tsakanin sojoji ku kuma kashe duk wanda ya bi ta da takobi.” Gama firist ya ce, “Kada ku kashe ta a haikalin Ubangiji.”
15 Så gjorde de plass for henne til begge sider, og da hun kom dit hvor Hesteporten fører inn til kongens hus, drepte de henne.
Saboda haka suka kama ta yayinda take kaiwa mashigin Ƙofar Doki a filin fada, a can suka kashe ta.
16 Og Jojada gjorde en pakt mellem sig og alt folket og kongen at de skulde være Herrens folk.
Sa’an nan Yehohiyada ya yi alkawari cewa shi da mutane da kuma sarki za su zama mutanen Ubangiji.
17 Og alt folket gikk inn i Ba'als hus og rev det ned; hans altere og hans billeder knuste de, og Ba'als prest Mattan drepte de foran alterne.
Dukan mutane suka tafi haikalin Ba’al suka rurrushe shi. Suka farfashe bagadan da gumakan, suka kuma kashe Mattan firist na Ba’al a gaban bagadan.
18 Og Jojada overlot tilsynet i Herrens hus til de levittiske prester, som David hadde inndelt i skifter for tjenesten i Herrens hus, til å ofre Herrens brennoffere, som skrevet er i Mose lov, med glede og sang efter Davids forskrift.
Sa’an nan Yehohiyada ya sa aikin lura da haikalin Ubangiji a hannuwan firistoci, waɗanda suke Lawiyawan da Dawuda ya ba su aikin haikali don su miƙa hadayun ƙonawa na Ubangiji kamar yadda yake a rubuce a Dokar Musa, da farin ciki da kuma rerawa, kamar yadda Dawuda ya umarta.
19 Og han satte dørvoktere ved portene til Herrens hus, forat ingen som var blitt uren på nogen måte, skulde komme inn der.
Ya kuma sa matsaran ƙofofi a ƙofofin haikalin Ubangiji don kada wani da ba shi da tsarki yă shiga.
20 Så tok han med sig høvedsmennene over hundre og de fornemste og de mektige blandt folket og hele folkemengden og førte kongen ned fra Herrens hus, og de gikk gjennem den øvre port inn i kongens hus og satte kongen på kongetronen.
Ya ɗauki shugabannin ɗari-ɗari, manyan gari, shugabannin mutane da dukan mutanen ƙasar tare da shi ya saukar da sarki daga haikalin Ubangiji. Suka shiga fada ta Ƙofar Bisa suka kuma zaunar da sarki a kujerar sarauta,
21 Og hele folkemengden gledet sig, og byen var rolig; men Atalja hadde de drept med sverd.
sai dukan mutanen ƙasar suka yi farin ciki. Birnin kuwa ya samu zaman lafiya domin an kashe Ataliya da takobi.