< 1 Timoteus 6 >
1 Så mange som er træler under åket, skal akte sine herrer all ære verd, forat Guds navn og læren ikke skal bli spottet.
Bari duk wadanda ke bayi a karkashin karkiya su ga iyayengijinsu sun cancanci dukan daraja. Su yi haka domin kada a sabawa sunan Allah da koyarwarsa.
2 Men de som har troende herrer, skal ikke forakte dem, fordi de er brødre, men så meget heller gjøre sin tjeneste, fordi de som nyter godt av deres velgjerning, er troende og elsket. Dette skal du lære og formane til.
Bayin da suke da iyayengiji da ke masu ba da gaskiya kada su rena su saboda su 'yan'uwa ne. A maimakon haka, su yi masu hidima da kwazo. Gama iyayengijin da suke cin ribar aikinsu masu bi ne, kaunattatu kuma. Ka koyar ka kuma bayyana wadannan abubuwa.
3 Dersom nogen farer med fremmed lære og ikke holder sig til vår Herre Jesu Kristi sunde ord og den lære som hører til gudsfrykt,
Idan ya kasance wani na koyar da wani abu dabam bai kuma yarda da amintaciyar koyarwa ba, wato maganar Ubangijinmu Yesu Almasihu. Alal misali ba su amince da koyarwa da ke kai ga Allahntaka ba.
4 han er opblåst skjønt han intet forstår, men er syk for stridsspørsmål og ordkrig, som volder avind, kiv, spottord, ond mistanke,
Wannan mutum mai girman kai ne, kuma bai san komai ba. A maimakon haka, yana da matukar jayayya da gardama game da kalmomi. Wadannan kalmomi na kawo kishi, da husuma, da zage-zage, da miyagun zace-zace, da
5 stadig krangel iblandt mennesker som er fordervet i sitt sinn og har tapt sannheten, idet de akter gudsfrykten for en vei til vinning.
yawan rashin jituwa tsakanin mutane masu rubabbun hankula. Sun bijire wa gaskiya. Suna tunani cewa ibada hanya ce ta yin arziki.” Ka zame daga wadannan abubuwa.
6 Ja, gudsfrykt med nøisomhet er en stor vinning;
Yanzu bin Allah tare da dangana babbar riba ce.
7 for vi har ikke hatt noget med oss til verden; det er åpenbart at vi heller ikke kan ta noget med oss derfra;
Gama ba mu kawo komai a duniya ba, ba zamu iya fita cikinta da komai ba.
8 men når vi har føde og klær, skal vi dermed la oss nøie;
A maimakon haka, mu dangana da abinci da kuma sutura.
9 men de som vil bli rike, faller i fristelse og snare og mange dårlige og skadelige lyster, som senker menneskene ned i undergang og fortapelse.
To wadanda ke son zama mawadata su kan fada cikin jaraba, cikin tarko. Suna fadawa cikin abubuwan wauta da sha'awoyi masu illa da kowanne abu da ke sa mutane su dulmaya cikin lallacewa da hallaka.
10 For pengekjærhet er en rot til alt ondt; av lyst dertil har somme faret vill fra troen og har gjennemstunget sig selv med mange piner.
Gama son kudi shine tushen kowacce irin mugunta. Wadansu mutane garin neman kudi sun kauce daga bangaskiya, sun kuma jawowa kansu bakin ciki mai yawa.
11 Men du, Guds menneske, fly disse ting, jag efter rettferdighet, gudsfrykt, tro, kjærlighet, tålmodighet, saktmodighet!
Amma kai, mutumin Allah, ka guji wadannan abubuwa, ka bi adalci, ibada, aminci, kauna, jimiri, da tawali'u.
12 Strid troens gode strid, grip det evige liv, som du blev kalt til, du som og har avlagt den gode bekjennelse for mange vidner! (aiōnios )
Ka yi fama, fama mai kyau na bangaskiya. Ka kama rai madawami da aka kira ka gare shi. A kan wannan ne ka ba da shaida a gaban shaidu masu yawa game da abin da ke da kyau. (aiōnios )
13 Jeg byder dig for Gud, som gir alle ting liv, og for Kristus Jesus, som vidnet for Pontius Pilatus den gode bekjennelse,
Ina ba ka wannan umarni a gaban Allah wanda ke rayar da dukan abubuwa, da gaban Almasihu Yesu, wanda ya fadi abin da ke gaskiya ga Bilatus Babunti.
14 at du skal holde budet rent og ulastelig inntil vår Herre Jesu Kristi åpenbarelse,
Ka bi doka daidai, babu abin zargi har bayanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu.
15 som den Salige og alene Mektige skal vise oss i sin tid, han som er kongenes konge og herrenes herre,
Allah zai nuna bayyanuwarsa a daidai lokaci- Allah, mai albarka, Makadaicin iko, Sarkin da ke sarauta, Ubangiji mai mulki.
16 han som alene har udødelighet, som bor i et lys som ingen kan komme til, han som intet menneske har sett eller kan se; ham tilhører ære og evig makt. Amen. (aiōnios )
Shine kadai marar mutuwa, mai zama cikin hasken da ba ya kusantuwa. Ba wanda ke ganinsa, ko ya iya hango shi. Girma ya tabbata a gare shi da kuma madawwamin iko. Amin. (aiōnios )
17 Byd dem som er rike i den nuværende verden, at de ikke skal være overmodige eller sette sitt håp til den uvisse rikdom, men til Gud, som gir oss rikelig alle ting å nyte, (aiōn )
Ka gaya wa masu dukiya a cikin wannan duniya kada su daga kai, kada su sa bege ga arziki mara dawwama. Maimamakon haka, su sa begensu ga Allah wanda ke ba mu wadatar gaske domin jin dadin mu. (aiōn )
18 at de skal gjøre godt, være rike på gode gjerninger, gavmilde, godgjørende,
Gaya masu su yi nagarta su arzurta a ayyuka nagari, su zama masu bayarwa hannu sake.
19 så de legger sig op en god grunnvoll for den kommende tid, at de kan gripe det sanne liv.
Ta haka za su ajiye wa kansu harsashi mai kyau kan abin da ke zuwa domin su amshi rayuwa ta kwarai.
20 Timoteus! ta vare på det som er dig overgitt, så du vender dig bort fra det vanhellige tomme snakk og motsigelsene fra den kunnskap som falskelig kalles så,
Timoti, ka kare abin da aka ba ka. Ka nisanci maganar wauta da gardamomin da ke sabawa juna wanda ake kira ilimi a karyace.
21 som nogen bekjenner sig til, så de har faret vill i troen. Nåden være med dig!
Wadansu mutane suna shelar wadannan abubuwa, don haka sun kauce wa bangaskiyar. Bari alheri ya kasance tare da kai.