< 1 Timoteus 6 >

1 Så mange som er træler under åket, skal akte sine herrer all ære verd, forat Guds navn og læren ikke skal bli spottet.
Duk waɗanda suke ƙarƙashin bauta, ya kamata su ɗauki iyayengijinsu a kan sun cancanci girmamawa matuƙa, don kada a ɓata sunan Allah da kuma koyarwarmu.
2 Men de som har troende herrer, skal ikke forakte dem, fordi de er brødre, men så meget heller gjøre sin tjeneste, fordi de som nyter godt av deres velgjerning, er troende og elsket. Dette skal du lære og formane til.
Waɗanda suke da iyayengiji masu bi, to, kada su yi musu reni domin su’yan’uwa ne. A maimako, sai ma su fi bauta musu, saboda waɗanda suke cin moriyar hidimarsu masu bi ne, ƙaunatattu ne kuma a gare su. Waɗannan su ne abubuwan da za ka koya musu ka kuma gargaɗe su.
3 Dersom nogen farer med fremmed lære og ikke holder sig til vår Herre Jesu Kristi sunde ord og den lære som hører til gudsfrykt,
In wani yana koyarwar ƙarya bai kuma yarda da sahihiyar koyarwar Ubangijinmu Yesu Kiristi da kuma koyarwa ta tsoron Allah ba,
4 han er opblåst skjønt han intet forstår, men er syk for stridsspørsmål og ordkrig, som volder avind, kiv, spottord, ond mistanke,
yana cike da girman kai bai kuma san kome ba. Yana da mugun halin son gardama da muhawwara game da kalmomin da suke kawo kishi, rikici, maganar ƙeta, da mugayen zace-zace
5 stadig krangel iblandt mennesker som er fordervet i sitt sinn og har tapt sannheten, idet de akter gudsfrykten for en vei til vinning.
da yawan tankiya tsakanin mutane masu mugun hali, waɗanda aka raba su da gaskiya, suke kuma tsammani cewa bin Allah wata hanya ce ta samun kuɗi.
6 Ja, gudsfrykt med nøisomhet er en stor vinning;
Amma bin Allah da gamsuwa riba ce mai yawa.
7 for vi har ikke hatt noget med oss til verden; det er åpenbart at vi heller ikke kan ta noget med oss derfra;
Gama ba mu zo duniya da kome ba, ba kuwa za mu fita daga cikinta da kome ba.
8 men når vi har føde og klær, skal vi dermed la oss nøie;
In dai muna da abinci da sutura, ai, sai mu gamsu da su.
9 men de som vil bli rike, faller i fristelse og snare og mange dårlige og skadelige lyster, som senker menneskene ned i undergang og fortapelse.
Mutanen da suke son yin arziki sukan fāɗi cikin jarraba, su fāɗa a tarko, suna mugayen sha’awace-sha’awace iri-iri na wauta da cutarwa, irin waɗanda suke dulmuyar da mutane, su kai ga lalacewa da hallaka.
10 For pengekjærhet er en rot til alt ondt; av lyst dertil har somme faret vill fra troen og har gjennemstunget sig selv med mange piner.
Gama son kuɗi shi ne tushen kowane irin mugun abu. Waɗansu mutane, don tsananin son kuɗi, sun bauɗe daga bangaskiya suka kuma jawo wa kansu da baƙin ciki iri-iri.
11 Men du, Guds menneske, fly disse ting, jag efter rettferdighet, gudsfrykt, tro, kjærlighet, tålmodighet, saktmodighet!
Amma kai, mutumin Allah, ka guji duk wannan, ka kuma nemi adalci, tsoron Allah, bangaskiya, ƙauna, jimrewa da kuma hankali.
12 Strid troens gode strid, grip det evige liv, som du blev kalt til, du som og har avlagt den gode bekjennelse for mange vidner! (aiōnios g166)
Ka yi fama, kyakkyawar fama ta bangaskiya. Ka riƙi rai madawwamin nan, wanda aka kira saboda shi, sa’ad da ka yi kyakkyawar shaida a gaban shaidu masu yawa. (aiōnios g166)
13 Jeg byder dig for Gud, som gir alle ting liv, og for Kristus Jesus, som vidnet for Pontius Pilatus den gode bekjennelse,
Na umarce ka, a gaban Allah mai ba da rai ga kome, da kuma Kiristi Yesu wanda yayinda yake ba da shaida a gaban Buntus Bilatus ya yi kyakkyawar shaida,
14 at du skal holde budet rent og ulastelig inntil vår Herre Jesu Kristi åpenbarelse,
ka kiyaye wannan umarni ba tare da wani aibi ko abin zargi ba har yă bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Kiristi,
15 som den Salige og alene Mektige skal vise oss i sin tid, han som er kongenes konge og herrenes herre,
wanda Allah zai kawo a daidai lokaci, Allah, mai albarka wanda yake kaɗai Mai Mulki, Sarkin sarakuna da Ubangijin iyayengiji,
16 han som alene har udødelighet, som bor i et lys som ingen kan komme til, han som intet menneske har sett eller kan se; ham tilhører ære og evig makt. Amen. (aiōnios g166)
wanda shi kaɗai ne marar mutuwa wanda kuma yake zaune cikin hasken da ba ya kusatuwa, wanda babu wanda ya taɓa gani ko zai iya gani. A gare shi girma da iko su tabbata har abada. Amin. (aiōnios g166)
17 Byd dem som er rike i den nuværende verden, at de ikke skal være overmodige eller sette sitt håp til den uvisse rikdom, men til Gud, som gir oss rikelig alle ting å nyte, (aiōn g165)
Ka umarci waɗanda suke da arziki a wannan duniya kada su ɗaga kai ko su sa begensu a kan dukiyar da ba ta da tabbaci, sai dai su sa begensu ga Allah, wanda yake ba mu kome a yalwace don jin daɗinmu. (aiōn g165)
18 at de skal gjøre godt, være rike på gode gjerninger, gavmilde, godgjørende,
Ka umarce su su yi nagarta, su wadatu cikin ayyuka nagari, su kuma zama masu bayarwa hannu sake da kuma masu niyyar yin taimako.
19 så de legger sig op en god grunnvoll for den kommende tid, at de kan gripe det sanne liv.
Ta haka za su ajiye wa kansu dukiya a matsayin tushen mai ƙarfi don tsara mai zuwa, don su riƙi rai wanda yake na tabbatacce.
20 Timoteus! ta vare på det som er dig overgitt, så du vender dig bort fra det vanhellige tomme snakk og motsigelsene fra den kunnskap som falskelig kalles så,
Timoti, ka lura da abin da aka danƙa maka amana. Ka yi nesa da masu maganganun rashin tsoron Allah da kuma yawan mūsu da ake ƙarya, ake ce da shi ilimi,
21 som nogen bekjenner sig til, så de har faret vill i troen. Nåden være med dig!
wanda waɗansu suka furta kuma ta yin haka suka bauɗe daga bangaskiya. Alheri yă kasance tare da ku.

< 1 Timoteus 6 >