< 1 Peters 2 >

1 Avlegg derfor all ondskap og all svik og også hykleri og avind og all baktalelse,
Saboda haka, ku rabu da kowace ƙeta da dukan ruɗu, munafunci, kishi, da kuma kowace irin ɓata suna.
2 og lenges som nyfødte barn efter den åndelige uforfalskede melk, forat I kan vokse ved den til frelse,
Kamar sababbin jarirai, ku yi marmarin madara zalla ta ruhaniya, domin ta wurinta za ku yi girma cikin cetonku,
3 så sant I har smakt at Herren er god!
yanzu da kuka ɗanɗana alherin Ubangiji.
4 Kom til ham, den levende sten, som vel blev forkastet av mennesker, men er utvalgt og kostelig for Gud,
Da kuka zo gare shi, rayayyen Dutse, da mutane suka ƙi amma Allah ya zaɓa, kuma mai daraja a gare shi
5 og bli også I opbygget som levende stener til et åndelig hus, et hellig presteskap til å frembære åndelige offer, som tekkes Gud ved Jesus Kristus.
ku ma, a matsayinku na duwatsu masu rai, ana gina ku ga zama gidan ruhaniya don ku zama tsattsarkar ƙungiyar firistoci, kuna miƙa hadayun ruhaniya, abin karɓa ga Allah ta wurin Yesu Kiristi.
6 For det heter i Skriften: Se, jeg legger i Sion en hjørnesten, utvalgt, kostelig, og den som tror på ham, skal ingenlunde bli til skamme.
Gama a cikin Nassi an ce, “Ga shi, na kafa dutse a Sihiyona, zaɓaɓɓen dutse na kusurwar gini mai daraja, wanda kuma ya dogara gare shi ba zai taɓa kunyata ba.”
7 Eder altså som tror, hører æren til; men for de vantro er den sten som bygningsmennene forkastet, blitt til hjørnesten og snublesten og anstøtsklippe,
A gare ku da kuka gaskata, wannan dutse mai daraja ne. Amma ga waɗanda ba su gaskata ba, “Dutsen da magina suka ƙi ya zama dutsen kusurwar gini,
8 disse som snubler ved sin vantro mot ordet; dertil er de og satt.
kuma, “Dutse ne da yake sa mutane tuntuɓe kuma fā ne da yake sa su fāɗi.” Sun yi tuntuɓe domin sun ƙi su yi biyayya da saƙon, wanda kuma yake abin da aka ƙaddara musu.
9 Men I er en utvalgt ætt, et kongelig presteskap, et hellig folk, et folk til eiendom, forat I skal forkynne hans dyder som kalte eder fra mørke til sitt underfulle lys,
Amma ku zaɓaɓɓu ne, ƙungiyar firistocin babban Sarki, al’umma mai tsarki, jama’a mallakar Allah, domin ku shaida yabon shi wanda ya kira ku daga cikin duhu zuwa haskensa mai banmamaki.
10 I som fordum ikke var et folk, men nu er Guds folk, I som ikke hadde funnet miskunn, men nu har fått miskunn.
Dā ku ba mutane ba ne, amma yanzu ku mutanen Allah ne; Dā ba ku karɓi jinƙai ba, amma yanzu kun karɓi jinƙai.
11 I elskede! jeg formaner eder som fremmede og utlendinger at I avholder eder fra de kjødelige lyster, som strider mot sjelen,
Abokaina ƙaunatattu, ina roƙonku, a matsayin bare da kuma baƙi a duniya, ku rabu da sha’awace-sha’awacen zunubin da suke yaƙi da ranku.
12 så I lar eders ferd iblandt hedningene være god, forat de mens de baktaler eder som ugjerningsmenn, kan se eders gode gjerninger og for deres skyld prise Gud på besøkelsens dag.
Ku yi irin rayuwa mai kyau a cikin masu bautar gumaka, yadda ko da sun zarge ku da yin laifi, za su iya ganin ayyukanku nagari, su ɗaukaka Allah a ranar da zai ziyarce mu.
13 Vær derfor all menneskelig ordning undergitt for Herrens skyld, enten det nu er kongen som den høieste,
Saboda Ubangiji, ku yi biyayya ga kowace hukumar da aka kafa cikin mutane, ko ga sarki, a matsayi wanda ya fi iko,
14 eller landshøvdinger som utsendinger fra ham til straff for ugjerningsmenn, men til ros for dem som gjør godt.
ko ga gwamnoni, waɗanda ya aika domin su hukunta masu laifi su kuma yabi masu aikata abin da yake daidai.
15 For således er det Guds vilje at I ved å gjøre det gode skal målbinde de uvettige menneskers vankundighet,
Gama nufin Allah ne cewa ta wurin yin nagarta za ku toshe jahilcin marasa azanci.
16 som frie, og ikke som de som har friheten til ondskaps skjul, men som Guds tjenere.
Ku yi rayuwa kamar mutanen da aka’yantar, sai dai kada ku yi amfani da’yancinku a matsayin hujjar aikata mugunta; ku yi rayuwa kamar bayin Allah.
17 Ær alle, elsk broderskapet, frykt Gud, ær kongen!
Ku nuna ladabin da ya dace ga kowa. Ku ƙaunaci’yan’uwantakar masu bi, ku ji tsoron Allah, ku girmama sarki.
18 I tjenere! vær eders herrer undergitt i all frykt, ikke bare de gode og rimelige, men også de vrange!
Bayi, ku yi biyayya ga iyayengijinku da matuƙar ladabi, ba kawai ga waɗanda suke da kirki da masu sauƙinkai ba, amma har ga masu zafin rai ma.
19 For dette finner nåde, om nogen av samvittighet for Gud finner sig i sorger når han lider urettferdig.
Gama abin yabo ne in mutum ya yi haƙuri cikin zafin wahalar rashin adalci saboda yana sane da Allah.
20 For hvad ros er det om I er tålmodige når I synder og får straff for det? Men om I er tålmodige når I gjør det gode og allikevel må lide, da finner dette nåde hos Gud.
Amma ina abin taƙama in kuka sha duka saboda kun yi laifi kuka kuma jimre? Sai dai in kuka sha wahala saboda yin nagari kuka kuma jimre, abin yabo ne a gaban Allah.
21 For dertil blev I og kalt, fordi også Kristus led for eder og efterlot eder et eksempel, forat I skal følge efter i hans fotspor,
Ga wannan ne aka kira ku, domin Kiristi ya sha wahala dominku, ya bar muku gurbin da ya kamata ku bi.
22 han som ikke gjorde synd, og i hvis munn det ikke blev funnet svik,
“Bai taɓa yin laifi ba sam, ba a kuma sami ƙarya a bakinsa ba.”
23 han som ikke skjelte igjen når han blev utskjelt, ikke truet når han led, men overlot det til ham som dømmer rettferdig;
Sa’ad da suka zazzage shi, bai rama ba; sa’ad da ya sha wahala, bai yi barazana ba. A maimakon haka, ya miƙa kansa ga wanda yake shari’ar adalci.
24 han som bar våre synder på sitt legeme op på treet, forat vi skal avdø fra våre synder og leve for rettferdigheten, han ved hvis sår I er lægt.
Shi kansa ya ɗauki zunubanmu a jikinsa a kan itace, domin mu mutu ga zunubai mu kuma rayu ga adalci; ta wurin raunukansa ne kuka sami warkarwa.
25 For I var villfarende som får, men har nu omvendt eder til eders sjelers hyrde og tilsynsmann.
Gama dā kuna kama da tumakin da suka ɓace, amma yanzu kun dawo ga Makiyayi da kuma Mai lura da rayukanku.

< 1 Peters 2 >