< 1 Kongebok 5 >
1 Kongen i Tyrus Hiram sendte sine tjenere til Salomo, da han hadde fått høre at han var blitt salvet til konge i sin fars sted; for Hiram hadde alltid vært en venn av David.
Sa’ad da Hiram sarkin Taya ya ji an shafe Solomon sarki yă gāji mahaifinsa Dawuda, sai ya aika da jakadunsa zuwa wurin Solomon, gama shi da Dawuda abokai ne sosai dukan kwanakinsa.
2 Og Salomo sendte bud til Hiram og lot si:
Solomon ya mayar da wannan saƙo ga Hiram ya ce,
3 Du vet at min far David ikke kunde bygge et hus for Herrens, sin Guds navn for de krigers skyld hvormed de hadde omringet ham, inntil Herren la dem under hans føtter.
“Ka san cewa saboda yaƙe-yaƙen da abokan gāba suka yi da mahaifina a kowane gefe, ya sa bai iya gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahnsa ba, sai da Ubangiji ya sa abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
4 Men nu har Herren min Gud gitt mig ro rundt omkring; det finnes ingen motstandere, og ingen ulykker truer.
Amma yanzu Ubangiji Allahna ya ba ni hutu a kowane gefe, babu kuma gāba ko masifa.
5 Derfor tenker jeg nu på å bygge et hus for Herrens, min Guds navn, således som Herren sa da han talte således til min far David: Din sønn, som jeg vil sette på din trone i ditt sted, han skal bygge huset for mitt navn.
Ina niyya in gina haikali domin Sunan Ubangiji Allahna, yadda Ubangiji ya faɗa wa mahaifina Dawuda, sa’ad da ya ce, ‘Ɗanka wanda zai gāje ka, shi zai gina haikali domin Sunana.’
6 Så byd nu at de skal hugge sedrer for mig på Libanon, så skal mine tjenere være med dine tjenere, og lønnen til dine tjenere vil jeg gi dig efter som du selv bestemmer; for du vet at det ikke finnes nogen blandt oss som skjønner sig så godt på å hugge trær som sidonierne.
“Don haka, ka ba da umarni a yanka mini itatuwan al’ul na ƙasar Lebanon. Ma’aikatana za su haɗa hannu da ma’aikatanka, ni kuwa zan biya ka albashin ma’aikatanka kamar yadda ka faɗa. Gama ka san cewa babu wani a cikinmu da ya iya yanka itacen katako kamar Sidoniyawa.”
7 Da Hiram mottok dette budskap fra Salomo, blev han meget glad, og han sa: Lovet være Herren idag, som har gitt David en vis sønn og satt ham over dette store folk!
Da Hiram ya ji saƙon Solomon, sai ya ji daɗi ƙwarai, ya kuma ce, “Yabo ga Ubangiji a yau, gama ya ba wa Dawuda ɗa mai hikima yă yi mulki a bisa wannan al’umma mai girma.”
8 Og Hiram sendte bud til Salomo og lot si: Jeg har mottatt det budskap du har sendt mig; jeg skal i alle måter gjøre som du ønsker med sedertrærne og cypresstrærne.
Sai Hiram ya aike wa Solomon da kalmomin nan, “Na sami saƙon da ka aika mini, zan kuma yi duk abin da kake so ta wurin tanada katakan al’ul da na fir.
9 Mine tjenere skal føre dem fra Libanon ned til havet, og jeg vil la dem legge i flåter på havet og føre til det sted du vil sende mig bud om, og la dem ta fra hverandre der, og så lar du dem hente. Men så må du gjøre det jeg ønsker, og la mig få fødevarer til mitt hus.
Ma’aikatana za su gangara da su daga Lebanon zuwa bakin teku. Zan sa a ɗaɗɗaura su su bi ruwan teku daga Lebanon zuwa bakin Bahar Rum da za ka nuna mini. A can zan kunce maka su, sa’an nan ka kwashe. Kai kuma za ka biya bukatata ta wurin tanadin abinci wa gidana.”
10 Og Hiram lot Salomo få sedertrær og cypresstrær, så meget som han ønsket.
A haka Hiram ya ci gaba da aika wa Solomon al’ul da kuma fir da yake bukata.
11 Og Salomo gav Hiram tyve tusen kor hvete til føde for hans hus og tyve kor olje av støtte oliven; så meget gav Salomo Hiram år efter år.
Solomon kuma ya ba wa Hiram mudu gari dubu ashirin na alkama a matsayin abinci domin gidansa, ya ƙara da garwa dubu ashirin na tataccen man zaitun. Solomon ya ci gaba da yin haka ga Hiram, shekara-shekara.
12 Herren gav Salomo visdom, således som han hadde lovt ham; og det var fred mellem Hiram og Salomo, og de gjorde en pakt med hverandre.
Ubangiji ya ba wa Solomon hikima, kamar yadda ya yi masa alkawari. Dangantakar zaman lafiya ta kasance tsakanin Hiram da Solomon, su biyun suka yi yarjejjeniya.
13 Og kong Salomo uttok pliktarbeidere av hele Israel, og pliktarbeiderne var tretti tusen mann.
Sarki Solomon ya ɗebi ma’aikata daga dukan Isra’ila, su dubu talatin.
14 Dem sendte han skiftevis til Libanon, ti tusen om måneden; en måned var de på Libanon og to måneder hjemme. Adoniram hadde opsyn med pliktarbeiderne.
Ya riƙa aika su dubu goma-goma zuwa Lebanon kowane wata, saboda su yi wata ɗaya a Lebanon, watanni biyu kuma a gida. Adoniram ne ya lura da aikin gandun.
15 Salomo hadde sytti tusen bærere og åtti tusen stenhuggere på fjellene,
Solomon ya kasance da’yan ɗauko guda dubu saba’in da masu yankan duwatsu guda dubu tamanin a cikin tuddai,
16 foruten arbeidsformennene, som var tre tusen og tre hundre i tallet; de rådet over de folk som utførte arbeidet.
ya kuma kasance da shugabanni dubu uku da ɗari uku waɗanda suke lura da aikin, su ne kuma suke bi da ma’aikatan.
17 Og kongen bød at de skulde bryte store og kostbare stener, så grunnvollen til huset kunde legges ned med huggen sten.
Bisa ga umarnin sarki sai suka cire manyan duwatsu masu kyau don a tanada tushen duwatsun da aka gyara domin haikalin daga wurin haƙar duwatsun.
18 Og Salomos bygningsmenn og Hirams bygningsmenn og giblittene hugg dem til og gjorde i stand både stokkene og stenene som huset skulde bygges av.
Gwanayen Solomon da na Hiram da kuma mutanen Gebal, su suka yanka, suka kuma shirya katako da dutse don ginin haikali.