< 1 Kongebok 2 >

1 a det led mot den tid at David skulde dø, bød han sin sønn Salomo og sa:
Da lokacin mutuwar Dawuda ya yi kusa, sai ya gargaɗe Solomon ɗansa, ya ce,
2 Jeg går all jordens vei; så vær du sterk og vær en mann!
“Ina gab da bin hanyar da kowa a duniya zai bi. Saboda haka ka yi ƙarfin hali, ka nuna kanka namiji,
3 Og ta vare på hvad Herren din Gud vil ha varetatt, så du vandrer på hans veier og holder hans forskrifter, hans bud og hans lover og hans vidnesbyrd, som der er skrevet i Mose lov, så du kan gå viselig frem i alt det du gjør og i alt du gir dig i ferd med,
ka kiyaye abin da Ubangiji Allahnka yake bukata. Yi tafiya a hanyoyinsa, ka kiyaye ƙa’idodi, da umarnai, da dokoki, da kuma farillansa, kamar yadda suke a rubuce a Dokar Musa, don ka yi nasara a cikin kome da za ka yi, da kuma inda za ka tafi.
4 forat Herren må opfylle sitt ord, det som han talte om mig da han sa: Dersom dine sønner akter vel på sin vei så de vandrer for mitt åsyn i sannhet, av hele sitt hjerte og av hele sin sjel, så skal det - sa han - aldri fattes en mann av din ætt på Israels trone.
Ubangiji kuwa zai kiyaye alkawarinsa gare ni da ya ce, ‘In zuriyarka suka lura da yadda suke rayuwa, in kuma suka yi tafiya da aminci a gabana da dukan zuciyarsu, da kuma dukan ransu, ba za ka kāsa samun mutum a kujerar sarautar Isra’ila ba.’
5 Du vet og hvad Joab, Serujas sønn, har gjort mot mig - hvad han gjorde mot begge Israels hærførere, Abner, Ners sønn, og Amasa, Jeters sønn, hvorledes han drepte dem og utøste blod i fredstid som om det var krig, og lot det komme blod på beltet han hadde om sine lender, og på skoene han hadde på sine føtter, som om det var krig.
“Yanzu fa, kai kanka ka san abin da Yowab ɗan Zeruhiya ya yi mini. Abin da ya yi wa shugabanni biyun nan na mayaƙan Isra’ila, wato, Abner ɗan Ner, da Amasa ɗan Yeter. Ya kashe su, ya kuma zub da jininsu a lokacin salama sai ka ce a fage yaƙi, da wannan jini ya yi ɗamara a gindinsa, ya kuma sa takalma a ƙafafunsa.
6 Gjør derfor som din visdom lærer dig, og la ikke hans grå hår fare med fred ned i dødsriket. (Sheol h7585)
Ka yi da shi gwargwadon hikimarka, amma kada ka bari yă gangara kabari da furfura cikin salama. (Sheol h7585)
7 Men gileaditten Barsillais sønner skal du gjøre vel imot, og de skal være blandt dem som eter ved ditt bord; for på samme måte kom de mig i møte da jeg flyktet for din bror Absalom.
“Amma ka yi alheri ga’ya’yan Barzillai mutumin Gileyad, ka sa su kasance a cikin waɗanda suke ci a teburinka. Sun goyi bayana sa’ad da nake gudu daga ɗan’uwanka Absalom.
8 Så har du og benjaminitten Sime'i fra Bahurim, sønn av Gera, hos dig; det var han som bante mig så stygt den dag jeg drog til Mahana'im; men siden kom han mig i møte ned til Jordan, og jeg tilsvor ham ved Herren og sa: Jeg skal ikke la dig dø for sverdet.
“Ka tuna, akwai kuma Shimeyi ɗan Gera, mutumin Benyamin daga Bahurim, wanda ya yi ta yin mini muguwar la’ana a ranar da na tafi Mahanayim. Sa’ad da ya gangara ya same ni a Urdun, na rantse masa da sunan Ubangiji na ce, ‘Ba zan kashe ka da takobi ba.’
9 Men la ham nu ikke bli ustraffet! Du er en vis mann og vil nok vite hvad du skal gjøre med ham, så du lar hans grå hår fare med blod ned i dødsriket. (Sheol h7585)
Amma yanzu, kada ka ɗauke shi marar laifi. Kai mutum ne mai hikima; za ka san abin da za ka yi da shi. Ka kawo furfuransa zuwa kabari da jini.” (Sheol h7585)
10 Så la David sig til hvile hos sine fedre og blev begravet i Davids stad.
Sa’an nan Dawuda ya huta tare da kakanninsa. Sai aka binne shi a Birnin Dawuda.
11 Den tid David var konge over Israel, var firti år; i Hebron regjerte han i syv år og i Jerusalem i tre og tretti år.
Ya yi sarauta shekaru arba’in a bisa Isra’ila. Wato, shekaru bakwai a Hebron da kuma talatin da uku a Urushalima.
12 Og Salomo satt på sin far Davids trone, og hans kongedømme blev meget sterkt.
Solomon kuwa ya zauna a kan kujerar sarautar mahaifinsa Dawuda, mulkinsa kuwa ya kahu sosai.
13 Men Adonja, Haggits sønn, kom inn til Batseba, Salomos mor. Hun spurte: Kommer du med fred? Han svarte: Ja!
To, sai Adoniya, ɗan Haggit ya tafi wurin Batsheba mahaifiyar Solomon. Ita kuwa ta tambaye shi ta ce, “Lafiya?” Ya amsa ya ce, “I, lafiya.”
14 Så sa han: Jeg har noget å tale med dig om. Hun sa: Tal!
Sa’an nan ya ƙara da cewa, “Ina da ɗan wani abin da zan faɗa miki.” Ta ce, “Faɗa.”
15 Da sa han: Du vet at riket var mitt, og at hele Israel hadde festet sine øine på mig og ventet at jeg skulde bli konge; men kongedømmet gikk fra mig og over til min bror; det var Herren som gav ham det.
Sai ya ce, “Kamar yadda kika sani, mulkin nan nawa ne. Dukan Isra’ila suna ɗaukana a matsayin sarki. Amma abubuwa suka canja, sai mulkin ya koma ga ɗan’uwana; gama ya zo masa daga Ubangiji ne.
16 Og nu er det en ting jeg vil be dig om; du må ikke vise mig bort! Hun svarte: Tal!
Yanzu ina da roƙo guda da zan yi gare ki. Kada ki hana mini.” Ta ce, “Sai ka faɗa.”
17 Da sa han: Bed kong Salomo - for dig viser han ikke bort - at han vil gi mig Abisag fra Sunem til hustru!
Sai ya ci gaba, “In kin yarda, ki yi magana da Sarki Solomon, gama ba zai ƙi jinki ba, ki ce yă ba ni yarinyan nan, Abishag, mutuniyar Shunam, tă zama matata.”
18 Batseba svarte: Godt, jeg skal tale til kongen for dig.
Batsheba ta ce, “Da kyau, zan yi magana da sarki dominka.”
19 Så gikk Batseba inn til kong Salomo for å tale til ham for Adonja, og kongen stod op og gikk henne i møte og bøide sig dypt for henne. Derefter satte han sig på sin trone, og det blev satt frem en trone for kongens mor, og hun satte sig ved hans høire side.
Sai Batsheba ta tafi wurin Sarki Solomon don tă yi masa magana a kan Adoniya. Sarki ya miƙe tsaye don yă sadu da ita, ya rusuna mata, ya kuma zauna a kujerar sarautarsa. Ya sa aka kawo wa mahaifiyar sarki kujerar sarauta, ta kuwa zauna a gefen damansa.
20 Hun sa: Det er bare en eneste liten ting jeg vil be dig om; du må ikke vise mig bort! Kongen svarte: Kom du med din bønn, mor! Jeg skal ikke vise dig bort.
Ta ce, “Ina da ɗan roƙon da zan nema ka yi mini. Ina fata ba za ka hana ni ba.” Sai sarki ya amsa ya ce, “Mahaifiyata, sai ki faɗa in ji, ba zan hana miki ba.”
21 Da sa hun: La din bror Adonja få Abisag fra Sunem til hustru!
Saboda haka sai ta ce, “Ka sa a ba wa ɗan’uwanka Adoniya, Abishag mutuniyar Shunam tă zama matarsa.”
22 Men kong Salomo svarte sin mor: Hvorfor ber du om Abisag fra Sunem for Adonja? Bed da like så godt om riket for ham - han er jo min eldre bror - ja både for ham og for presten Abjatar og for Joab, Serujas sønn!
Sarki Solomon ya amsa wa mahaifiyarsa ya ce, “Me ya sa kika roƙar wa Adoniya Abishag mutuniyar Shunam kawai? Ki ma sa a ba shi mulkin mana. Ai, shi yayana ne. I, ki roƙa dominsa, da domin Abiyatar firist, da kuma domin Yowab ɗan Zeruhiya mana!”
23 Og kong Salomo svor ved Herren og sa: Herren la det gå mig ille både nu og siden om ikke dette ord skal koste Adonja hans liv.
Sai Sarki Solomon ya rantse da sunan Ubangiji ya ce, “Bari Allah yă yi mini hukunci mai tsanani, idan ban sa Adoniya ya biya wannan roƙo da ransa ba!
24 Så sant Herren lever, han som har gitt mig denne makt og satt mig på min far Davids trone, og som har bygget mig et hus, således som han har talt: Adonja skal late livet idag!
Yanzu kuwa, muddin Ubangiji yana a raye, shi wanda ya kafa ni sosai a kan kujerar sarautar mahaifina Dawuda, ya kuma kafa mini mulki kamar yadda ya yi alkawari; za a kashe Adoniya yau!”
25 Så sendte kong Salomo Benaja, Jojadas sønn, avsted, og han hugg ham ned så han døde.
Saboda haka Sarki Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada yă kashe Adoniya; ya kuwa kashe shi.
26 Og til presten Abjatar sa kongen: Gå til Anatot, til din gård, for du har fortjent døden; men idag vil jeg ikke la dig dø, fordi du har båret Herrens, Israels Guds ark foran min far David, og fordi du har lidt med i alt hvad min far måtte lide.
Ga Abiyatar firist kuwa sarki ya ce, “Tafi gonarka a Anatot. Ka cancanci ka mutu, amma ba zan kashe ka yanzu ba, domin ka ɗauki akwatin alkawarin Ubangiji Mai Iko Duka a gaban mahaifina Dawuda, ka kuma sha wahala tare mahaifina.”
27 Så drev Salomo Abjatar bort og lot ham ikke få være Herrens prest lenger, forat Herrens ord skulde bli opfylt, det som han hadde talt mot Elis hus i Silo.
Saboda haka Solomon ya cire Abiyatar daga aikin firist na Ubangiji, ya cika maganar da Ubangiji ya yi a Shilo game da gidan Eli.
28 Da Joab fikk høre om dette, flyktet han til Herrens telt og grep fatt i alterets horn; for Joab hadde holdt med Adonja, om han enn ikke hadde holdt med Absalom.
Sa’ad da labarin ya kai wurin Yowab, wanda ya haɗa kai da Adoniya, ko da yake bai haɗa kai da Absalom ba, sai ya gudu zuwa tentin Ubangiji, ya kama ƙahonin bagade ya riƙe.
29 Men det blev meldt kong Salomo at Joab var flyktet til Herrens telt og stod ved alteret. Da sendte Salomo Benaja, Jojadas sønn, avsted og sa: Gå og hugg ham ned!
Aka faɗa wa Sarki Solomon cewa Yowab ya gudu zuwa tentin Ubangiji, yana kuma kusa da bagade. Sai Solomon ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada ya ce, “Je ka kashe shi!”
30 Da Benaja kom til Herrens telt, sa han til ham: Så sier kongen: Gå bort herfra! Men han sa: Nei, her vil jeg dø. Og Benaja bar bud tilbake til kongen og sa: Så sa Joab, og så svarte han mig.
Sai Benahiya ya shiga tentin Ubangiji ya ce wa Yowab, “Sarki ya ce, ‘Ka fita!’” Amma Yowab ya amsa ya ce, “A’a, a nan zan mutu.” Sai Benahiya ya ce wa sarki, “Ga yadda Yowab ya amsa mini.”
31 Da sa kongen til ham: Gjør som han sier, og hugg ham ned og begrav ham! Så frir du mig og min fars hus fra det uskyldige blod som Joab har utøst.
Sai sarki ya umarci Benahiya ya ce, “Yi kamar yadda ya faɗa. Ka kashe shi, ka kuma binne shi, ka wanke ni da gidan mahaifina daga laifin jini marasa laifin da Yowab ya zubar.
32 Og Herren skal la hans blod komme tilbake på hans hode fordi han hugg ned to menn som var rettferdigere og bedre enn han, og drepte dem med sverdet, så min far David ikke visste om det, Abner, Ners sønn, Israels hærfører, og Amasa, Jeters sønn, Judas hærfører.
Ubangiji zai sāka masa saboda jinin da ya zubar, domin ba da sanin mahaifina Dawuda ne ya fāɗa wa mutum biyun nan da takobi ba. Dukansu biyu, Abner ɗan Ner, shugaban mayaƙan Isra’ila, da Amasa ɗan Yeter, shugaban mayaƙan Yahuda, mutane ne mafi kyau da kuma mafi adalci fiye da shi.
33 Deres blod skal komme tilbake på Joabs hode og på hans efterkommeres hode til evig tid; men David og hans efterkommere og hans hus og hans trone skal Herren gi lykke til evig tid.
Bari alhakin jininsu yă koma a kan Yowab da kuma zuriyarsa har abada. Amma bari salamar Ubangiji tă kasance a kan Dawuda da zuriyarsa, da gidansa, da kuma mulkinsa, har abada.”
34 Så gikk Benaja, Jojadas sønn, op og hugg ham ned og drepte ham, og han blev begravet ved sitt hus i ørkenen.
Sai Benahiya ɗan Yehohiyada ya haura ya bugi Yowab, ya kashe shi, ya kuwa binne shi a gidansa a ƙauye.
35 Og kongen satte Benaja, Jojadas sønn, over hæren i hans sted, og presten Sadok satte kongen i Abjatars sted.
Sai sarki ya sa Benahiya ɗan Yehohiyada ya zama shugaba a bisa mayaƙa a matsayin Yowab, ya kuma sa Zadok firist a wurin Abiyatar.
36 Så sendte kongen bud efter Sime'i og sa til ham: Bygg dig et hus i Jerusalem og bo der og gå ikke ut derfra, hverken til det ene sted eller det annet.
Sa’an nan sarki ya aika aka kawo Shimeyi, ya kuma ce masa, “Ka gina wa kanka gida a nan a Urushalima, ka zauna a ciki, kada ka kuskura ka tafi wani wuri.
37 For det skal du vite for visst, at den dag du går ut og går over bekken Kidron, skal du dø; ditt blod skal komme på ditt eget hode.
Gama ran da ka fita, ka haye Kwarin Kidron, ka tabbata za ka mutu, alhakin jininka kuwa zai koma kanka.”
38 Da sa Sime'i til kongen: Det er rett det du sier; som min herre kongen har sagt, så skal din tjener gjøre. Og Sime'i blev boende i Jerusalem en lang tid.
Shimeyi ya amsa wa sarki ya ce, “Abin da ka faɗa yana da kyau. Bawanka zai yi kamar yadda ranka yă daɗe sarki, ya faɗa.” Shimeyi kuwa ya yi zama a Urushalima na dogon lokaci.
39 Men da tre år var gått, hendte det at to av Sime'is tjenere rømte til kongen i Gat, Akis. sønn av Ma'aka. og det blev meldt Sime'i: Dine tjenere er i Gat.
Amma bayan shekaru uku, biyu daga cikin bayin Shimeyi suka gudu zuwa wurin Akish ɗan Ma’aka, sarkin Gat. Aka faɗa wa Shimeyi cewa, “Bayinka suna a Gat.”
40 Da gjorde Sime'i sig rede og salte sitt asen og drog til Akis i Gat for å lete efter sine tjenere; Sime'i drog da dit og hadde sine tjenere med sig tilbake fra Gat.
Da jin haka, sai ya tashi ya shimfiɗa wa jakinsa abin zama, ya hau, ya tafi Gat wurin Akish domin neman bayinsa. Shimeyi kuwa ya dawo da su gida daga Gat.
41 Men Salomo fikk vite at Sime'i var reist fra Jerusalem til Gat og var kommet tilbake.
Da aka faɗa wa Solomon cewa Shimeyi ya bar Urushalima zuwa Gat, har ya dawo.
42 Da sendte kongen bud efter Sime'i og sa til ham: Har jeg ikke svoret ved Herren og høitidelig sagt dig: Det skal du vite for visst at den dag du går ut og drar til noget annet sted, skal du dø? Og du svarte: Det er rett det du sier; jeg har hørt det.
Sai sarki ya aika a kawo Shimeyi, ya ce masa, “Ban sa ka rantse da sunan Ubangiji, na kuma ja maka kunne cewa, ‘A ranar da ka kuskura ka bar nan ka tafi wani wuri, ka tabbata za ka mutu ba’? A lokacin ka ce mini, ‘Abin da ka faɗa yana da kyau. Zan kuwa kiyaye.’
43 Hvorfor har du da ikke holdt dig efter den ed som var svoret ved Herren, og det bud jeg gav dig?
To, me ya sa ba ka kiyaye rantsuwar da ka yi ga Ubangiji, ka kuma yi biyayya da umarnin da na ba ka ba?”
44 Og kongen sa til Sime'i: Du kjenner selv alt det onde som ditt hjerte vet om at du har gjort mot min far David, og Herren lar nu din ondskap komme tilbake på ditt eget hode.
Sarki ya ce wa Shimeyi, “Ka sani a zuciyarka dukan muguntar da ka yi wa mahaifina Dawuda. Yanzu Ubangiji zai sāka maka saboda muguntarka.
45 Men kong Salomo skal være velsignet, og Davids trone skal stå fast for Herrens åsyn til evig tid.
Amma za a yi wa Sarki Solomon albarka, sarautar Dawuda kuma za tă kasance a tsare a gaban Ubangiji har abada.”
46 Så gav kongen Benaja, Jojadas sønn, sin befaling, og han gikk ut og hugg ham ned så han døde. Og kongedømmet lå trygt og fast i Salomos hånd.
Sai sarki ya umarci Benahiya ɗan Yehohiyada, yă fita, yă bugi Shimeyi, yă kashe shi. Ya kuwa kashe shi. Mulki kuwa ya kahu sosai a hannun Solomon.

< 1 Kongebok 2 >