< 1 Kongebok 12 >

1 Rehabeam drog til Sikem; for hele Israel var kommet til Sikem for å gjøre ham til konge.
Rehobowam ya tafi Shekem, gama dukan Isra’ila sun je can don su naɗa shi sarki.
2 Da Jeroboam, Nebats sønn, hørte det - han var ennu i Egypten; han var flyktet dit for kong Salomo og bodde således nu i Egypten,
Sa’ad da Yerobowam ɗan Nebat ya ji labari (gama har yanzu yana a Masar, inda ya gudu daga Sarki Solomon), sai ya dawo daga Masar.
3 men de sendte bud dit og kalte ham hjem - da kom han og hele Israels menighet og talte til Rehabeam og sa:
Saboda haka mutane suka aika Yerobowam yă zo, sai shi da dukan taron Isra’ila suka tafi wurin Rehobowam, suka ce masa,
4 Din far gjorde vårt åk tungt; men lett nu du den hårde tjeneste og det tunge åk som din far la på oss! Så vil vi tjene dig.
“Mahaifinka ya sa mana kaya mai nauyin gaske, amma yanzu ka sassauta wannan aiki mai zafi, da kuma kaya masu nauyin da ya sa a kanmu, mu kuwa za mu bauta maka.”
5 Han svarte dem: Gå bort og vent i tre dager og kom så hit til mig igjen! Så gikk folket bort.
Rehobowam ya amsa, “Ku tafi, bayan kwana uku, ku dawo.” Sai mutane suka watse.
6 Og kong Rehabeam rådførte sig med de gamle, som hadde gjort tjeneste hos hans far Salomo, mens han ennu levde, og han sa: Hvad råder I mig til å svare dette folk?
Sai Sarki Rehobowam ya nemi shawarar dattawa waɗanda suka yi wa mahaifinsa Solomon, hidima a kwanakinsa. Ya ce, “Wace shawara ce za ku ba ni don in amsa wa waɗannan mutane?”
7 De svarte ham: Hvis du idag lyder dette folk og retter dig efter dem og gir dem gode ord til svar, så vil de være dine tjenere for alle tider.
Suka amsa, “In a yau za ka zama bawan waɗannan mutane, ka kuma yi musu hidima, ka ba su amsa mai kyau, kullum za su kasance bayinka.”
8 Men han aktet ikke på det råd som de gamle hadde gitt ham, men rådførte sig med de unge, som var vokset op sammen med ham, og som nu var i hans tjeneste.
Amma Rehobowam ya ƙi shawarar da dattawan suka ba shi, sai ya nemi shawarar matasa waɗanda suka yi girma tare, waɗanda kuma suke masa hidima.
9 Han spurte dem: Hvad råder I til at vi skal svare dette folk som har sagt til mig: Lett det åk din far la på oss?
Ya tambaye su, “Mece ce shawararku? Yaya za mu amsa wa waɗannan mutane masu cewa, ‘Ka sassauta nauyin da mahaifinka ya sa a kanmu’?”
10 Og de unge, som var vokset op sammen med ham, svarte ham: Så skal du si til dette folk som sa til dig: Din far gjorde vart åk tungt, men gjør du det lettere for oss - så skal du tale til dem: Min lillefinger er tykkere enn min fars lender;
Matasan, waɗanda suka yi girma tare da shi, suka amsa, “Faɗa wa waɗannan mutanen da suka ce maka, ‘Mahaifinka ya sa kaya masu nauyi a kanmu, amma ka sassauta kayanka.’ Ka ce musu, ‘Ƙaramin yatsana ya fi ƙugun tsohona kauri.
11 har nu min far lagt et tungt åk på eder, så vil jeg gjøre eders åk ennu tyngre; har min far tuktet eder med sveper, så vil jeg tukte eder med skorpioner.
Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.’”
12 Så kom Jeroboam og alt folket til Rehabeam den tredje dag, således som kongen hadde sagt: Kom til mig igjen om tre dager!
Bayan kwana uku, Yerobowam da dukan mutane suka dawo wurin Rehobowam yadda sarki ya faɗa, “Ku dawo gare ni cikin kwana uku.”
13 Da gav kongen folket et hårdt svar - han aktet ikke på det råd som de gamle hadde gitt ham,
Sai Sarki ya amsa wa mutane da zafi. Yana ƙin shawarar da dattawa suka ba shi.
14 men svarte dem som de unge hadde rådet til: Har min far gjort eders åk tungt, så vil jeg gjøre eders åk ennu tyngre; har min far tuktet eder med sveper, så vil jeg tukte eder med skorpioner.
Ya bi shawarar matasa, ya ce, “Mahaifina ya sa muku kaya masu nauyi; ni zan ma sa su fi haka nauyi. Mahaifina ya hore ku da bulala; ni kuwa zan hore ku da kunamai.”
15 Kongen hørte ikke på folket; for Herren styrte det så forat hans ord skulde bli opfylt, det som Herren hadde talt til Jeroboam, Nebats sønn, ved Akia fra Silo.
Saboda haka sarki bai saurare mutane ba, gama wannan abin da ya faru daga wurin Ubangiji ne, don a cika maganar Ubangiji da ya yi wa Yerobowam ɗan Nebat ta wurin Ahiya, mutumin Shilo.
16 Da nu hele Israel så at kongen ikke hørte på dem, svarte folket kongen og sa: Hvad del har vi i David? Vi har ingen lodd i Isais sønn. Til dine telt, Israel! Se nu selv til ditt hus, David! Så drog Israel hjem igjen.
Da dukan Isra’ila suka ga sarki ya ƙi yă saurare su, sai suka amsa wa sarki, “Ina ruwanmu da Dawuda! Ai! Ba mu da gādo wurin ɗan Yesse. Ya Isra’ila, kowa yă koma tentinsa! Dawuda, sai ka lura da gidanka!” Saboda haka Isra’ilawa suka watse zuwa gida.
17 Bare over de Israels barn som bodde i Judas byer, blev Rehabeam konge.
Amma ga Isra’ilawan da suke zama a garuruwan Yahuda kuwa, Rehobowam ya ci gaba da mulki a kansu.
18 Da sendte kong Rehabeam Adoram avsted, han som hadde opsyn med pliktarbeidet; men hele Israel stenet ham, så han døde, og kong Rehabeam selv måtte i all hast springe op i sin vogn og flykte til Jerusalem.
Sarki Rehobowam ya aiki Adoniram wanda yake shugaban aikin gandu, amma Isra’ila suka jajjefe shi da dutse har ya mutu. Sarki Rehobowam, ya sullale ya hau keken yaƙinsa ya tsere zuwa Urushalima.
19 Således falt Israel fra Davids hus, og så har det vært til denne dag.
Tun daga wannan ranar ne mutanen Isra’ila suka shiga gāba da gidan Dawuda har wa yau.
20 Da hele Israel hørte at Jeroboam var kommet tilbake, sendte de bud og kalte ham til folkeforsamlingen og gjorde ham til konge over hele Israel; det var ikke nogen som holdt sig til Davids hus, uten Juda stamme alene.
Sa’ad da dukan Isra’ilawa suka ji Yerobowam ya dawo, sai suka aika, suka kira shi zuwa taro, suka kuma naɗa shi sarki bisa dukan Isra’ila. Kabila Yahuda kaɗai ta kasance mai biyayya ga gidan Dawuda.
21 Da Rehabeam kom til Jerusalem, samlet han hele Judas hus og Benjamins stamme, hundre og åtti tusen utvalgte krigsmenn, forat de skulde stride mot Israels hus og vinne riket tilbake for Rehabeam, Salomos sønn.
Da Rehobowam ya isa Urushalima, ya tattara dukan gidan Yahuda da kabilar Benyamin, ya sami sun kai mayaƙa dubu da tamanin. Sai aka shirya don su yaƙi gidan Isra’ila, su kuma mayar da masarautar wa Rehobowam ɗan Solomon.
22 Da kom Guds ord til Semaja, den Guds mann, og det lød således:
Amma waɗannan kalmomin Allah suka zo wa Shemahiya, mutumin Allah, cewa,
23 Si til Rehabeam, Salomos sønn, Judas konge, og til hele Judas og Benjamins hus og resten av folket:
“Faɗa wa Rehobowam ɗan Solomon, sarkin Yahuda, ka faɗa wa dukan gidan Yahuda da Benyamin, da kuma dukan sauran mutane,
24 Så sier Herren: I skal ikke dra op og stride mot eders brødre, Israels barn. Vend hjem igjen hver til sitt hus! For det som har hendt, er kommet fra mig. Da lød de Herrens ord; de vendte om og drog bort, som Herren hadde sagt.
‘Ga abin da Ubangiji ya ce, “Kada ku haura don ku yi yaƙi da’yan’uwanku, Isra’ilawa. Ku koma gida, kowannenku, gama wannan aikina ne.”’” Saboda haka suka yi biyayya da maganar Ubangiji, suka sāke watse zuwa gida, yadda Ubangiji ya umarta.
25 Jeroboam bygget Sikem i Efra'im-fjellene om til en fast by og bosatte sig der; siden drog han derfra og bygget også Pnuel om til en fast by.
Sai Yerobowam ya ƙara gina Shekem a ƙasar tudu ta Efraim, ya zauna a can. Daga can ya tafi ya gina Fenuwel.
26 Og Jeroboam tenkte ved sig selv: Riket kunde snart komme tilbake til Davids hus;
Yerobowam ya yi tunani a ransa ya ce, “Mai yiwuwa mulkin yă koma gidan Dawuda.
27 dersom dette folk drar op for å bære frem offer i Herrens hus i Jerusalem, så vil deres hjerte igjen vende sig til deres herre Rehabeam, Judas konge, og så vil de drepe mig og vende tilbake til Judas konge Rehabeam.
In waɗannan mutane sun riƙa haurawa don su miƙa hadayu a haikalin Ubangiji a Urushalima. Za su sāke nuna biyayya ga mai girma, Rehobowam, sarkin Yahuda. Za su kashe ni su kuma koma ga Sarki Rehobowam.”
28 Og kongen holdt råd, og så gjorde han to gullkalver; og han sa til folket: I har nu lenge nok draget op til Jerusalem; se, her er dine guder, Israel, som førte dig op fra Egyptens land.
Bayan ya nemi shawara, sai sarki ya yi siffofin’yan maruƙa biyu na zinariya. Ya ce wa mutane, “Kun daɗe kuna haurawa zuwa can Urushalima. Ga allolinku, ya Isra’ila, waɗanda suka fitar da ku daga ƙasar Masar.”
29 Og han stilte den ene op i Betel, og den andre satte han i Dan.
Sai ya kafa ɗaya a Betel, ɗaya kuma a Dan.
30 Dette blev en årsak til synd; folket gikk like til Dan for å trede frem for den ene av dem.
Wannan ya zama zunubi, gama mutane suna tafiya yin wa wannan da yake a Betel sujada, su kuma je har Dan don su yi wa ɗayan sujada.
31 Han bygget også hus på offerhaugene og gjorde hvem han vilde av folket til prester, enda de ikke var av Levis barn.
Yerobowam ya gina masujadai da suke kan tuddai, ya kuma naɗa firistoci barkatai daga cikin mutanen da ba na zuriyar Lawi ba.
32 Og Jeroboam holdt en fest i den åttende måned, på den femtende dag i måneden, i likhet med festen i Juda, og han ofret på alteret. Således gjorde han i Betel; han ofret til kalvene som han hadde gjort, og han lot dem som han hadde gjort til prester ved offerhaugene, gjøre tjeneste i Betel,
Ya kafa biki a rana ta goma sha biyar ta watan takwas, kamar bikin da ake yi a Yahuda, ya kuma miƙa hadayu a bisa bagade. Ya yi haka a Betel, yana miƙa wa siffofin maruƙan da ya yi hadayu. A Betel kuma ya naɗa firistoci a wuraren tudun da ya yi.
33 og han ofret på det alter han hadde gjort i Betel, den femtende dag i den åttende måned, den måned som han hadde valgt efter sitt eget hode. Da holdt han en fest for Israels barn og ofret på alteret og brente røkelse.
A rana ta goma sha biyar ta watan takwas, watan da ya zaɓa, ya miƙa hadayu a bisa bagaden da ya gina a Betel. Saboda haka ya kafa biki don Isra’ilawa, ya kuma haura zuwa bagade don yă miƙa hadayu.

< 1 Kongebok 12 >