< 1 Korintierne 15 >
1 Jeg kunngjør eder, brødre, det evangelium som jeg forkynte eder, som I og tok imot, som I og står fast i,
To,’yan’uwa, ina so in tuna muku da bisharar da na yi muku wa’azinta, wadda kuka karɓa, wadda kuma kuka yanke shawara ku tsaya a kai.
2 som I og blir frelst ved dersom I holder fast ved det ord hvormed jeg forkynte eder det, såfremt I ikke forgjeves er kommet til troen.
Ta wurin wannan bisharar ce kuka sami ceto, muddin kuna riƙe da wa’azin da na yi muku kam-kam. In ba haka ba, kun gaskata a banza ke nan.
3 For jeg overgav eder blandt de første ting det som jeg selv mottok, at Kristus døde for våre synder efter skriftene,
Gama abu farko mafi muhimmancin da na karɓo shi ne na ba ku cewa Kiristi ya mutu domin zunubanmu bisa ga Nassi,
4 og at han blev begravet,
cewa an binne shi an kuma tashe shi a rana ta uku bisa ga Nassi,
5 og at han opstod på den tredje dag efter skriftene,
cewa ya bayyana ga Bitrus, sa’an nan ga Sha Biyun.
6 og at han blev sett av Kefas, derefter av de tolv.
Bayan haka, ya bayyana ga fiye da ɗari biyar daga cikin’yan’uwa a lokaci guda. Yawancinsu kuwa suna nan da rai, ko da yake waɗansu sun riga sun yi barci.
7 Derefter blev han sett av mere enn fem hundre brødre på én gang - av dem er de fleste ennu i live, men nogen er hensovet.
Sa’an nan ya bayyana ga Yaƙub, sa’an nan ga dukan manzannin,
8 Derefter blev han sett av Jakob, derefter av alle apostlene.
a ƙarshe duka, ya bayyana a gare ni, kamar wanda an haifa a lokacin da bai kamata ba.
9 Men sist av alle blev han og sett av mig som det ufullbårne foster; for jeg er den ringeste av apostlene og er ikke verd å kalles apostel, fordi jeg har forfulgt Guds menighet;
Gama ni ne mafi ƙanƙanta a cikin manzanni, ban kuma isa a kira ni manzo ba, domin na tsananta wa ikkilisiyar Allah.
10 men av Guds nåde er jeg det jeg er, og hans nåde mot mig har ikke vært forgjeves, men jeg har arbeidet mere enn de alle, dog ikke jeg, men Guds nåde som er med mig.
Amma bisa ga alherin Allah, na zama abin da nake, alherinsa zuwa gare ni kuwa bai zama a banza ba. A’a, na yi aiki fiye da dukansu, duk da haka, ba ni ba ne, sai dai alherin Allah da yake tare da ni ne.
11 Hvad enten det da er jeg eller de andre, så forkynner vi således, og således kom I til troen.
To, ko ni ne, ko su ne, wannan shi ne abin da muke wa’azi, shi ne kuma abin da kuka gaskata.
12 Men forkynnes det om Kristus at han er opstanden fra de døde, hvorledes kan da nogen iblandt eder si at det ikke er nogen opstandelse av døde?
Amma in ana wa’azi cewa Kiristi ya tashi daga matattu, yaya waɗansu a cikinku suke cewa babu tashin matattu?
13 Men er det ikke nogen opstandelse av døde, da er heller ikke Kristus opstanden;
In babu tashin matattu, to, ba a tā da Kiristi ma ba ke nan.
14 men er Kristus ikke opstanden, da er vår forkynnelse intet, da er også eders tro intet;
In ba a tashe Kiristi ba kuwa, ai, wa’azinmu, da bangaskiyarku banza ne.
15 da finnes vi og å være falske vidner om Gud, fordi vi har vidnet mot Gud at han har opvakt Kristus, som han dog ikke har opvakt såfremt altså de døde ikke opstår.
Sai ma ya zama mun zama masu ba da shaidar ƙarya game da Allah ke nan, domin mun shaida game da Allah cewa ya tashe Kiristi daga matattu. Bai tashe Kiristi ba ke nan, in lalle ba a tā da matattu.
16 For dersom de døde ikke opstår, da er heller ikke Kristus opstanden;
Gama in ba a tā da matattu ba, to, Kiristi ma ba a tashe shi ba ke nan.
17 men er Kristus ikke opstanden, da er eders tro unyttig, da er I ennu i eders synder,
In kuwa ba a tashe Kiristi ba, bangaskiyarku a banza take, ya zama har yanzu kuna cikin zunubanku ke nan.
18 da er altså også de fortapt som er hensovet i Kristus.
Ashe, waɗanda suka yi barci a cikin Kiristi ma sun hallaka ke nan.
19 Har vi bare i dette liv satt vårt håp til Kristus, da er vi de ynkverdigste av alle mennesker.
In a wannan rayuwar ce kaɗai muke da bege cikin Kiristi, mun zama abin tausayi fiye da dukan mutane.
20 Men nu er Kristus opstanden fra de døde og er blitt førstegrøden av de hensovede.
Amma tabbatacce, an tā da Kiristi daga matattu, nunan fari kuwa cikin waɗanda suka yi barci.
21 For eftersom døden er kommet ved et menneske, så er og de dødes opstandelse kommet ved et menneske;
Da yake mutuwa ta zo ta wurin mutum, haka tashin matattu ma ya zo ta wurin mutum.
22 for likesom alle dør i Adam, så skal og alle levendegjøres i Kristus.
Kamar yadda duka suka mutu cikin Adamu, haka duka za su rayu cikin Kiristi.
23 Men hver i sin egen avdeling: Kristus er førstegrøden; derefter skal de som hører Kristus til, levendegjøres ved hans komme;
Sai dai kowa da lokacinsa. Kiristi ne nunan fari; sa’an nan sa’ad da ya dawo; za a tā da waɗanda suke nasa.
24 derefter kommer enden, når han overgir riket til Gud og Faderen, efterat han har tilintetgjort all makt og all myndighet og velde.
Sa’an nan sai ƙarshen ta zo, sa’ad da zai miƙa wa Allah Uba mulki, bayan ya hallaka dukan sarauta, mulki da iko.
25 For han skal være konge inntil han får lagt alle sine fiender under sine føtter.
Gama dole yă yi mulki har sai ya sa dukan abokan gābansa a ƙarƙashin ƙafafunsa.
26 Den siste fiende som tilintetgjøres, er døden;
Abokin gāba na ƙarshen da za a hallaka kuwa, shi ne mutuwa.
27 for han har lagt alt under hans føtter. Men når han sier at alt er ham underlagt, så er det klart at han er undtatt som har underlagt ham alt;
Gama ya “sa kome a ƙarƙashin ƙafafunsa.” To, da aka ce an sa “kome” a ƙarƙashinsa, a fili yake cewa ba a haɗa da Allah a ciki ba, shi wannan da ya sa kome a ƙarƙashin Kiristi.
28 men når alt er ham underlagt, da skal og Sønnen selv underlegge sig ham som la alt under ham, forat Gud skal være alt i alle.
Sa’ad da ya yi haka, sa’an nan Ɗan kansa yă koma a ƙarƙashin shi wanda ya sa kome a ƙarƙashinsa, domin Allah yă zama kome da kome.
29 Hvad gjør da de som lar sig døpe for de døde? Dersom de døde i det hele tatt ikke opstår, hvorfor lar de sig da døpe for dem?
To, in babu tashin matattu, mene ne waɗanda ake musu baftisma saboda matattu za su yi? In ba a tā da matattu sam, me ya sa ake yin wa mutane baftisma saboda su?
30 Hvorfor setter også vi oss hver time i fare?
Mu ma don me muke sa kanmu cikin hatsari a kowace sa’a?
31 Jeg dør hver dag, så sant som jeg kan rose mig av eder, brødre, i Kristus Jesus, vår Herre.
Ina fuskantar mutuwa kowace rana. I, kamar yadda yake tabbatacce cewa ina taƙama da ku cikin Kiristi Yesu Ubangijinmu.
32 Var det på menneskelig vis jeg stred med ville dyr i Efesus, hvad vinning har jeg da av det? Dersom de døde ikke opstår, da la oss ete og drikke, for imorgen dør vi!
In na yi kokawa da mugayen namomin jeji a Afisa bisa ga ra’ayin mutane ne kawai, mece ce ribata, in har ba a tā da matattu? Ai, “Sai mu ci mu sha, da yake gobe za mu mutu.”
33 Far ikke vill! Dårlig omgang forderver gode seder.
Kada fa a ruɗe ku, “Ajiyar mugayen abokai yana ɓata hali mai kyau.”
34 Våkn op for alvor og synd ikke! for somme har ikke kjennskap til Gud; til skam for eder sier jeg det.
Ku koma cikin hankalinku yadda ya kamata, ku kuma daina yin zunubi, gama akwai waɗansu da ba su san Allah ba, na faɗi wannan ne don ku kunyata.
35 Men en kunde si: Hvorledes opstår de døde? og med hvad slags legeme kommer de frem?
Amma wani yana iya tambaya yă ce, “Ta yaya ake tā da matattun? Da wane irin jiki za su tashi?”
36 Du dåre! det du sår, blir ikke levendegjort uten det dør.
Kai, marar azanci! Abin da kuka shuka ba zai tsira ba sai ya mutu.
37 Og når du sår, sår du ikke det legeme som skal bli, men et nakent korn, kan hende av hvete eller av noget annet slag;
Sa’ad da kuke shuki, ba tsiron da zai yi girma ba ne kuka shuka, ƙwayar ce kawai, ko ta alkama ko kuma na wani irin dabam.
38 men Gud gir det et legeme efter sin vilje, og hvert slags sæd sitt eget legeme.
Amma Allah yakan ba ƙwayar jiki yadda ya yi niyya, kuma ga kowane irin ƙwaya yakan ba ta irin jikinta.
39 Ikke alt kjøtt er det samme kjøtt, men ett er kjøtt i mennesker, et annet i fe, et annet i fugler, et annet i fisker.
Ba dukan nama ne iri ɗaya ba. Mutane da irin nasu, dabbobi da irin nasu, tsuntsaye da irin nasu, kifaye kuma da irin nasu.
40 Og der er himmelske legemer, og der er jordiske legemer; men én herlighet har de himmelske legemer, en annen de jordiske.
Akwai jikuna iri na samaniya, akwai kuma jikuna iri na duniya; sai dai darajar jikunan samaniya dabam take, darajar jikunan duniya kuma dabam take.
41 Én glans har solen, og en annen månen, og en annen stjernene; for den ene stjerne skiller sig fra den andre i glans.
Rana tana da wata irin daraja, wata yana da wata darajar dabam, taurari kuma suna da tasu dabam. Wani tauraro kuwa yakan bambanta da wani a wajen daraja.
42 Så er det og med de dødes opstandelse. Det såes i forgjengelighet; det opstår i uforgjengelighet;
Haka ne tashin matattu zai kasance. Abin da aka shuka yakan ruɓe, abin da aka tā da shi kuma ba ya ruɓewa;
43 det såes i vanære, det opstår i herlighet; det såes i skrøpelighet, det opstår i kraft;
akan shuka shi cikin ƙasƙanci, a kuma tā da shi cikin ɗaukaka, akan shuka shi da rashin ƙarfi, a kuma tā da shi da ƙarfi;
44 der såes et naturlig legeme, der opstår et åndelig legeme. Så visst som det gis et naturlig legeme, gis det og et åndelig legeme.
akan shuka shi da jiki na mutuntaka, a kuma tā da shi da jikin ruhaniya. In akwai jiki na mutuntaka, to, lalle akwai jikin ruhaniya ma.
45 Således er det og skrevet: Det første menneske, Adam, blev til en levende sjel; den siste Adam er blitt til en levendegjørende ånd.
Haka yake a rubuce cewa, “Adamu, mutumin farko ya zama mai rai”; Adamu na ƙarshe kuwa ruhu ne mai ba da rai.
46 Men det åndelige er ikke det første, men det naturlige, derefter det åndelige.
Ba jikin ruhaniya ne ya zo da farko ba, na mutuntakan ne, daga baya kuma sai na ruhaniya.
47 Det første menneske var av jorden, jordisk; det annet menneske er av himmelen.
Mutumin farko daga turɓaya ce ya fito, mutum na biyu kuwa daga sama ne ya fito.
48 Sådan som den jordiske var, så er og de jordiske, og sådan som den himmelske er, så skal og de himmelske være,
Kamar yadda mutumin turɓaya yake, haka ma waɗanda suke na turɓaya. Kuma kamar yadda mutumin sama yake, haka ma waɗanda suke na sama.
49 og likesom vi har båret den jordiskes billede, så skal vi og bære den himmelskes billede.
Kamar dai yadda muka ɗauki siffar mutumin turɓaya, haka kuma za mu ɗauki siffar mutumin sama.
50 Men dette sier jeg, brødre, at kjød og blod kan ikke arve Guds rike, heller ikke arver forgjengelighet uforgjengelighet.
Ina sanar da ku,’yan’uwa, cewa nama da jini ba za su gāji mulkin Allah ba, haka ma ruɓa ba zai gāji rashin ruɓa ba.
51 Se, jeg sier eder en hemmelighet: Vi skal ikke alle hensove, men vi skal alle forvandles,
Ku saurara, in gaya muku wani asiri. Ba dukanmu ne za mu yi barci ba, sai dai duk za a sauya kamanninmu
52 i et nu, i et øieblikk, ved den siste basun. For basunen skal lyde, og de døde skal opstå uforgjengelige, og vi skal forvandles.
farat ɗaya, cikin ƙyaftawar ido, da busan ƙaho na ƙarshe. Gama za a busa ƙaho, za a tā da matattu da jiki irin da ba ya ruɓewa, za a kuma sauya kamanninmu.
53 For dette forgjengelige skal bli iklædd uforgjengelighet, og dette dødelige bli iklædd udødelighet.
Gama dole mai ruɓa yă maye wa mai ruɓan nan, marar mutuwa kuma yă maye wa mai mutuwan nan.
54 Og når dette forgjengelige er iklædd uforgjengelighet, og dette dødelige er iklædd udødelighet, da opfylles det ord som er skrevet: Døden er opslukt til seier.
Sa’ad da mai ruɓan nan ya maye marar ruɓan nan, mai mutuwa kuma ya maye marar mutuwan nan, sa’an nan ne karin maganar da yake a rubuce zai zama gaskiya cewa, “An haɗiye mutuwa cikin nasara.”
55 Død, hvor er din brodd? Død, hvor er din seier? (Hadēs )
“Ya ke mutuwa, ina nasararki? Ya ke mutuwa, ina dafinki?” (Hadēs )
56 Men dødens brodd er synden, og syndens kraft er loven;
Zunubi ne yake ba wa mutuwa dafi, Doka kuma take ba wa zunubi iko.
57 men Gud være takk, som gir oss seier ved vår Herre Jesus Kristus!
Amma godiya ga Allah! Shi ne ya ba mu nasara ta wurin Ubangijinmu Yesu Kiristi.
58 Derfor, mine elskede brødre, vær faste, urokkelige, alltid rike i Herrens gjerning, da I vet at eders arbeide ikke er unyttig i Herren!
Saboda haka, ƙaunatattu’yan’uwana, ku tsaya da daram. Kada wani abu yă jijjiga ku. Ku ba da kanku kullum ga aikin Ubangiji, domin kun san cewa famar da kuke yi saboda Ubangiji ba a banza take ba.