< 1 Korintierne 11 >

1 Bli mine efterfølgere, likesom jeg efterfølger Kristus!
Ku bi gurbina, kamar yadda ni nake bin gurbin Kiristi.
2 Jeg roser eder for at I kommer mig i hu i alle ting og holder fast ved mine forskrifter, således som jeg gav eder dem.
Ina yabonku saboda kuna tunawa da ni a cikin kowane abu, kuna kuma riƙe da koyarwar, yadda na ba ku.
3 Men jeg vil at I skal vite at Kristus er enhver manns hoved, og mannen er kvinnens hoved, og Gud er Kristi hoved.
To, ina so ku gane cewa shugaban kowane namiji Kiristi ne, shugaban mace namiji ne, shugaban Kiristi kuma Allah ne.
4 Hver mann som beder eller taler profetisk med noget på hodet, vanærer sitt hode;
Kowane namijin da ya yi addu’a ko annabci da kansa a rufe ya jawo kunya wa kansa.
5 men hver kvinne som beder eller taler profetisk med utildekket hode, vanærer sitt hode; for det er aldeles det samme som om hun var raket.
Duk macen da ta yi addu’a ko annabci da kanta a buɗe kuwa ta rena kanta, ya zama kamar an aske kanta ke nan.
6 For hvis en kvinne ikke tildekker sig, da la henne også klippe håret av; men er det usømmelig for en kvinne å klippe eller rake av sig håret, da la henne tildekke sig.
In mace ba ta so tă rufe kanta, to, sai tă aske gashinta; in kuwa abin kunya ne mace tă yanke ko tă aske gashinta, to, sai tă rufe kanta.
7 For en mann skal ikke tildekke sitt hode, eftersom han er Guds billede og ære; men kvinnen er mannens ære.
Namiji kuwa bai kamata ya rufe kansa ba, da yake shi kamannin Allah ne, da kuma darajar Allah, amma mace dai, darajar namiji ne.
8 For mannen er ikke av kvinnen, men kvinnen er av mannen;
Gama namiji bai fito daga mace ba, sai dai mace ce ta fito daga namiji.
9 mannen blev jo heller ikke skapt for kvinnens skyld, men kvinnen for mannens skyld.
Ba a kuma halicci namiji don mace ba, sai dai mace don namiji.
10 Derfor bør kvinnen ha et undergivenhets-tegn på sitt hode for englenes skyld.
Don haka, saboda wannan, da kuma saboda mala’iku, dole mace ta ɗaura wani abu a kanta.
11 Dog, i Herren er hverken kvinnen noget fremfor mannen eller mannen noget fremfor kvinnen;
Duk da haka a cikin Ubangiji, mace ba a rabe take da namiji ba, namiji kuma ba a rabe yake da mace ba.
12 for likesom kvinnen er av mannen, så er også mannen ved kvinnen, og alt er av Gud.
Kamar yadda mace ta fito daga namiji, haka kuma aka haifi namiji ta wurin mace. Sai dai kowane abu daga Allah yake.
13 Døm hos eder selv: passer det sig at en kvinne beder til Gud med utildekket hode?
Ku kanku duba mana. Ya yi kyau mace tă yi addu’a ga Allah da kanta a buɗe?
14 Lærer ikke endog selve naturen eder at dersom en mann lar håret vokse langt, er det ham til vanære,
Kai, yadda halitta take ma, ai, ta koya muku cewa in namiji yana da dogon gashi, abin kunya ne a gare shi,
15 men dersom en kvinne lar håret vokse langt, er det henne til ære? for det lange hår er gitt henne til slør.
amma in mace tana da dogon gashi, ai, daraja ce a gare ta. Gama an ba ta dogon gashi saboda rufe kanta ne.
16 Men dersom nogen vil være trettekjær, da har ikke vi en sådan skikk, heller ikke Guds menigheter.
In akwai mai gardama da wannan, to, mu dai ba mu da wata al’ada, haka ma ikkilisiyoyin Allah.
17 Men idet jeg påbyder dette, roser jeg ikke at I kommer sammen, ikke til det bedre, men til det verre.
Game da umarnan nan dai, ban yaba muku ba, domin taruwarku ba ta kirki ba ce, ɓarna ce.
18 For for det første, når I kommer sammen i menighets-samling, hører jeg at det er splid iblandt eder, og for en del tror jeg det;
Da farko dai, na ji cewa sa’ad da kuka taru a matsayin ikkilisiya, akwai tsattsaguwa a tsakaninku, har na fara yarda da zancen.
19 for det må være partier iblandt eder, forat de ekte kan bli åpenbare iblandt eder.
Ba shakka dole a sami bambanci a tsakaninku don a nuna wa Allah ya amince da shi a cikinku.
20 Når I altså kommer sammen, da blir det ikke Herrens nattverd I eter;
Sa’ad da kuka taru, ba Cimar Ubangiji kuke ci ba,
21 for idet I eter, tar hver på forhånd sin egen mat, og den ene er hungrig, og den annen er drukken.
gama yayinda kuke ci, kowa yakan ci gaba ba tare da jiran wani ba. Wani yă zauna da yunwa, wani kuma yă bugu.
22 Har I da ikke hus til å ete og drikke i? eller forakter I Guds menighet og vanærer dem som intet har? Hvad skal jeg si til eder? skal jeg rose eder? I dette roser jeg eder ikke.
Kai, ba ku da gidajen da za ku ci ku sha ne? Ko dai kun rena ikkilisiyar Allah ne, kuna kuma wulaƙanta waɗanda ba su da kome? Me zan ce muku? In yabe ku ne game da wannan? A’a, ko kaɗan!
23 For jeg har mottatt fra Herren dette som jeg også har overgitt eder, at den Herre Jesus i den natt da han blev forrådt, tok et brød,
Gama abin da na karɓa daga wurin Ubangiji shi ne nake ba ku. Ubangiji Yesu, a daren da aka bashe shi, ya ɗauki burodi,
24 takket og brøt det og sa: Dette er mitt legeme, som er for eder; gjør dette til minne om mig!
bayan ya yi godiya, sai ya kakkarya ya ce, “Wannan jikina ne, wanda yake dominku, ku yi wannan don tunawa da ni.”
25 Likeså også kalken efter aftensmåltidet, idet han sa: Denne kalk er den nye pakt i mitt blod; gjør dette, så ofte som I drikker den, til minne om mig!
Haka kuma bayan cimar, ya ɗauki kwaf, yana cewa, “Wannan kwaf ne sabon alkawari a jinina; ku yi wannan, a duk sa’ad da kuke sha, don tunawa da ni.”
26 For så ofte som I eter dette brød og drikker denne kalk, forkynner I Herrens død, inntil han kommer.
Gama a duk sa’ad da kuke cin wannan burodi, kuke kuma sha daga wannan kwaf, kuna shelar mutuwar Ubangiji ne har yă dawo.
27 Derfor, hver som eter brødet eller drikker Herrens kalk uverdig, han blir skyldig i Herrens legeme og blod.
Saboda haka, duk wanda ya ci burodin ko ya sha daga kwaf na Ubangiji da rashin cancanta, ya yi laifin wulaƙanta jiki da jinin Ubangiji ke nan.
28 Men hvert menneske prøve sig selv, og så ete han av brødet og drikke av kalken!
Dole kowa yă bincike kansa kafin yă ci burodin yă kuma sha daga kwaf ɗin.
29 for den som eter og drikker, han eter og drikker sig selv til dom dersom han ikke gjør forskjell på Herrens legeme.
Gama duk wanda ya ci ya kuma sha ba tare da fahimtar jikin Ubangiji ba, ya ci ya kuma sha wa kansa hukunci ne.
30 Derfor er det mange skrøpelige og syke iblandt eder, og mange sovner inn.
Shi ya sa da yawa a cikinku ba su da ƙarfi, suna kuma da rashin lafiya, waɗansunku kuma sun riga sun yi barci.
31 Men dersom vi dømte oss selv, blev vi ikke dømt;
Amma in da za mu auna kanmu sosai, da ba za mu shiga irin hukuncin nan ba.
32 men når vi dømmes, da refses vi av Herren, forat vi ikke skal fordømmes sammen med verden.
Duk da haka sa’ad da Ubangiji ya hukunta mu, ana yin mana horo ne don kada a ƙarshe a hallaka mu tare da duniya.
33 Derfor, mine brødre, når I kommer sammen for å ete, da del med hverandre;
Saboda haka’yan’uwana, sa’ad da kuka taru don ci, ku jira juna.
34 og hvis nogen hungrer, da ete han hjemme, forat I ikke skal komme sammen til dom! Det annet skal jeg foreskrive når jeg kommer.
In wani yana jin yunwa, sai yă ci abinci a gida, saboda in kuka taru kada yă jawo hukunci. Sa’ad da na zo kuma zan ba da ƙarin umarnai.

< 1 Korintierne 11 >